Showing 21001 words to 24000 words out of 157890 words

Chapter 8 - ZAUJATU JINNUL-ASHIQ

03 Nov 2025

135

fara warware kansa daga jikin Sulaima. Ganin haka ya sa mutanen wurin suka fara darewa, Kabiru ne ya dafa ƙofar a hankali ya zura ƙafarsa ɗaya cikin ɗakin.

Kallon-kallo aka fara yi tsakanin kumurcin macijin nan da Kabiru, a hankali Kabiru ya fara karanta duk wata addu'ar tsari da ta zo bakinsa. A zabure macijin ya fara ja da baya Kabiru na sake tunkararsa, wani kofi Kabiru ya hango da ruwa a jarka da sauri ya ɗauka ya zuba ruwa a kofi ya fara karanta ayoyin tsari yana tofawa. Daddy ban da leƙe babu abin da yake yi. Kasancewar Jabun Raihan ta san irin soyayyar da Mahaifin Raihan yake yi mata ya sa ta kwaɓe baki a lokacin da ta ga Kabiru ya tasamman halaka Macijin da ubangidanta ya turo, ta ƙwalla wata ƙara tana faɗin, "Daddy wuyana." Kabiru ya waiwayo yana kallonta, Daddy ya kai hannu kan wuyanta yana faɗin, "Mu je asibiti a duba ki, wallahi duk abin da ya samu ƴata ka kuka da kanka." Daddy ya ƙarasa maganar yana watsawa Kabiru mugun kallo. Raihan ta sake langwaɓewa ta ce, "Daddy don Allah a bar korar macijin nan kar wani ya ƙara mutuwa kawai ka kira fire service." Daddy ya kalli wurin da Kabiru yake ya ce, "Kai maza fito daga ɗakin nan kar kaima ka yi mana mushe." Intisar ta kalli jabun Raihan ta watsa mata harara, sannan ta mayar da kallonta wurin Daddy ta ce, "Daddy amma naga kamar macijin ya fara ja da baya mai zai hana a bari a ga ƙoƙarinsa..." Alhaji Mustafa ya katse ta da cewar, "Tabbas ni ma haka na gama ayyanawa don yaron nan kamar akwai wani taimako da zai yi mana." Kabiru bai bi ta kansu ba ya sake tunkarar wurin macijin, lokaci ɗaya ya watsa masa ruwan tofin hannunsa bakinsa na ci gaba da ambaton Allah. Nan take macijin ya faɗi gefe yana wani iri gurnani, zaburowa ya sake yi da niyyar kai wa Kabiru sara da sauri Kabiru ya watsa masa sauran ruwan da ke hannunsa. Wata dariyar farinciki Intisar ta saki don ko ba komai ta san an yi wa Mama Uwani illa, jikinsu Daddy ba ƙaramin sanyi ya yi ba da ganin gwagwarmayar da suka yi tsakanin Kabiru da macijin.

Jabun Raihan ta sake kallon Intisar ta saki ƙwafa a takaice, ta so ace Huzaifa ya bata umarni da tuni ta nunawa Intisar iyakarta. A wahalce Kabiru ya sa hannu ya hanyo macijin, ya fito daga ɗakin fuskarsa ɗauke da gumi lokaci ɗaya Daddy ya ji Kabiru ya birge shi saboda jarumtar da ya nuna, wannan ne karo na farko da ya ji ba zai iya ɗaukan mataki a kan wanda ya taɓa gudan jininsa ba, saboda yana matuƙar son mutum mai dakakkiyar zuciya. Sai dai har lokacin yana jin haushin Kabiru saboda abin da ya yi wa Raihan a idonsa.

Kusan tare suka tarkata suka fito daga sashen, kowa da abin da yake faɗa. Kabiru fita ya yi da macijin can bayan gidan Daddy ya kai ya wurgar da shi, Daddy da kansa ya sa aka rufe sashen Raihan tare da cewar sai ya kira ma'aikata sun yi wa ɗakin feshin magani, a ɓangare ɗaya yana tunanin barinsu daga gidan gabaɗaya.

