Showing 27001 words to 30000 words out of 145898 words
ta kar6i ledar magungunan,muryar ta a hankali mai cike da jin zazza6i tace"nagode"
Murmushi kawai yarinyar ta mata snn ta wuce taje ta sami jamil a waje yana jingine jikin motar sa yana jiran fitowar ta.
Tana qarasowa ya tashi daga jinginen da yake tare da fad'in"hope she is doing ok sanyin be riga ya kamata ba dai ko?
Tace"inafa har zazza6i ya kamata ai,se ma kaji irin yanda jikin ta yayi zafi da zata qarfi ledar magunguna a hannu na naji hannun ta kmr garwashi.
Oh no!to kin mata bayanin yanda zata sha magungunan?
Aa kawai dai nace ta duba kowanne da akwai yanda zata sha.
No zainab ba haka ba plz koma kiji idan taci abinci se ki 6a66alla mata magungunan ki bata tasha,idan kuma bata ci abinci ba ki samu abunda kika d'an dafa mata me sauqi taci kinji zanje na dawo.
"Ok to"
Ta fad'a snn ta koma daga ciki.
Zarah wacce ana bata magungunan ta kaisu kan bedside drawer ta ajiye,ta kwanta knn ta koma jin knocking,ba yanda ta iya haka ta taso ta bud'e qofa.
Zainab tace"yi haquri se damunki nake tayi,yaya ne yace na dawo na miki bayanin yanda zaki sha magungunan.
Hanya Zarah ta bata tare da fad'in to shigo daka ciki.
Zainab ta shiga ta d'auki ledar magun gunan ta ciro su snn ta kalli zarah tace"kinci abinci na 6alle miki magungunan kisha?
A hnkli Zarah ta girgiza kanta alamar bata ci ba
zainab tace"Ok to me zan dafa miki?
A'a ki barshi nagode ko tea zan had'a na sha...No abu me d'an nauyi ya kamata kici idan akwai indomie zan dafa miki kina so?
"Eh"
zarah ta fad'a nn zainab ta ajiye mayafinta ta fita.
Tana cikin dafa indomien ne jamil ya kirata a waya acewar tazo ya dawo yana a farfajiyar gidan.
Taje ta same shi ya miqa mata er qaramar farar ledar pharmacy dake hannun shi yace"allurai ne a ciki plz ki mata a hankli kar ki jiwa matar mutane ciwo"
A hnkli Zainab ta lumshe idanun tare da ware su akan shi snn tace"haba dai yaya se kace ba aikina ba kuma ko dan kai ae dole na bita a hankli gudun kar nayi laifi.
Yace"to iyayen surutu jeki ki mata ina jiranki kizo mu tafi"
Tace"ai bata ci abinci ba shine nake dafa mata yanzu"
Ya girgiza kansa tare da fad'in"Allah sarki zarah,kawai to ki tsaya ki mata duk abunda take so snn idan kin kammala se ki kirani nazo na maida ki gida.
Ok to.
Zainab ta fad'a snn ta koma daga ciki.
Bayan ta gama dafawa zarah indomie har ma zarah d'in taci snn ta shiga had'a allurai,zarah se kallonta take ita wa zatayi wa allura to dan dai taga kmr tayi qarama da iya allura har ta ma mutum.
Murmushi zainab tayi tana mai kallon zarah sbd yanayin fuskar zarah kad'ai ya isa ya bayyana abinda ke zuciyar ta,tace"kar ki damu ni ma'akaciyar asibiti ce karatun da nayi knn fannin nurse.
D'an murmushi zarah tayi dan haka kawai taji ta birge ta.
Bayan zainab ta mata allura ne ta tambaye ta ko da akwai wani abunda take so ta mata kafin ta tafi,tace"ba komai nagode.
Murmushi Zainab ta mata cikin kad'a kanta alamar ba komai snn ta kira jamil yazo ya tafi da ita.
Tun fitar Saifuddeen se bayan zuhur ya dawo gidan rungume da kitty a jikin shi wacce ta d'an walwale ba kmr d'azun da ya fita da ita ba.
