Showing 51001 words to 54000 words out of 231169 words
takesha bazata yi karyan batada lafia ba tunda ya ganta jiya a wurin dinner... ganin batada mafita kawai ta shiga yarfa hannayenta hawaye na turereniya kan cheeks dinta tace"am...sor..ry"..Matron tace"ko dan gaba baa yin irin haka a asibiti..da kikasan bazaki zoba sai samu wata ta rike maki amma ba ki tafi ki bar patients on their own ba sbd ba wanda zaiyi tunanin su kadai ne...ba don Allah ya taimaka wadan nan sunzo jiyan ba da kilan asarar da zamuyi sai yafi haka"..kuka kawai takeyi tana gyada mata kai...Bobby ya zaro kudi a aljihu ya mikama mutum biyu da suka taimaka suka rike dakin snn yayi musu godia suka wuce...Matron da taga yanda ranshi ke 6ace tace"ayi mata uzuri dr kaga yarinya ce..zanyi mata fada inshaAllah bazata sake aikata makamancin haka ba"...bai ko kalleta ba bare tasa ran zai amsa idanunshi kan Aysha da har yanxu bata bar kuka ba yace"wuce muje"...a rikice ta dago tana kallonshi...ya zuba mata idanun nan nashi aikuwa ba shiri ta wuce gaba tana cigaba da kukanta...haka suka fito daga ward din tana gaba yana binta a baya har zuwa office dinshi...karasawa yayi seat dinshi ya zauna fuskan nan ba sarari yace"sbd bakida hankali kika wuce kika barmin patients su kadai dan bakisan aikinki ba koh?..anya kuwa bada malpractice kikayi passing Clinical skills dinki ba?.."dukda halin da take ciki mgnrshi ba karamin kular da ita yayi ba...wato ita yake nufi tana satan amsa amma Allah ya isanta wlh...cikin daga murya yace"are u deaf ina miki mgn zakimin shiru?..are u sick?.."runste idonta tayi sabbin hawaye na sake gangaro mata...itadai yau ta shiga uku da masifan wnn mutumin...sai ihu yakeyi mata kaman ita tajs ta shaqe matar ta kasheta...shima runste nashi idon yayi yana murza goshinshi trying very hard to control his temper don idan ya biye ta zuciyarshi yana iya gaggaura mata mari sbd haushin datake bashi...what did she think of herself da zai ringa mata mgn tana banza dashi...ganin bafa shiru zatayi ba ya buga table din gabanshi cikin karaji yace"kin rufemin baki ko sai na gaura maki mari a wurin...are u even alright da zaki sani a gaba kina min kuka?..are u mad?.."ya karasa mgnr cikin tsananin 6acin rai...sbd tsoratan da tayi batasan time data hadiye kukan nata tana toshe baki da hannayenta ba...shi kuma yacigaba da fadin"from today onwards aikinki ya dawo office dina...ke zaki dinga cleaning min office kullum kina wanke toilet dina...snn duk wani aike na office dina ke zaki dinga zuwa zan sallami cleaner da messenger dina har zuwa lokacin da zaki gama punishment dinki...if u like ki tafi gidan biki ku hadu da saurayinki kiqi zuwa aiki kiga yanda zanyi dake lazy fellow kawai"...har yanxun idanu a lumshe take sauraronshi...wato ma itace zata zama mishi cleaner kuma messenger sbd bashida imani...kuka kawai takeyi har yanxun batace mishi qala ba...shi kuwa kallonta yake har yanxu yana ganin yanda dimples dinta ke fitowa as a result of kukan da takeyi...ya sake daure fuska snn yace mata"go to the Nurses Station kice ina kiran Zarah"...ba tareda ta bude idon ba ta juya ta fita a office din...saida ta tsaya ta gama clearing face dinta dukda tasan a banza dan ana ganinta za'aga alamun kuka tattare da ita snn ta wuce nurses station din...tare suka fito sa nurse din zuwa office dinshi...Aysha taja gefw ta tsaya tana daure fuska dan a ganinta