Showing 129001 words to 132000 words out of 139076 words

Chapter 44 - ZAWARCI COMPLETE HAUSA NOVEL

14 Oct 2025

125

sama,zan mayar da nurse in na dawo zan shigo na same ki tana kuka ta ruga da gudu ta haura sama yayin da kuma ya watsawa matar harara wacce nake tunanin matarsa ce,ita ma barin wurin ta yi.



 Ka faWa wa ungulu ta koma gidanta na tsamiya,domin gidan rama ba nata ba ne gimbiya Layya ta faWa .
Kai tsaye na amsa mata da cewa  kar ki taSa tunanin Wan ?aramin siddabarunki zai tsorata SEERAT! Wannan Win ba komai ba ne a wurina face wasa yara, ki sa a ranki kuma ni ce nan zan ruguza ba?ar tawagarki ta matsafa ina gama faWa na ware tafin hannuna na hagu na cilla ta can sama sannan ta bugu ga ?arfen bene har goshinta na fashewa.


Da sauri Uwais ya nufo ni yana cewa  don Allah ki rabu da ita,tana da ciwon kwanya ne ita Win mahaukaciya ce fa ko ba ki lura da hakan ba tun Wazu

Na yi wata dariya na ce  au haba? Sai yanzu na lura ka san ba kasafai ake gane haukan mutum uku ba,attajiri,malami da kuma sarki to ita ma ka san basarakiya ce ta matsafa ina gama faWa na saka idona cikin nata tare da yi mata murmushin ?eta, Uwais ne ya ja ni muka fito.


Wannan karon da kansa ya karSi key zai yi draving Wina,sai bayan mun fita daga cikin masarauta sannan na ce  amma mi yasa na ga kamar duk kuna tsoronta?


 Ba kama ba ce haka Win ne,kaf masarautar yanzu ?ar?ashin ikonta muke.Ni ne mai Wan sau?i saboda ina Wauke da abubuwan sirri na mai martaba,ciki kuwa har da sar?ar wuyansa wacce ke bani damar shiga sashen da yake a yanzu.


 To amma mi zai hana kai ka hau karagar mulkin kafin Sarki ya samu lafiya?

 A'a bana bu?ata gaskiya,Yarima ne ya cancanci kujerar ba ni ba.Amma na tambaye ki wannan abun da kika yi wa gimbiya Layya mine ne shi?

 Ni kaina ban sani ba kawai dai na san ina iya sarrafa hannuna na motsa abubuwa da shi

Ya ja numfashi kafin ya ce  amma kin san da yau sai sun ya?e ki ko?

 Eh na sani! Yanzu haka na matsu ka sauke ni akwai da wacce nake son yin magana

 Ki kira ta izuwa nan mana

 A'a ba za ta zo ba

 Saboda me?

 Kana Wauke da sar?a mai hoton tambarin masarauta

Ya saki murmushi kawai kafin ya ce  kin san mene ne ainihin asalin tambarin nan?

 A'a sai ka faWa 

 To gimbiya Zahra'u ce ta fitar da shi,ita wacce kike ikirarin kina son ganinta za ku yi magana Yayar mahaifiyar Khaleed ce.Ita ce babba sannan Zahra'u ni kuma autansu,tun muna yara ra'ayoyinmu suka sha banban da na juna musamman yadda ita Bintu take da mugun son abin da ya shafi tsatsubai ni kuma da gimbiya Zahra'u bar mu da tilawar Alkur'ani wanda hakan ashe yana ba?anta ranta ba tare da ta san dalili ba sai ta shiga zana hoton wani tambari wanda shi Win ya kasance ashe na wata masarautar jinnu ne,a lokacin da ta nuna wa Zahra'u ita ma sai ta zana wannan Win wanda yake Wauke da sar?ar wuyanmu daga nan suka fara rigimar cewa na wa ya fi kyau.Ana cikin haka ne wani iska mai ?arfi ya taso ya mamaye duk illahirin farfajiyar wurin,a gaban idonmu wani abu mai kamar inuwa ya bayyana yayi sama da Bintu wato Bafulatanarki,yayin da mu kuma aka cilla mu gidan sarki Hasheem mahaifin mai martaba a lokacin shi ke mulki .Tambarin Zahra'u shine abu na farko da ya Wauki hankalinsa da ya tambaye ta nawa za ta sayar masa sai ba ta ce komai ba sai kuka da take yi,ni ne na yi masa bayanin abin da ya faru jin haka sai ya zuba malamai aka soma karatun Alkur'ani yayin da kuma Waya Sangaren ya sa aka yi amfani da tambarin gimbiya Zahra'u matsayin na masarauta.Kwana uku da Satan Bafulatanarki sai aka tsince ta a ?ofar masarauta,sama da sati biyu kafin ta farfaWo mun yi murna sosai sai dai sam ba ta yin magana yana kawo wa nan sai yayi shiru.