Kae tsaye d'akin sa ya nufa d'ayan hannun sa riqe da ledar takeaway d'in da ya siyo.
Har dare be sake fita gidan ba se aikin faman jinyar kitty yake.
Zarah kuwa tunda zainab ta bar gidan ta kwanta bacci koda ta tashi zazza6in ya d'an mata sauqi,sai dai sosai mura ta kamata da dare ko baccin kirki bata iya yi ba da qyar taga safiya.
Koda akayi kwana biyu muryar ta duk ta shaqe bata wani fita sosai,ga masifaffen ciwon kai da mura ta sako mata,ko yaushe tana kwance ko girki bata iya yi se idan Zainab tazo duba ta ne take mata girki dama duk wani abunda take so snn ta tafi.
Washe gari ta kasance Wednesday Alhmdlh ta d'anji sauki ba kmr sauran kwanaki ba dan yau da kanta ta fito kitchen tana girka abincin da zata ci.
Tana kitchen d'in ne ta soma jin qarar doorbell,a tunanin ta ko Zainab ce tazo amma koda taje ta bud'e qofa se taga Jamil.
A natse ta gaida shi ya amsa tare da tambayar ta ya jikin nata tace mishi taji sauqi.
Snn yace Saifuddeen fa ko yana nn?
Gyad'a masa kai tayi alamar eh sbd d'azu kafin ta fito taji shigowar shi.
Yace"plz kira min shi kice masa gani nazo ina magana"
"To"
Tace tare da bashi hanya ya shigo yaje ya zauna,har takai gun staircase zata haura sama se kuma ta dawo ta durqusa kanta qasa tana riqe da en yatsun ta snn muryar ta a hankli tace"yaya dan Allah idan ba damuwa in yazo ina son gobe ya barni in tafi gida naga su umma,ina gudun na tambaye shi yace bazan je ba.
Jamil dake kallonta yace"ok ba damuwa in yazo zanyi magana dashi.
Godiya ta mishi snn ta tashi ta haura sama zuwa d'akin Saifuddeen.
Knocking d'in farko ana biyu ya bud'e qofa.
Farar singlet ce a jikin shi se dogon wando jeans fuskar sa ba yabo ba fallasa yake kallonta,tun rnr da ya jefa ta sweeming pool be sake sata a idon sa ba se yau wanda yasan ta kamu da rashin lfy ne sbd yana ganin shiga da fitar da zainab keyi a gidan suna had'uwa har su gaisa and yasan ba kowa ke turo ta ba face jamil.
Sau d'aya zara ta kalle sa ta kauda idonta tare da gaya mishi yaya Jamil keson ganin shi.
Daga haka ta wuce ba tare da ta jira me zai ce ba.
Ya sauko ya sami Jamil ya zauna yana me kallon sa fuskar sa a d'aure yace"lafiya?
Murmushi Jamil yayi snn yace"Buddy knn yanzu akan kitty kake fushi dani haka,baka d'aga waya ta snn idan naje office d'inka baka saurara ta and yanzu nazo ka wani d'aure min fuska har da fad'in lafiya knn me ya kawo ni gidan ka ko?
Saifuddeen dake kallon sa yace"wa ya gaya maka akan kitty ne,nifa ka 6ata min rai ne sosai,wai kan wnn banzar yarinyar zaka zazzage ni har kana gaya min magana marar dad'i a kanta,abinda be ta6a faruwa a tsakanin mu ba tun muna yara har girman mu,a gskiya kasani tun wuri ka ajiye dmn bazan d'aukar maka ba wlh.
Jamil ya numfasa tare da fad'in"calm down yi haquri raina ne ya 6aci ba kad'an ba and kai d'in ne baka kyauta ba wlh dmn na tabbatar Zarah bazata wurgo kitty kamar yanda kace ba may be ta bar qofar a bud'e ne har kitty ta fita bata sani ba.
Hm jamil knn shi kuma plate d'in abincin fa ko shima qafafu yayi ya biyo kitty suka fito tare.