sbd tana mishi kuka ne yasa yake raina mata wayo...Zarah ta karasa bayan ta gaisheshi yace"how many files do we have?.."tace"they are many sir.."yace"ohk kuje da ita ki bata ta kawo and kina iya tafiya gida u are done for today"...nan da nan ta washe baki hadda risinawa tace"thank u sir"...Aysha ta maka mata wani harara a kan idon Bobby dake kallonta ta gefen ido...cikin ranta tace"azzaluma ba dole kiyi godia ba"...saura kadan daria ya subuce mishi sbd ganin yanda tayi hararan kaman idonta zasu fado kasa...tare suka sake fita Zarah ta hadata da uban files na patients din da zai gani yau snn ta koma office din nashi ta kai mishi da kyar take iya dauka sbd nauyinsu...ta ajiye mishi su nan gabanshi snn taja baya ta tsaya tareda rungume hannunta...yace"zo kiyi arranging files din according to their numbers"...sake daurw fuska tayi ta matsa ta janyo kujera zata zauna yayi saurin dakatar da ita da cewa"and who ask u to seat?.."shiru tayi tana kallonshi yace"C'mon get started before i loose my temper with u...ba dai aikinki tafia gidan biki kina barin patients su kadai ba?..as small as you are har kinsan ki hada Ap da saurayi ya sameki wani wurin sbd ba gaban parents dinki kike ba kou?..i know exactly how to deal with people like u..now start what i asked u see the other side of me"...a hankali ta matsa gaban table din ta kai hannu ta janyo files din gabanta...har zata fara dubawa ta tuna batasa glasses dinta ba dan haka ta mike zuwa inda bag dinta ke ajiye ta dauko glass din ta saka snn ta sake komawa ta fara abunda ya sata...shidai yana zaune yayi crossing hands dinshi a kirji yana kallonta...Allah ya taimaketa gaba daya files din a jere suke according to numbers dan haka ta dago tana kallonshi tace"Sir a shirye suke"...without looking at her yace"call the first person"...cikeda haushi sosai take kallonshi jin abunda yace..ta kalli bell dake gabanshi dannawa kawai fa zaiyi patients din su fara shigowa amma bazai iyaba sbd dole sai ya bata wahala...ganin wasu hawayen na sake ciko idonta ta dauki file din farko tareda juyawa ta fita sai gasu sun dawo ciki da me file din...ya nuna mata wuri ta zauna ita kuma Aysha ta kwashi files din gaba daya zata fita dasu yace"where do u think u are going?.."ba tareda ta juyo ba tace"waje.."yace"su kuma files din suyi mene a wajen?..and ke kanki waya baki permission din zuwa waje?.."saida ta hadiye tears dinta snn tayi qundunbala ta juya tana kallon tsakiyar idonshi trying so hard ta 6oye tsoronshi dake cikin nata idanun tace"sai nacigaba da turosu daga waje"...kallon tsakiyar nata idanun shima yayi kafin yace"zo ki ajiyemin files and if u dare step out of this office sai na baki mamaki wlh"...sauke idonta qasa tayi tareda lumshe su allowing tears dake ciki fitowa kan cheeks dinta...ai ita tasan ta gama yawo tunda ta fada hannun wnn azzalumin...bata damu data goge hawayen ba ta maida mishi files din gabanshi kaman yanda yace snn ta koma gefe ta tsaya tana cigaba da hawaye...hankalinshi ya maida kan patient dinshi yana mata tambayoyi...Aysha tayi mamaki sosai yanda taga yana interacting da patients din nashi sam batayi zaton haka daga wurinshi ba...gani take ko patients din ma zare musu ido zai ringayi yana daure musu fuska amma sai taga ba hake yakeyi ba sam...mgn yakeyi dasu full of attention da kuma concern kamar dai ba arrogant and wicked Proprietor dinsu