*************

Raihan bata da zaɓi don haka ta gyaɗa masa kai tare da faɗin, "Duk abin da kika faɗa na amince don Allah ki mayar da ni." Huzaifa ya yi murmushi jindaɗi don shi kansa ya lura da yadda Raihan ta gama tsorata da shi. Lokaci ɗaya ya ji ta bashi tausayi, ya sa hannu ya zaro fiƙoƙin bakinsa waɗanda suka tsiro ya wara hannuwansa da niyyar Raihan ta rungume shi amma fir ta ƙi. Ya kalli fuskarta ya ce, "Kina ƙaunata." Raihan bata da zaɓi duk abin da ya faɗa sai dai ta amsa masa da amincewarsa. Tana tsaka da tunani ta ji ya ce, "Rufe idonki." Kallon hagu da dama ta fara yi a hankali ta furta, "Don Allah kar ki yi min komai." Huzaifa ya yi murmushi ya ce, "Kina rufe ido za ki ganki a gida." Tun bai rufe baki ba Raihan ta rufe idonta da ƙarfi, bata jima da rufewa ba ta ji tashin hayaniya na tashi sama-sama. Tana buɗe ido ta ganta zaune a falon Daddynsu, a hankali ta fara bin wurin da kallo, ta hango Intisar da sauran ƴanmatan da suke tare da su a ɗakinta. Suna haɗa ido da Intisar ta ji gabanta ya faɗi rass musamman da ta tuna irin gargaɗin da Mai siffar Mama Hasiya ta yi mata, a hankali ta miƙe ba tare da furta komai ba. Tana fita ta nufi sashen Mommy a kan step ɗin bene ta ci karo da Mama Uwani, tana ganinta ta washe baki ta ce, "Barka da hutawa uwar ɗakina." Sama-sama Raihan ta amsa, "Yauwa Mama Uwani ina Mommy take?" Mama Uwani ta nuna ɗakin mommy ta ce, "Tana ciki yanzu na kaiwa baƙi abinci ko na yi miki jagora." Raihan ta dakatar da ita da cewar, "A'a Mama Uwani ki je kawai." Mama Uwani ta yi murmushi tana faɗin, "Hutawarki lafiya uwar ɗakina." Raihan bata amsa ba ta wuce cikin ɗakin. Kafin Mama Uwani ta sauka daga kan bene Intisar ta doshi wurin, kallon-kallo suka fara yi wa junansu don ma mutane na zaune a falon, Mama Uwani ta saki wani malalacin murmushi ta wuce ba tare da ta tanka wa Intisar ba.

Intisar na shiga ta yiwa Mommy sallama don a cewarta za ta tafi gida, amma koda ta yi wa Raihan magana ko ƙurarta bata kalla ba balle ta tanka mata. Tun da ta ga haka ta sha jinin jikinta, don haka tana fita daga gidan ta ɓace daga ƙofar bata tsaya a ko'ina ba sai a tsibirin ƙungiyar asirinsu.

Raihan na zuwa jiki a sanyaye ta zauna, tana son sanarwa da mahaifiyarta cewar Mama Hasiya bata mutu ba amma tana tsoron abin da zai sake faruwa da ita. Tana nan zaune Daddy ya kira wayar Mommy ta waya yake sanar da ita, ɓacewar su Inno da Goggo sannan ta ce ta haɗa duk wani kayan sakawarsu don ya sa a ɗauke su daga gidan da suke zuwa gidansa da ke Unguwar sharaɗa. A cewarsa gidan cike yake da miyagun dabbobi, ba za su ci gaba da zama a ciki ba.

(Abin da bai sani ba duk in da zai je indai yana tare da Raihan tana tare da ZAUJATU JINNUL-ASHIQ😂 Idan kuma yana tare da Mama Uwani yana tare da JINNUL-ASHIQ😂 Mu je zuwa.😎)

Duk yadda Daddy ya so hukunta Kabiru ya ji zuciyarsa ta gagara ɗaukan mataki akansa, sai dai abu ɗaya ya riƙe duk abin da ya samu Raihan sai ya ɗauki mummunan mataki a kansa. A wunin ranar suka tare a sabon gidan Daddy da ke sharaɗa, da sauran ƴan gaisuwa suka tare. Ɗakin da ke jikin gate aka bawa Kabiru, yana shiga ɗakin ya ga akwai komai na buƙata sai dai lokaci guda ɗakin ya rikiɗe masa zuwa tafka-tafkan maciji masu fasalin irin wanda ya kashe a ɗakin Raihan. Yana shirin ja da baya ya ji wani ya faɗ masa a gadon baya lafin ya yi wani yunƙuri, ya fara nannaɗe masa jikinsa.


Intisar na zuwa ta kwashi gaisuwa wurin Hatsabibiya bungulu, bayan ta yi gaisuwa Hatsabibiya ta dubi Intisar ta ce, "Me yake tafe da ke da tsakar rana?"

Fuska ba walwala ta ce, "Hatsabibiya akwai tarin matsaloli domin Huzaifa ya saka ni a gaba, bayan Huzaifa akwai wani bafulatanin maigadinsu da alama zai kawo mana matsala. Amma wanda ya fi kawo mana matsala Huzaifa ne, don haka na ce ba zan yi ƙasa a gwiwa ba sai mun san abin yi don yanzu haka..."

Tun Intisar bata rufe baki ba Hatsabibiya Bungulu ta katseta da cewar, "Duk na ga abin da ya faru har ɗaukan Raihan da ya yi zuwa tsibirinsa." Intisar ta jinjina kai cikin huci tana cewa, "Da alama ya tsoratar da ita kuma a kowanne lokaci tana gabda bijirewa umarninmu."