Jamil yace"kaga Saifuddeen koma dai mene hukuncin da kayi wa zarah is hard,marin ta fa kayi ina kallo snn kaje ka jefa ta a cikin ruwa masu masifar sanyi wanda hakan ya janyo mata zazza6i da mura still har yanzu kana jin muryar ta bata fita sosai duk sbd wata banza can kitty.
Hararar sa Saifuddeen yayi tare da fad'in kar ka sake.
Jamil yace"Kaji zafi ne sbd na kira kyanwar masoyiyar ka banza,ni kuma fa da kake kiran zarah banza a gabana ka san irin zafin da nake ji kuwa.
Cikin d'aga kafad'a Saifuddeen yace"Oho maka ka bari idan na sake ta ka aure ta qauna yasa ka had'iye ta in ka iya amma ba yanzu da take qarqashin ikona ba dole kayi haquri da duk wani abunda kaga na mata.
Jamil yace"Shikenan Allah ya nuna min ta dawo qarqashin ikona ta huta da qiyayyar da kake nuna mata.
Saifuddeen yace"ko dai ni na huta da jarababben auren ta ba.
Jamil dake kallon sa girgiza kansa kawai yayi.
Snn ya numfasa tare da fad'in"ka dai rage wani abun dan gashi yanzu kan shakkun ka tana son zuwa gida but she can't ask u.
Ta6e da baki Saifuddeen ya kalle sa yace"Au shine se ta gaya maka,to tafi ruwa gudu duk inda zata je ita ta sani Allah yasa ma in taje kar ta dawo".
Murmushi kawai Jamil yayi yana kallon sa be ce masa komai ba.
[11:14AM, 3/6/2018] 鈥�+234 806 858 0203鈥�: _Monday 19/02/2018_
*锘柯宦宦籗AIFUDDEEN!芦禄禄芦芦禄*
By
*Billy giro馃槉*
*Dedicated to禄禄禄Zarah gwandu*
*芦禄Page芦禄 17*
"Ke!
kawo masa lemu!"
Saifuddeen ya fad'a cikin d'aga murya ta yanda zarah zata iya jiyo shi har kitchen.
Snn ya tashi tare da cewa Jamil bari naje na sako riga muje gidan Hjy na kwana biyu banje na ganta ba.
Jamil yace"Ok to"
Kafin Saifuddeen ke wuce wa ya haura zuwa sama,nn se ga zarah tazo d'auke da qaramin tray da juice da kuma cup akai ta ajiye kan stool snn ta tsiyaya mishi lemun a cup ta bashi,ya kar6a tare da fad'in"nayi magana dashi yace kije,gobe da safe se ki shirya zan turo Zainab ta kai ki inshaa Allah"
Cikin nuna jin dad'i ta masa godiya snn ta wuce.
Washe gari koda 11 tayi ta kammala shirin ta tsaf cikin wani dakakken lace dake cikin kayan lefen ta,lace d'in baqi ne da akayi zanen manyan flowers baby pink in colour se lace d'in ya mata kyau sosai sbd d'inkin riga da skirt ne da yayi d'as a jikinta.
D'an kwali riqe a hannun ta ta rasa ta yanda zata d'aura sbd ba iya d'aurin d'an kwali tayi ba gashi da girma.
Ba yanda ta iya se kan bed taje ta shinfid'a shi ta kama gefe da gefe ta linka snn ta d'auka ta d'aura ba tare da tayi wani style ba amma baya se yayi kmr tush sbd yanda tayi rolling d'in d'an kwalin a kan parking d'in sumar kanta da tayi a tsakiya,yayinda jelar gashin nata se reto yake har yana ta6a gadon bayan ta bata kama shi ta dunqule a ciki ba,se gyale ta d'auka ta yafa a kanta baby pink in colour tsadadde me kyau irin na matan manya.
Tasa takalmi snn ta d'auki jaka ta fita da sauri sbd doorbell da ake ta fmn dannawa bata son 6atawa Zainab lokaci.