ba...haka yacigaba da attending patients dinshi tana tsaye saidai idan ya gama yace ta kira next patient and ba yanda ta iya haka tayita sintiri from office dinshi zuwa waje...legs dinta har sun fara mata ciwo sbd tsaiwa ga wnn kai kawon da takeyi shima ba karamin wahala ne dashi ba...ga patients din da masifan yawa dan gani take kaman ma karosu akeyi ace tun dazu suna abu daya amma har yanxun sunki karewa...har aka kira sallahn magrib basu kammala ba...zuwa yanxun karfinta ya gama karewa tass neman wanda zata saukema kukan dake cinta kawai takeyi amma babu dan haka ta jingina da bango tareda kai hands dinta ta rufe fuskanta dasu ta shiga rera kukanta a hankali...Bobby na jinta baice komai ba har ya sallami wadda take gabanshi snn ya mike zuwa bathroom yayo alwala ya fito ko kallon inda take baiyi ba ya fice zuwa masjid...tana jin ya fita ta zauna nan kasa zaman dirshan ta dora hannu a kanta tana rushewa da wani matsanancin kuka...kuka take sosai dan idan ka ganta zaka ranste da Allah wani gagarumin abun akayi mata...saida ta shafe kusan minti goma tana abu daya kafin ta mike da sauri kaman wanda ta tuno wani abu ta dauki bag dinta tana goge hawayenta ta bude office din ta fita...a bakin kofa sukayi karo dashi yana tsaye ya zuba mata ido kaman yasan abunda take niyyar yi yace mata"waya baki permission din tafiya?.."takai hannu ta goge tears dinta ta bude baki da kyar sbd kukan da taci tace"Sir...dan..Allah...inje gida...wlh na gaji...kaina namin ciwo"...kallonta kawai yake yanda tayi mgn dama tun ba yanxu ba yasan sangartacciya ce so baiyi mamaki ba sam...baice komai ba yakai hannu ya bude kofar office din yana binta wnn kallon da bataso cikin stern voice dinshi yace"get in.."yarfe hannu ta farayi tana dan bubbuga legs dinta a kasa da alama abun ya motsa cikin shehssheka tace"Sir dan...Muhammdu...Rasulillahi...dan darajan..."kasa karasawa tayi sbd ido daya tsareta dasu...haka nan ta juya ta koma office din sabbin hawaye na sake antayowa fuskanta...shima shiya yayi ya maida kofan ya rufe snn ya karasa seat dinshi ya zauna...ya duba sauran files da suka rage mishi yaga guda uku yasan idan yace ta kirasu 6ata mishi time zatayi dan haka ya danna kararrawa ba dadewa wanda yake kan layi ya shigo...wuri ya nuna mata ta zauna snn ya shiga attending dinta...Aysha dai har yanxun tana tsaye tana kuka kaman wanda akama dan banzan duka...ganin bafa dena kukan zatayi ba daya sallami ta gabanshi sai ya juya yana watsa mata harara yace"ke kinada hankali kuwa?..office din nawa zaki maida wurin iskancinki are u insane?.."banza tayi dashi tana cigaba da kukanta...ya daka mata tsawa yace"are u deaf"...ai batasan lokacin data hadiye ragowar kukan ba sbd tsabar tsoratan da tayi...ya nuna mata wani seat dake kusada ita yace"seat down and keep shut...idan kika sake na sake miki mgn you will see the other side of me"...ba musu ta zauna kan kujeran tana kunshe kukanta...haka tayita zaune har ya karasa ganin patients din snn ya mike ya tattara kayanshi ya dau keys da wayoyinshi ba tareda ya kalleta ba yace"leave my office immediately..and make sure gobe ki fito da wuri kimin clearing office idan ba hakaba zakiga yanda zanyi dake"...tun kafin ya karasa ta bude office din ta fita da sauri tana sakin kukan da take rike dashi tun daxu.
Rano✨
Wnn littafin na kudi ne...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556.
