Showing 30001 words to 33000 words out of 139076 words

Chapter 11 - ZAWARCI COMPLETE HAUSA NOVEL

14 Oct 2025

131

abin ta,Hajara na ta kallon ta .Can ta kasa ha?uri ta ce  ni kam Hajiya lafiya yau na ga sai sauri kike?

Momah ta yi murmushi ta ce  suruka ta ke zuwa,tsawon lokaci da Daddyn yara ke ta ro?onta kan ta dawo nan garin da zama amma ta ?i.Yau dai Allah ya nufa za su dawo 

Haka kawai Hajara ta ji babu daWi,ta ce  har su nawa ne?
 Su biyu ita da autarta 
Ta Wan Sata rai ta ce  Hajiya na ga sai murna kike halan ba ki san zama wuri Waya da suruka ba akwai matsala

Momah ta murmusa ta ce  ai gidanta daban wanda ya gina mata,a can za su sauka girkin dai ne nake yi musu.Kina ji Hajara don Allah ki manta rayuwarki ta baya ki soma wata sabuwa.Dubi fa yadda maza ke sintiri a kanki amma kin ?i kula su,ko mai gadi sai da ya ce yana son ki amma kin yi biris 


Tsabar takaici Hajara ji ta yi kamar ta sha?e Momah,ita da take da burin auren Daddy shi ne za ta wani yi mata zancen mai gadi.
Safeenatu ta shigo tana cewa  Gwaggo Hajara wai ba dai ba ki wanke min uniform Win makaranta ba? Duk fa sun yi datti


Cikin masifar da take cinta ta ce  ke masaka ce da ba za ki wanke da hannunki ba? ?ar uniform Win ma.... kallon da Momah ke yi mata ne yasa Hajara yin shiru tare da fita daga kitchen Win ,nan ne fa ?iyayyar Safeenatu ta soma yi mata tsiro a zuciya.Uniform Win da sun fi kala biyar ta Wauko ta wanke su tana kukan zuci,tana tsaka da wankin ne Safeenatu ta fito sanye da riga da wando jeans ta saka takalmi masu tsini,can ?asa-?asa ta ce  shegiya Allah sa ?afar taki ta ruSe a guntule sai na ga ta hawa takalmi mai tsini kamar wacce za ta le?o bangon duniya



Cike da ba?in ciki dai Hajara ta wuni,a gaban idonta Momah da yara suka fita bayan sun kwashi abinci.
A mutumce Momah ke gaida Hajiya yayin da Habibah kuwa ta ?ure ?afar Safeenatu da kallo,kasa ha?uri ta yi ta ce  zo nan yarinyata na ga ?afarki Safeenatu ta zo ta faWa jikinta tana dariya,cikin sigar wasa Hajiya ta ce  kar ki karya min auta
Feenat ta ce  ai dai Mamata ce gefe ta koma yayin da Habibah ke shafa ?afar na tsawon lokaci,Hajiya dai na kallonta .Bayan tafiyarsu ne ta dubi Habibah ta ce  auta ban son tsiyar gumi fa,Wazu na ga sai faman shafa ?afar Safeenatu kike to mine ne kuma kika gani? Kin sani sarai saboda wannan canfin yasa na yarda muka baro garinmu muka dawo nan.
 Mama babu fa komai,sanin kan ki ina da baiwa ne ta wankin ido duk wata ...

 Ya isa haka ban son jin komai Hajiya ta bar ta nan falo ta shiga sashen da aka tabbatar mata da shi ne nata.Habibah kuwa shiru ta yi tana nazarin lamarin da ta gani a ?afar Safeenatu,ga kuma Murjanatu da ta gani wai ?ar mai aikinsu ce .Da wannan zullumi ta kwana tare da ?udirin in sha Allah gobe za ta kai wa gidan yayan nata girgiza.