Na ce  amma iyayenku fa?
 Duk sun rasu
 To kenan Bafulatanata fatalwa ce?
 Eh kusan haka ne tun da esprit Winta ne ke yawo
 Mi ya jawo hakan ?
 Ta auri wani mutum ne a nan garin tana tsananin sonsa amma kuma cutar da ita yake har dukanta yake,wata rana tsautsayi yasa ya dake ta ashe aljanin da ya taSa tafiya da ita har yanzu yana jikinta kawai sai ta Wirka wa mijin uban duka har sai da ya suma shine a ?arshe ya sake ta



Shiru na yi kawai ina nazari maganganun sa,sam ban yarda da su Wari bisa Wari ba,amma tuni ya kawo ni gida sai na fita ina yi masa sallama.Ko da na shiga ciki mutanen da na tarar tsiraru ne duk sun tafi aiki,kan ?ar katifata na haye sannan na kira Yaya Khaleed.Sai da na jera wajen kira biyar,a na shidda ne ya Wauka.


 Shine sai yanzu ka Wauka na faWa a shagwaSe.
Ya ce  ki yi ha?uri babyna, wallahi abubuwa ne sun yi yawa.Wata shari'a ce aka yi munafurci ya yi wa ?ar aikinsa fyaWe a ?arshe ya kashe ta amma a haka tsabar zalunci ka tauye ha?in yarinyar aka basa gaskiya saboda iyayensa nada kuWi,to amma kin san me?


Da sauri na ce  a'a sai ka faWa 
 Wallahi ya haukace ! Sai hauka yake yana faWar sunayen ?an matan da ya lalata

Na saki murmushi na ce  Alhamdullah! Shi yasa ba kowanne mahaukaci ne ya kamata ya bamu tausayi ba,wani Allah kaWai ya san mene ne silar haukan nasa.Ita ainahin wacce ya yi wa fyaWen tana Wauke da ba?in iska wanda ya aure ta shekara da shekaru,shine ya haukata shi amma kai abun ya bada citta  na faWa tare da yin dariya sai na ji an kwaikwayi dariyar tawa cikin muryar Seraye.


Shiru na yi ina baza ido amma ko alamun Sera ban gani ba don babu wasu kaya sosai a Wakin ballantana na ce a can ya Suya.

 SEERAT ? Kina ji na?

 Eh Yaya ina ji na faWa tare da ?o?arin saita nutsuwata sai dai abu ya cuttura saboda ina ji a jikina kamar ana ankare da duk wani motsina,duk sai na tsargu.
 Yaya zan kira ka daga baya na furta tare da kashe kiran ,kamar wata mahaukaciyar na ce  to ina sauraren ku me kuka zo nema wurina? shiru babu amsa sai labulayen Wakin da suka soma kaWawa,yayin da ?wan lantarki ya soma wasar yara ya kunna kansa ya kuma kashe kansa.