18
Parking lot ta zauna tacigaba da rusa kuka kaman wadda aka aikoma saqon mutuwa...tana nan zaune taga fitar motanshi aikam tabi motan da harara kamar idanun zasu fadi...saida tayi me isarta snn ta daga waya ta kira besty dan yazo yayi picking dinta...yana dauka ko mgn kasawa tayi kawai ta rushe mishi da kuka...a rikice sosai Sa'eed ke tambayan abunda ya sameta amma ko uffan batace ba sai azabar kuka take...daga karshe sai ya kashe wayan kawai snn ya dauki hanyan Hospital dama he is near by so within few minutes ya iso...da sauri ya karasa inda ya hangota zaune tana kuka shima ya zauna nan gefenta hankalinshi duk a tashe yace"besty dan Allah what is it?..why are u crying like this?..are u sick?.."girgiza mishi kai tayi meaning she is fine...yace"then what happened?..why are u crying?.."kuka tacigaba dayi kaman bazata yi mgn ba sai can daga baya tayi kokari ta tsayar da kukan nata snn tayi mishi bayanin duk abunda ya faru tun shigowarta asibitin zuwa yanxu...sauraronta yake saida ta gama tsaf snn yace mata"yanxu dai kiyi hakuri ki fara mikewa mu wuce kinga dare na karayi sosai...shi kuma proprietor kiyi mishi addu'a Allah zai saka maki kinji kou?.."gyada kanta tayi tareda mikewa a hankali suka nufi inda yayi parking...if u see how she is walking u will think irin tayi shekara da shekaru tana ciwon kafa...a haka suka isa inda motan yake ya bude mata ta shiga shima ya shiga suka fita daga asibitin...koda suka isa hostel saida ya kira Billy a waya wai tazo ta shiga da ita ciki aikuwa ta fito a rikice dan tana tunanin wani mugun abun ne ya faru da ita...mamaki ya kamata ganin yanda idon 'yar uwar tata yayi ja sosai face dinta duk yayi red sbd kukan dataci kafin ma ta tambaya Sa'eed ya labarta mata abunda Ayshan ta fada mashi ya faru...jikinta yayi sanyi kalau ita kanta tausayin Ayshan takeji...tasan haduwa irin wnn da proprietor ba abun alkhairi bane mutumin da ko idanu ka hada dashi sai kaji a jikinka inaga kuma ace ya tsareka da a gaba yana suburbuda maka masifa...ai dole ma Aysha ta jigata wlh..ko ba don zirga zirgan da tayi ba ko zama at the same roof da wnn mutumin kadai ya isa yasa mata zazza6i balle kuma ga wahalar da ita da yayi...Allah kadai yasan adadin sau nawa cikinta na kadawa sbd wmn matsiyacin kallon nashi...a hankali ta kamata suka shiga hostel din shi kuma Sa'eed ya juya kan motarshi ya wuce gida...suna shiga ciki ta hada mata warm water ta taimaka mata zuwa bathroom snn ta dawo ta shiga kitchen ta hado mata thick tea shima mai zafi ta jiye mata kan study table...ta dauko pcm da ruwa shima ta ajiye mata nan kusada tean sai kuma ta bude wardrobe dinta ta dauko mata jessy dinta as usual na Man Utd fara qal da wandonta duk ta jiye mata su kan gado...tana fitowa ta dauki kayan ta saka snn tasha tea da magani snn ta nannade kan gado tana sauke ajiyar zuciya...kawai imagining take yanda zatayi spending three whole weeks tareda wnn azzalumin mutumin da baida imani da tausayi ko kadan.
Washegari da wuri ta tashi duk da ba wani baccin kirki ta samu ba amma she woke up as early as possible sbd gudun sake yin wani laifin...a gurguje ta shiga bathroom tayi wanka snn tazo ta shirya suka fita tareda Billy ko breakfast ta kasa tsayawa tayi sbd tsoron kar tayi latti ya samu daman ci mata mutunchi.