Sai dai koda ta bud'e qofa ba zainab bace kmr yanda take tunani Jamil ne wanda tana bud'e qofar ya sauke idanun sa akanta se kallonta yake bako qyaftawa dmn ba qaramin kyau ta mishi ba,duk da bata wani qware da yin ja gira ba kmr yanda Nusaiba ke koya mata amma yanda ta jata d'in tayi kyau ba laifi,snn ta shafa powder dai dai bata yi yawa ba bata yi kad'an ba,ba abinda ma yafi birge shi kmr shafin kwallin ta,dmn kwallin ya hau kan idonta dai dai yanda ake so wanda hakan ya bayyanar da ainihin kyawon idanuwan ta manya dasu farare qal,kana ya tafi da idanuwan sa a hnkli kan d'an madaidai cin bakinta da ta shafawa janbaki pink me haske wato klr flowers d'in less d'in ta snn tayi lining with dark pink lip pencil liner.
Se duk yaji ya qara sonta kan yanda ta yafa gyalen ta tun daga saman kai dmn shi dai ko kad'an baya son irin yafin gyalen da yaga en matan yanzu nayi yafi son yaga mace cikin mutunci da kamala.
Can ya tsinkayo muryar ta tana gaida shi,ya kauda fuskar sa a hnkli a ransa yana fad'in subhanallah! tare da yin istigfari dan be san ma ya shagaltu da kallon ta haka ba.
Snn ya amsa mata gaisuwar tare da fad'in"kiyi haquri Zainab baza ta sami zuwa ba tana asibiti aikin safe take dashi yau,but muje mu sauke ki Saifuddeen yana a waje yana jiran mu.
To tace tare da binshi a baya suka fita.
Jamil da kanshi ya bud'e mata gidan baya ta shiga shi kuma ya zagaya ya shiga gaba gurin me zaman banza.
Tsaki Saifuddeen yaja tare da jan motar ransa a 6ace.
Kallon sa kawai jamil yayi ba tare da yace masa komai ba har suka isa.
Basu shiga ciki ba zarah kawai suka sauke suka wuce.
Koda ta shiga falo ta had'u da Abba ze fita umma ta rako shi.
A natse ta durqusa har qasa ta gaida su.
Cike da fara'a suka amsa mata gaisuwar snn ta tashi se kallon ta suke ganin yanda tayi kyau kmr ba ita ba.
Abba yace"ina Saifuddeen d'in yake da kika shigo ke kad'ai?
Tace yanzu suka wuce shida yaya jamil kmr sauri suke da akwai inda zasu je.
Ok to inace dai lafiya lau kuke zaune ko?
Tace"lafiya lau"
Mashaa Allah Abba ya fad'a snn ya kalli umma yace"to ni zan fita se na dawo"
Tace"a dawo lafiya"
Ya fita su kuma suka haura sama zuwa d'akin umma.
kan sofa suka zauna umma na kallon zarah da kulawa tace"har yanzu dai murar nn bata rabu dake ba kina shan magani kuwa?
Zarah tace"Eh inna ina sha ae kinji murya tawa ta d'an sake ba kmr farko ba.
Haka ne ina ce dai bada ruwan sanyi kike wanka ba har murar nn ta kama ki.
Tace"A'a inna ni da ruwan zafi nake wanka,wnn sanyin ina zan iya wanka da ruwan sanyi,na kamu da ita ne kawai.
Umma tace"to Allah qara sauqi"
Ameen su Nusaiba fa yau da wuri suke dawowa koh?
Eh da wuri suke dawowa qarfe biyu tun jiya take zancen yau idan sun dawo gidan naku zasu tafi in yaso su dawo kafin me lesson d'in nasu yazo se gashi kinxo.
Eyyah jiya da muka yi waya se bata gaya min ba amma kuma ni dama na matsu da inzo gida duk kad'ai ci ya min yawa,satin nn uku naji kmr watanni har so nake ma inje rimin dako in ga inna itama ina kewar ta sosai.