 Ah to na fahimta wasa kuka zo yi ashe to ku ci gaba in kuna da magana bayan hakan sai ku taSo ni na faWa tare da saka airpix a kunne,hoton mai martaba kuwa Ammy Habibah na turawa shi duk da kuwa ina cikin fushi da ita.Kamar wacce ke jirana dama ina turawa ta buWe,sai kuma ta kira ni video call kamar ba zan Wauka ba sai kuma na Waga.Sai da wayar ta kusan kubce min saboda ban shirya ganinsu ba,wasu baba?un fuskoki ne suka bayyana a screen Win wayata dukkansu suna zaune a bayana sun zagaye ni........
```MRS SADAUKI=ث?
'?```


My book is only 500 via
6042551755
Hassana ibrahim
Keystone bank,ko kuma katin MTN na 500? ?an Nijar kuma carte airtel ko Moov ta 500f sai a turo da shaidar biya ta WhatsApp +22795045822,in kin san ba ki biya kuWin karatu ba kar ki karanta min littafi domin mallakina ne .

___________________
BOOK3


23_24



Ina ?o?arin kashe kiran amma Ammy Habibah ta dakatar da ni, su wane ne suka kawo miki ziyara SEERAT? 

Ban kai ga bata amsa ba na ji an sha?e min wuya a dole na saki wayar domin ?watar kaina,amma ina tuni sun yi min ?awanya ta ko ina sai duk na rasa yadda zan kuSutar da kaina kamar ?uda a cikin ?ullun waina.

Idona har wani lummm suke tsabar yadda nake jin azaba ta ko ina,sai kuma na ji tsit kamar cirar ?aya komai ya tsaya.Na ri?e wuyana da dukkan hannuwana ina jawo numfashi,kamar daga sama nake jin muryarsa  SEERATna??? sai kuma ya tallabo ni ya rungume ?am a ?irjinsa,dakyar na ?o?arta na ce  Yaya Khaleed zan mutuuu! bai ce min komai ba sai bakinsa da ya Wora kan nawa ya dinga shayar da ni yawunsa waWanda suka zame min tamkar maganin waraka.


Ras na dawo normal,na janye jikina daga nasa ina kallonsa kafin na ce  ya aka yi ka zo nan alhalin ba mu daWe da ida waya ba kana Yamai?


 SEERAT na sha faWa miki duk wannan abin da kuke kira baiwa duk sharrin sheWanu ne da fatalwa,in na ce miki ga ta?amaimai hanyar da na bi na zo nan to na yi miki ?arya.Ni dai kawai na san na ga tsuntsuwar nan kuma sai na tsinci kaina a nan,haka zuciyata ke faWa min wai kina cikin matsala


Na lumshe ido ina zancen zuci  tabbas dakwai banbanci tsakanin mutanen da na ya?a a can baya da kuma su gimbiya Layya da tawagarta! Mene ne suke ta?ama da shi? Duk ?arfin tsafi ne ko me?  na tambayi kaina ba tare da kuma na samo amsoshin ba na ware idona ga Yaya Khaleed.



 Meke faruwa SEERAT? Ji nake kamar yanayin iskan garin ya sha banban da na saura

Shiru na yi ban basa amsa ba saboda bayyana Bafulatanata a can bakin ?ofa ta yi wata tsayuwa da fararen kayanta tana kallona.Ni ma ido kawai na zuba mata,can ta gaji ta ce  za ki kirawo Basheer domin wannan ba aikinki ba ne nasa ne,ke Win wurin ajiyarsu kawai kike da.Ki tabbatar duk kin kwashe su kin zuba su a sar?ar wuyanki kar ki manta a cikin masarauta akwai mutum Waya mai fuska biyu naki ne gano kowane mutum ne tana gama faWa ta fice,daidai nan kuma wayata ta Wau ruri.


Na jawo na duba sai na ga sunan Ammy na yawo kan screen,da sauri na Waga sai na ji ta ja wata doguwar ajiyar zuciya tana mi cewa  Alhamdullah! In sha Allah zuwa gobe muna shigo wa ,yanzu haka tuni na haWa kayana zan zo

 Ku tawo tare da Basheer  na faWa da sauri.
 To babu damuwa sai kuma ta kashe,jikin Yaya Khaleed na je na shige ina jin wata irin kasala ga kuma yunwa .