8:17 suka shigo Hospital ko sallaman kirki bata tsaya sunyi da Billy ba ta wuce sbd tsoron abunda zai iya mata...saida ta tsaya ta gama jero addu'o'inta a bakin office dinshi snn ta tura kofan ta shiga a hankali da sallamanta ciki ciki...yana zaune kan office chair dinshi sanye da suit as always yana filling wani file dake kan table dinshi...ko kallon inda take baiyi ba balle har tasa ran zai amsa sallaman da tayi..itama hakan bai dameta ba ta karasa inda ta tsaya jiya ta tsaya kanta a kasa...wayanshi ne keta ringing yana ciki file din amma yayi banza dashi kaman bashi ake kira ba...saida ya gama snn yayi sliding tareda putting nata on speaker da igbo yace"Sab bakada hankali kou?..why kaketa jeramin missed calls haka?.."daga daya bangaren Sab ya amsa mishi cikin igbo shima saying yanason mgn dashi ne...Aysha dai na tsaye tana jin yanda suke mgn da igbo dagashi har wanda ya kirashi a wayan...dukda ba fahimtan language din takeba for sure tasan masifa yake sbd yanda yake daga murya...can kasa kasa tace"duk wani inyamuri dai ya iya masifa..kilan abun a jininsu yake"...tayi nisa cikin tunaninda take har batasan ya kammalan wayan da yake ya dawo sa hankalinshi gareta ba...yana kallon yanda dan bakinta ke motsawa as a result of zancen zuci da take kawai sai yaji gabanshi ya fadi...ya lumshe ido yana karanta innalillahi cikin ranshi...ya dauki tsahon lokaci idon nashi a rufe har saida yaji heartbeat dinshi ya daidaita snn ya bude..still kuma idanun kanta suka fada this time around sai ya kasa dauke idanun daga kanta...he just keep staring at her like mirror...har yanxun bakinta mosti yake and he wonder what she's saying da bakin ke motsawa haka...a hankali yayi sama da eyes dinshi zuwa forehead dinta da black thick hair kenan a kwance luf kaman na jaririya har zuwa sajenta da kuma dimples dinta da ko yaya cheeks dinta yayi motsi sai ya fito...sake lumshe eyes dinshi yayi yana dan murza goshinshi feeling somehow...baisan meya sameshi yau ya kasa dena kallonta ba and it's not as if she's beautiful kawai dai baisan dalili ba...wnn karon yana bude idon itama ta bude nata aikuwa idanunsu suka sarke cikin juna...Aysha da dauke nata da sauri sbd wnn abun dai da takeji duk ya zuba mata golden eyes dinshi a kanta...turo baki tayi murya can kasa tace"nidai Allah ya isana wlh..haka nan ya dinga zubama mutane idanun nan nashi sbd yasan ba'aso"...daure fuska yayi kafin yace"ke what are u saying?.."da sauri ta maida bakinta normal tareda kokarin daidaita face dinta kai a kasa tace"ba komai Sir...good morning"...bai amsa ba sai nuna forehead dinta da yayi yace"baki iya daura dankwali bane?..ko duk cikin rashin sanin darajar kai ne yasa kike yawo da gashi a waje?.."hannu takai ta dan janyo hijab din zuwa goshinta dukda ba rufe gashin yake ba dan kome zatasa sai ya fito shiyasa ma take barinshi..cikin ranta tace"na rasa a ina inyamurin nan yaji hausa wlh..he speaks like jakin kano"...kallon forehead din nata yayi yaga still gashin na nan waje kuma wai da sunan ta rufe kawai sai ya girgiza kai tareda sakin tsaki...mikewa yayi ya dauki phone dinshi snn ya kama hanyan fita yace mata"follow me"...ba musu tabishi a baya kaman body guard...eclmaptic ward taga ya nufa...ya jima suna mgn da wata nurse da doctors guda biyu kan wata patient da zasu shiga da ita theathre yanxu...after like ten minutes aka fito da matar zuwa theatre sauran doctors din suma duk suka shiga don shiryawa...shine karshen fitowa shima ya kama hanyan theatrn Aysha ta bishi a baya...daga bakin kofa ta tsaya ta dan daga murya yanda zai jiyota tace"Sir in koma knn?.."juyowa yayi yana kallonta da mamaki yace"go back where?..ba cewa nayi ki biyoni ba"...ta dan marairaice tace"to Sir naga zaku shiga theatre nefa"...ya daure fuska snn yace"C'mon come inside and get ready dake zamu shiga ai"...ta wani zarw idanu tana kallonshi hadda dora hannu a chest dinta tace"dani kuma?.."yace"ke don't waste my time here.. i said dake zamu shiga kiyi resuscitating baby and don't let me repeat myself"...hannu ta fara yarfewa zata kwaso magiya kawai ya zuba mata idanunshi yana yi mata irin kallon da yasan duk iskancinta bata isa ta