A can gidan Daddy kuwa bayan dawowarsu sarai Hajara ta ji hayaniyar su amma ta ?i fitowa har sai da Momah ta aika aka kira ta.
Fuskar nan a Wan haWe ta fito tare da cewa  Barka da dawowa Hajiya
 Yawwa ! Ki zauna ina son yin magana da ke bayan Hajara ta zauna ne sai ta ci gaba da cewa  ki yi ha?uri in maganar da na yi miki ta Sata miki rai,sanin darajar mace Wakin mijinta shi yasa na yi miki sha'awar haka.To ina amfanin ZAWARCI? Kullum a takure,yanzu yadda nake da Daddyn yara bai baki sha'awa? Don Allah Hajara ki nutsu ki gane ?aunarki nake da rahama shi yasa nake so ki raba hanya da ZAWARCI ki tsaya ku sasanta ke da baba direba yanzu ma sai da yayi min zancen har kuWi ya bada na baki 


Wannan karon hawaye suka zubowa Hajara ta ce  to in sha Allah Hajiya zan yi tunani da wannan suka rabu ta koma Wakinta,a cikin wannan daren ne Hajara ta fitar da ruhinta ya zaga duniyar Soye ta samo sirrika sosai na cimma burinta.

Washegari da farin ciki ta farka,ta shaidawa Hajiya ta yarda baba direba zai iya zuwa su fara yin zance.Sosai Momah ta yi farin ciki har ta bari Hajara ta kama mata girki wanda a yau take son fara zuba mata magani,sai dai ha?arta ba ta cimma ruwa ba Habibah ta yi sallama a gidan.Gaban Hajara ya faWi rasss lokacin da suka haWa ido......
```MRS SADAUKI=ث?
'?```


My book is only 500 via
6042551755
Hassana ibrahim
Keystone bank,ko kuma katin MTN na 500? ?an Nijar kuma carte airtel ko Moov ta 500f sai a turo da shaidar biya ta WhatsApp +22795045822,in kin san ba ki biya kuWin karatu ba kar ki karanta min littafi domin mallakina ne .

___________________
09/10/24

25_26

=؛?=؛?=؛?GHT B-CLEAR,FEMALE CARE AND GANODERMA=؛?=؛?
=؛?=؛? *BACK TO VIRGIN KIT* *(SABON BUDURCI)*

=؛?=؛?Assalam alaikum Mata albishirin ku>???
@&?>???
@&?ga abin da kuka Dade Kuna mafarkin samu ya samu=؃?>?p?
=؛?=؛?Abin nema ya samu ,Kowacce mace aduniya tana mafarkin sake kasancewa virgin
=؛?=؛?Ina manyan Mata da suka hayayyafa=??
=؛?=؛?ina zawarawa masu shirin aure=?
?
=؛?=؛?Ina budurwa da iftila'i ya fadawa a yayin tsallaka rame =?"?
=؛?=؛?Ina Mai jego da keso ta dinke ta game tsaf ciki da wajed'?
=؛?=؛?Duk ku marmatso kusa ga GHT back to virgin set na kawo muku ,magunguna ne namu na gargajiya bana bature ba
=؛?=؛?Kuma Sha akeyi ,insha Allahu muddin kikayi amfani da wannan Kayan Zaki dawo da martabar ki ta farko
=؛?=؛?Sai kin gwada za ki tabbatar da hakan.
Sisters no 08142506271 mmn Khadeejah sai najiku



Ido cikin ido suke kallon juna kafin Habibah ta kawar da kai ta maida dubanta ga Momah ta ce  ina kwana anty?


 Lafiya lau alhamdullah ya gajiya ya ba?unta? Momah ta amsa tana mai nuna wa Habibar wurin zama, gajiya ta bi jiki,ina ?ata Feenat?

 Tana Waki tana shirin makaranta,Hajara kawo wa ba?uwa drink ki haWo mata da abin motsa baki Momah ta faWa .
Hajara ba ta ce komai ba ta wuce kitchen hannunta na rawa ta haWa komai a ?aton faranti kafin ta fito ta dire gaban Habibah ,aka yi sa'a kuwa sun ?ara haWa ido.Habibah ta sakar mata murmushi ta ce  anty wannan fa?

 ?ar aikina ce
 Oh ita ce ashe Mamar Murjanatu 
 Eh wallahi
 Ina kwana Ummu Murja Habibah ta faWa tana tsure ta da ido tana tantance ta,Hajara ta yi murmushin ya?e ta ce  lafiya lau alhamdullah,Hajiya ko ita ce ?anwar Alhaji ?