 Yunwa nake ji na faWa wasu guntayen hawaye na zubo min.
Rigata ya Waga ya soma shafa cikina,bai kai ga yin magana ba muka ji tsayuwar mota kafin kuma sallamar Uwais.Da sauri na tashi zaune ina cewa  Yaya Khaleed don Allah ka Suya ban so su san ka zo sai dai ko kafin na rufe bakina Uwais ya shigo hankali tashe,a tare muka mi?e .


 Masarauta ta hargitse suna can sun tada bori suna kiraye-kirayen sunan aljanai Uwais ya faWa kamar zai yi kuka idonsa ?urrr kan Yaya Khaleed wanda shi ma Win Uwais yake kallo.

 Ka zauna zan je na dawo na faWa ,Yaya Khaleed yayi min wani kallo irin tun da mahaukaci ne ni.
 Mu je ya furta yana yin gaba, da sauri na biyo shi ina mai cewa  Yaya Khaleed don Allah kar ka je wallahi kashe ka za su yi,mutuwa za ka yi don Allah ka tsaya na kamo hannunsa hankali tashe don tuni duk an nuna min komai a mafarki muddin ya shiga masarauta to yayi ban kwana da duniya.



 WaWanda suka nuna miki hakan ki faWa musu sun yi ?arya Yaya Khaleed ya faWa tare da buWe mota da kansa ya shiga ,ni ma a dole na shiga dafe da zuciya.

Kamar Uwais zai tashi sama haka yake gudu,ina son yi wa Yaya Khaleed tambayoyi amma bai bani fuska ba.Muna isa masarautar sararin samaniya ya Wauki wani launi mai matu?ar firgitar wa,duk wani matsafi da ke wurin sai hankalinsa ya dawo gare mu.

Karon farko kenan da na ji tsoron tunkarar mugu saboda waWannan Win siffarsu ma kawai abar tsoro ce,bayan Yaya Khaleed na Suya ina mai ciro sar?ar wuyana.Daga inda nake a laSe nake jin sautin muryarsa yana karanto ayoyin tsari da kuma na ya?ar duk wani matsafi.

 Ku zo mu shiga daga ciki cewar Uwais,har mun bi bayansa sai kuma muka tsaya cak sakamakon wani iska da ya turnu?e wurin,wata dun?ulalar guguwa ta tawo tun daga sama har ta dira ga ?asa.

Na waro ido ganin Basheer a tsaye cikin wasu kaya kamar na mafarauci.Gimbiya Layya da ma?arabanta duk suka yi baya suna waro ido , Yaya Khaleed ka shiga daga ciki mai martaba na neman agajinka,kai kaWai ne ke iya yin wannan aiki ni kuma ka bar ni da SEERAT 

 A'a ba ta da wani ?arfi,zan shiga da ita cewar Yaya Khaleed.
Da sauri na ce  ka shiga kawai za mu yi aikin tare da Basheer sai na saki murmushi ganin karon farko mafarkina bai zo daidai ba duk an sauya shi a zahiri,Uwais ne ya ja hannun Yaya Khaleed suka shiga ciki.


Na matso na yi tsaye bayan Basheer ina cewa  ta ina za mu soma?
 Ki yi min shiru Malama kar ki Sadda min lissafi Basheer ya katse ni yana mai ci gaba da karanto wasu sunaye waWanda na tabbata na jinnu ne,sannu a hankali kuwa na soma ganin irin inuwar nan na cika masarautar.


 Wannan Win cin amana ne mai girma Shakal! Sam wannan bai dace da tsarin mulkin duniyar Soye ba,kai ne da kanka ka shimfiWa mana dokoki yanzu kuma shine za ka karya su ? Mene ne laifinmu don mun nemi adalci? gimbiya Layya ta faWa tana zarar ido .

Basheer ya buWe baki ya soma yin magana sai dai sam ba muryarsa ce ba ta wani tsoho ce, Layya kar ki manta aljani bai da gaskiya,cin amana wannan shine babban jigonmu.Kin yi min al?awarin bani abubuwa dayawa amma ko Waya babu wanda kika cika,Wan ?aramin tambarin ma kin kasa sauya wa to ina ga ?ona duk wasu takardun tarihi.Wacce ke da burin canza tambarin masarautar nan yanzu ta ce ba ta da muradi don haka kashe ki zan yi yana gama faWa ya jefa mata wata ?ar ?aramar ?usa da ya fitar daga bakinsa,sai dai tun kafin ta cake ta cikin tawagarta wani ya tare ?usar ta huda ?irjinsa ya faWi ?asa a mace.