Umma tace"Rimin dako kam ba yanzu ba duka duka yaushe ne akayi auren da har zaki je,ki dai bari zuwa wani lokaci snn.
A d'an shagwa6e tace"amma inna kinsan halin shi bazai ta6a cewa in tafi ba,ko yanzu da nazo seda na tambaya dan na fahimci ba zai ce nazo d'in ba tunda shi kullum yana zowa yana ganin ku baya da wata kewa.
Kar ki damu da zarar naga lokaci yayi da kaina zan mishi magana se muje gabad'ayan mu ko?
Murmushi tayi cike da jin dad'i.
Snn ta cire mayafin ta ta ajiye suka tafi kitchen tana taya umma girki.
Bayan su Nusaiba sun dawo ne har ma sunyi wanka sun ci abinci tana zaune ita da Zarah su biyu a d'aki se fira suke a cikin firar su ne Nusaiba ke cewa"ni kuwa 6ter ya plan d'in mu shiru har sati d'aya banji kin fara bani bayani ba.
Zarah tace"inafa ni ban fara gwada wa ba tukun zazza6in mura be barni ba kullum da ciwon kai nake fama yanzu haka ina d'an jin shi se dare yayi na kasa bacci.
Ikon Allah wnn wace irin mura ce haka yaya ya siyo miki magunguna kuwa?
Hm Nusaiba knn yaya jamil dai ya tura qanwar sa zainab ita keta kula dani tana duba ni dama girki duk ita ke min in tazo dan ko fitowa bana iyayi daga d'aki se d'aki.
Da mamaki Nusaiba ke kallonta tace"kuma shine se baki fad'i yanayin da kike ciki ba kika ce mura ce kawai ke damunki ashe har kwantawa kika yi.
To Nusaiba duk a dalilin muguntar yayanki ne fa,bansan ta yaya zan fad'i abun ba dmn ko kad'an bana son su umma su san yanayin da nake ciki da yayanki duk da dai sun san kafin aure ba qaunata yake ba.
Nusaiba ta girgiza kanta tare da fad'in"Oh Allah wane muguntar kuma ya miki har hakan ta faru?
Zarah tace"A dalilin wnn farar kyanwar ne da yake kira kitty,ze yi tafiya ya kawo min ita wai na kulata da ita har ya dawo nace masa bazan iya ba sbd ina mugun tsoron ta kuma ya sani amma ya tafi abinshi ya bar min ita.
Nan ta gayawa Nusaiba duk yanda akayi.
Nusaiba tace"Hm lallai yaya,ya ubangiji Allah ka sauya mishi wnn halin,kiyi haquri inshaa Allah shida kansa ze dawo yana nadamar abubuwan da ya aikata miki.
Shi ya sani ni ina zama dashi ne kawai sbd biyayya duk abunda ze min Allah ya fishi wahala bata kisa,idan kuma na mutu a dalilin muguntar sa shikenan haka Allah ya qaddara zan zama tarihi.
Nusaiba tace"baza ma ki mutu yanzu ba inshaa Allah har se kun zama cikakkin masoyan gaske kun haifi 'ya'ya har ma da jikoki.
Ta6e baki Zarah tayi snn tace"hm da kin tashi kinyi abinda ke gabanki ma da yafi kafin me lesson d'inku yazo".
Ta qarashe mgnr ne tare da kwanciya sbd headache d'in da ke damunta.
Nusaiba dake kallon ta tayi murmushi kawai snn ta tashi.
Har bayan sllr isha'i tana gidan bata koma ba umma ta shigo d'akin ta sami Nusaiba tasa yusra a gaba tana mata homework,zarah kuwa na kwance kan dardumar sallah,umma tace da ita"tashi ki tafi gida gasu Saifuddeen nn sunzo suna jiranki a falo.
Muryar ta a hnkli can ciki tace"wlh inna kaina ke min ciwo sosai,in na tashi har ji nake kmr ze tsage dan Allah a barni zuwa gobe se in koma"
Umma dake kallon ta a hnkli