Momah ta ce  i ita ce

 Allah sarki ai ga ma kama nan  Hajara ta faWa tare da ?o?arin barin wurin Momah ta tsayar da ita  ki kaiwa baba di??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????reba abincinsa ko
Ran Hajara ne ya ?ara Sacewa,Momah ta yi murmushi ta ce  a dai yi ha?uri a je a saurare shi

Haka Hajara ta Wauki abincinsa ta kai masa,ba don ta so ba ta zauna suna tattaunawa dangane da maganar auren nasu.Tun Hajara na jiran ganin Habibah ta fito domin tafiya har ta gaji wannan yasa ta mi?e ta koma ciki,sai ta tarar da Safeenatu zaune kusa da ita suna hira wai ta fasa zuwa makarantar ma.



Sai dab da magrib Habibah ta yi musu sallama direba ya mayar da ita.Sai a lokacin kawai Hajara ta ji sukuni,bayan sallar isha'i Daddy ya kira ta cike da kulawa ya ce  Suley mai gadi yayi min bayanin komai,sannan ya bu?aci a kai kuWin sadakinki can ?auyen naku sai a Waura auren.Hajara kin ga dai ke ba yarinya ba ce da za a tsaya a yi ta jan magana wannan yasa na yanke shawarar gobe da safe sai ki shirya za mu wuce can ?auye


Da wani mugun sauri ta Wago kai ta ce  don Allah Alhaji a ?ara min lokaci,kuma in dai aurena kai ma za ka iya Waura min shi ba sai an wani je can ?auye ba


 To babu damuwa zuwa juma'a in sha Allah sai a Waura

 Allah kai mu Hajara ta faWa tana wani murmushi wanda ita kaWai ta san ma'anar shi.Daddy da Momah kuwa sun zata na farin ciki ne,haka ta mi?e ta koma Wakinta ta fara shirya wa Suley mugunta.


Tsakar dare Suley direba na zaune yana sauraren radiyo kamar yadda ya saba kullum a nan yake cika dare yana aikin gadi.Yana dab da tashi sai ya ji tamkar wata murya na yin magana,da farko can ?asan ma?oshi ne ?asa-?asa kamar wanda ake yi wa raWa a kunne.A hankali ya mi?e yana kallon can nesa da shi wurin lungu inda Daddy ke ajiye motarsa,da tunanin ko Sarayi ne suka shigo ba tare da ya sani ba ya doshi wurin sai ko kafin ya isa sai kuma ya ji motsin faWuwar bokiti a toilet Win tsakar gidan.A lokacin da ya yo baya sai ya ji muryar nan na sake yin magana cikin raWa surutu ne sosai amma ya kasa tsintar mi ake cewa,a haka ya ?arasa ga ?ofar yana buWewa kuma muryar ta yi tsit babu kowa a ciki amma yana jin tamkar an saka wani abu ana fuzgo ruhinsa.
 Oh wato yau na cika dare ne sosai bari na je na kwanta tun da har kwanyata ta soma juy.... zancen da bai ida ba kenan jin wani abu sulululu cikin ?afar wandonsa yana tafiya,jikinsa tuni ya Wau kyarma bai kai ga ida shiga tashin hankali ba sai da ya ji ha?oran halittar da yake kyautata zaton maciji ne ya gantsara masa cizo a al'aura.

A nan take ya suma ,sai a lokacin Hajara ta fito daga wandonsa tana juya idonta na maciji da suke fitar da wani haske.Cike da iya mugunta ta naWe shi da bindinta sannan ta yarSa shi can ga bangon Wakinsa,muguwar buguwar da yayi ta dawo da shi daga suman da yayi.A rikice ya shige Waki ya saka sakata tare da zumbule wandonsa nan yayi mugun gani yadda al'aurar shi ta wani bushe tare da ?an?ancewa kamar ta yaron goye.Dirshen ya zauna kamar ?aramin yaro yana kuka,har aka kira sallar asubah Suley bai kwanta ba.