Hankali gimbiya Layya ya tashi,tsoron mutuwa ya fito kan fuskarta ?arara.Duk yadda Basheer ya so kashe amma abu ya cuttura,cikin wata irin murya ya ce  SEERAT yi amfani da tafin hannunki ki ruguza min taronsu  ko bakinsa bai rufe ba kuwa na aiwatar .

Tamkar fankon gyaWa haka duk suka watse suka yi sama cikin iska sai a lokacin ya samu ya caki gimbiya Layya ta zube ?asa dafe da saitin zuciya,Basheer ya ce  yi sauri ki jaye ta ki adana ta cikin sar?arki kafin ta fara aman powerta ban san dalilin duk saka mutane a cikin sar?ar ba,amma haka na cilla wa gimbiya Layya ita nan kuwa kifin ya haWiye ta.


Gefe na koma ina kallon yadda Basheer yake fatattakar matsafan da suka yi fito na fito,sai bayan ya gama kawai ya zube ga ?asa .Da sauri na nufe shi ina mai jijiga shi dakyar yake ware idonsa waWanda suke canza kaloli kamar hawainiya.

 Ruwaaa! ya furta kamar ransa zai fita,bai ko rufe bakinsa ba sar?ar hannuna ta soma feshin ruwa,da na duba sai na ga kifin nan ne ke amansu.


Sai bayan ya sha ruwan ne sannan ya karSi sar?ar hannuna ya soma kaWa ta kamar majaujawa,abun mamaki duk gawarwakin da ke zube a ?asa suka soma tashi sama suna bin iska tamkar haya?i haka suka Sace.


Bayan ya gama ne ya mi?a min na mayar da ita a wuyana,sai a lokacin muka shiga daga ciki.Duk yadda Basheer ya so bin bayana domin mu shiga part Win da mai martaba yake amma abu ya cuttura ya kasa ?etara ?ofar.

Da mamaki nake dubansa na ce  ka shigo mana
Ya girgiza min kai yana nuna min saitin zuciyarsa wacce ta kumbura.Ban san lokacin da na saki ihu ba,Basheer yayi baya zai faWi amma na taro shi.

Uwais da Yaya Khaleed suka fito suna tambayar ba'asi,na sanar da su.Sai na ga yanayin fuskar Uwais ya canza, mene ne? na jefo masa tambayar.

 Sai ha?uri gaskiya,ina ga sarki Shakal na son janye Wan uwanki izuwa waccan duniyar.

 Akan wane dalili?

 Saboda a cikin jikinsa ya girma,Basheer ba zai taSa dawowa normal ba muddin ya zauna a wannan duniyar.Wannan kumburin na zuciyarsa ba komai ya haifar masa da shi ba sai musulman aljanan da ke gadin sashen mai martaba,su Win sun kasance abokan gaban sarki Shakal in ba ki manta ba na baki labarin tambarin gimbiya Zahra'u da kuma na Bafulatanarki,to ita kanta gimbiya Zahra'u tana Wauke da aljanai amma su Win musulmai ne kuma tambarin masarautar nan ainahin nasu ne


 Duk ku bar zancen tambarin nan don Allah ku yi tunanin yadda za sama masa lafiya,a duk duniyar nan babu wanda ya isa ya yi maka wani abu sai da yardar Allah don hakan zancen tambarin gimbiya Zahra'u da na wata Bafulatana duk bai shafe mu ba. Yaya Khaleed ya faWa tare da tsuguno ya Wora hannunsa ga goshin BASHEER,yana soma yi masa karatu zuciyar ta soma yin motsi sosai yayin da kuma ya soma shure-shure.Mun shagala sosai akan Basheer na ga kamar mutum ya shiga sashen sarki da sauri na nufi Wakin, dakata!  na furta ganin wata mace hannunta ri?e da wu?a sai ta juyo jikinta na kyarma sai ta yi wani ihu tare da Waga wu?ar ta yo

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login