Washegari dakyar ya iya zuwa masjid,bayan an gama sallah suka jero shi da Daddy ba tare da ya lura kamar ba a hayyacinsa yake ba ya shiga basa labarin yadda suka yi da Hajara .

Murya na Wan rawa ya ce  da dai an bar zancen auren nan har zuwa gaba,ka san gaggawa aikin sheWan ce

Daddy yayi murmushi ya ce  kar ka wani damu shi aure lokaci gare shi ai duk yadda Suley ya so botsare wa amma Daddy ya ?i yarda haka suka rabu.

Gari na wayewa Hajara na ta jiran ta ji zancen an janye aurensu amma shiru,ta tabbata kuma aikinta ya tafi daidai.Bakin window ta yi tsaye tana hangen Suley ya rabka uban tagumi yau ko rediyon babu a kusa da shi,ta saki murmushi tana juya kambun maitarta ta dam?e kurwarsa a zuci tana cewa  wato duk da ban yi niyyar kashe ka ba amma ka tunzura ni zan yi haka tun a gabanta ya fara kelaya amai tare da Waukar buta yana zaryar shiga toilet yana gudawa.


Sai da ta bari ya galabaita sannan ta fito da gudunta zuwa falo, Momah da ke zaune tana yi wa Safeenatu kitso ta ce  Hajara lafiya?

Kamar wata yarinya ta soma yarfa hannu ta ce Suley ne wai babu lafiya,amai da gudawa.
 Subahanallah Momah ta faWa a tare duk suka fito,halin da ta gansa ciki ne yasa ta kira Daddy ta shaida masa babu jimawa ya aiko wani yaronsa da mota suka wuce asibiti,Hajara haka ta yi ta kuka ta bi bayan su.

Ana zuwa asibiti aka soma duba shi duk wani gwaji sai da aka yi masa kafin result ta fito.Hajara sai murmushi take a Soye,a nan aka kwantar da Suley tana jin sojan nan na yi wa Daddy bayani da fa matsala.Babu jimawa sai ga Daddyn,da ya karSi takardar sai da ya Wago kai ya dubi Hajara kafin ya ce  amma ni ko lokacin da zan Wauke shi aiki bai ce min yana da HIV ba,ko ke ya sanar da ke?

Kai ta girgiza tana sharar ?walla yayin da kuma can ?asan ruhinta a sannu a hankali take cinye kurwar Suley.Ba ta son mutuwarsa ta zama abar zargi wannan yasa ta shirya plan Win nan ta jefa masa ?wayar cuta ta ?arya wacce da ace an sake yin wani gwaji za a ga ?arya ce.


A wannan ranar Suley ya bar duniya, faWar irin kukan da Hajara ta yi Sata lokaci ne cikin son kwantar mata da hankali Momah ke cewa  ki gode wa Allah ma da ya toni asirinsa ai da tuni ya li?a miki cuta kamar wacce za ta yi wani abun arziki haka ta faWa jikin Momah tana mai ci gaba da yin kukan ,gefe guda kuma ta na sakar mata da gubar cuta don ta ga alamu in ta yi wasa garin kallon ruwa kwaWo zai yi mata ?afa.


&Kwana uku ana zaman makoki duk jikin Momah yayi wani iri, sannu-sannu ciwo ke ratsa duk wata gaSa ta jikinta kafin a farga tuni Momah ta soma ciwon jiki da kuma na ?afa.Kullum cikin shan magani take da kuma na shafawa wanda Hajara ce ke bata su,hakan ya kwashe wata Waya currr kafin ta faWi kwanciya .


Hankalin Daddy a tashe ya kwashe ta zuwa asibiti,suna zuwa aka bata gado.?arin ruwa aka saka mata don kawo sau?in raWaWin azabar da take ji yayin da kuma Hajara ke gefe ta ?ure ledar ruwan da ido tana sauya musu kala daga fari zuwa gurSatacen jini.A wannan ranar ne kuma ta yi nasarar gar?ame zuciyar Hajiya ta yi mata mugun kamu,da ta gwada yi wa Daddy sai kuma ta kasa juya shi saboda yana da yawan bautar Ubangiji.



Momah na daga kwance ranta ya kawo gargada ta buWe ido ta kalli Hajara ,da hannu ta yi mata nuni da ta zo.Ta kuwa taso ,murya na Wan rawa ta ce  in kin koma gida ki taimaka ki haWa kayan Safeenatu wuri guda a kai su wurin Habibah 

Hajiya da ke gefe ta ji sarai abin da ta ce sai ta goge ?wallar da ta ciko mata ido don duk mai hankali zai fahimci Momah wasiyya ce take bayar wa.

 Habibah tana Maradi wurin biki wata ?awarta ke aure cewar Hajiya .
Momah ta ce  babu komai sai ta zauna wurin ki kafin ta dawo

Hajara ta ce  haba Hajiya ya kike magana haka? Ni mine ne amfani na da ba zan kula da Safeenar ba kafin ki dawo?

Momah ta girgiza kai ta ce  ba zan tashi ba,ciwona ba mai warkewa ba Hajara .... sai kuma ta hau yin tari daidai nan Daddy ya shigo,da sauri ya isa ya tallabe ta bakinta sai fitar da gurSatacen jini yake amma a haka ta shiga maimaita kalmar shahada sai da ta yi wajen goma sha kafin ranta ya Wauke cak.Hawaye suka sirnano daga idon Daddy,yayin da Hajara ta fita a guje tana kuka ta kira likita .Cikin abin da bai wuce minti goma ba aka fitar da gawar Momah daga Wakin zuwa can mutuware ,tuni aka fara shaida wa mutane zancen mutuwar.Habibah wacce ke tsaka da shagalin biki labarin mutuwar matar yayanta ya zo mata,haka tana kuka ta biyo Bus ta ?arfe biyu ta dawo zinder lokacin kuma tuni an tafi rufe Momah.A tsakar gida ta zauna dirshen tana kallon yadda ahali suka cika gidan,tana nan tana sharSar kuka Daddy ya shigo ya mi?a mata dara(zanen gado) wacce aka rufe gawar Momah da ita.Haka ta ?an?ame zanen tana wani kuka mai tsuma rai, Safeenatu kuwa duk wanda ya ganta sai ya tausaya mata hatta Murjanatu ta ci kuka sosai.



Jikin Habibah ta zo ta faWa tana cewa  wai da gaske Momah ta mutu ba zan sake ganin ta ba? ba ta ce mata komai ba sai rungume ta da ta yi suka ci gaba da kukan.Daddy na shigo wa Safeenatu ta yun?ura ta je shi ma ta ri?e shi gam tana ce masa  Daddy ka kai can wurin Momahna ni zan zauna da ita,don mi za a rufe ta babu wanda ya tsaya a can.Daddy ina son ta ba zan iya rayuwa babu Momah ba,gidan duk babu daWi Daddy don Allah ka taimaka ka maido ta
Kamar ba soja ba haka shi ma Daddy ya soma hawaye tare da jan ta zuwa can ciki,Wakinsa ya kai ta kamar wata mai wasu shekarun hankali ya dinga yi mata nasiha daga ?arshe ya bata maganin bacci ya fito.



Yin mutuwa ba ya hana a ci abinci,haka aka soma raba abinci kamar wani gidan biki mutane suna ci suna hira kai kace ba gidan makoki ba.Hajara ita ce gaba wurin yin komai don in aka fidda Daddy a yanzu babu wanda zai fi ta sanin sirrin gidan,Habibah dai sam matar nan ba ta kwanta mata ba haka take jin tsanarta.Shi yasa ko girkin ba ta ci ba,fura ta dama da madara ta saka Safeenatu gaba bayan ta tashi doli ta sha kafin ta lafe jikinta tana hawaye.Sallah kawai ke tada Habibah daga wurin da ta zauna har dare yayi aka watse,gidan yayi saura sai dangin Momah na kusa da kuma na Daddy.


Tun zuwan Hajara gidan yau ce kawai ranar farko da Safeenatu ta raba shimfiWa da Murjanatu ta je jikin Habibah ta kwanta.Zanen nan dai da aka luluSe gawa Habibah ta rufa musu suka soma bacci,sai dai sam baccin tamkar wacce ake yi wa wahayi haka ya kasance wurin Habibah .


A cikin ma?abarta ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login