"Sai mu kashe Huzaifa idan zai kawo mana matsala." Hatsabibiya ta faɗa kanta tsaye ba tare da ji shakku ko shayi ba." A firgice Intisar ta ɗago cikin tashin hankali ta zubawa Hatsabibiya ido, bakinta na rawa ta furta. "Kin manta wanene Huzaifa a wurina? Mijina ne fa." Hatsabibiya ta wara hannuwa cikin halin ko'inkula ta ce, "Ci gabanki ya fi zamantakewarki da shi don haka bana ganin zai amfane ki da komai." Intisar ta turɓune fuska ta ci gaba da cewa, "Ba zan lamince a kashe mijina kuma uban ƴaƴana ba, amma tabbas dole a nemi wata hanyar da za a samu mafita."


🤭 NA SAN DA YAWA ZA KU YI MAMAKIN JIN INTISAR MATAR HUZAIFA CE, KO KUN TUNO MUGAZA😂 ITA CE INTISAR. AMMA MAI YA SA HUZAIFA BAI GANE TA BA HAR SUKE TAKUN-SAƘA, SHIN WACCE RIBA MUGAZA ZA TA CI DA TA JEFA RAIHAN A ƘUNGIYAR ASIRI? IDAN SU MOMMY SUKA KOMA SHARAƊA SUN TSIRA KO DA SAURAN TAFIYA?

Share pls🌚

*ZAUJATU JINNUL-ASHIQ*


© *AMEERA ADAM*

Littafin kuɗi ne idan kina buƙata 300 ne ta Account 3090957579 Aisha Adam, First bank. Za ki turo evidence ta wannan lambar 0706 206 2624 Whatsapp only Idan kati ne 300 MTN.

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

FREE PAGE 7


Daddy yana tafe Raihan na riƙe a hannunsa har suka shiga cikin gidan ayyane-ayyane yake yi, yana mamakin wane irin macijine da nan take zai naɗe mutum ya kashe shi, kuma a ce ya fito daga ɗakin Raihan ɗin sa. Kwafa ya yi yana tunanin irin matakan tsaron da zai ƙara akan na da, har suka shiga ciki. Mommy jikinta ba ƙaramin sanyi ya yi ba don tun lokacin da abin ya faru ta fahimci macijin ɗakin Raihan ba ainihin dabba ba ne. Sai dai a wannan karon ta ci alwashin faɗawa Daddy gaskiya duk irin ɓacin ran da zai yi, don haka suna zuwa ta nemi ganawa da shi a sabon ɗakinsa dama gidan ya gina shi ne da sunan bayan wasu watanni su tare, amma kasancewar ba a gama masa ƙaƙale-ƙaƙale ba ya sa suka dakata da komawar, amma dole ta sa suka tashi a rana tsaka suka koma. A gaggauce Daddy ya dubi mommy ya ce, "Faɗi ina jin ki, kin san yanzu aka yi mini waya wai ankai su Inno da Goggo Hisba dole sai na zo, wani tashin hankali wai an tsinci su Inno a cikin masallacin Malam Isa na ƙarshen layi." Sai a lokacin Mommy ta zaro ido don bata san abin da yake faruwa ba, ganin ta shiga tashin hankali ya sa ya dube ta fuska ba walwala ya ce, "Ba fa wani abu ne na ɗaga hankali ba, komai ya zo da sauƙi yanzu dai ina zuwa." Yana gama maganar ko jiran cewarta bai yi ba ya fice daga ɗakin, jigum Mommy ta yi abu goma da ashirin ya haɗe mata.

Wani irin zafi Kabiru ya fara ji a jikinsa kamar wanda yake gaban wuta, hajijiya ya ji ta fara ɗaukansa ga wata irin matsa da macijin yake yi masa, tun yana daga tsaye har ya durƙushe a wurin yana son furta ayar Allah, amma macijin ya matse masa maƙogaronsa. Kakari ya fara yi kamar wanda ransa zai fita, a zuciyarsa yana son biya ko da ayatulkursiyyu ce amma wani abu mai nauyi ya ji ya tokare masa ƙirji kamar dutse. Yana cikin wannan halin ya ga ɗaya daga cikin macizan ya miƙe tsaye cak ya fasa kai, a hankali fatar jikin macijin ta fara saɓewa tana fita daga jikinsa sai kuma ya fara rikiɗa daga siffar maciji zuwa siffar bil'adam. A hankali wata matashiyar mace ta bayyana ilahirin jikinta gashi ne tun daga kanta har zuwa ƙugunta, ya yin da ƙugunta yake a nannaɗe cikin surar maciji. Harshe ta fara zaro masa nan take wani jaririn maciji ya faɗo, ta damƙe shi a hannunta ta kalli Kabiru da yake cikin mummunan hali ta fara magana, "Kai matashin bafulatani, wa yace maka takun saƙa da ni sauƙi gare shi? Ka san wa ka illata kuwa? Ka san wa ka kashe min kuwa? Ko kana tsammanin ka ci bulus ne?" Kabiru ya ɗago yana sauke numfashi da ƙyar idanunsa jawur ga gumi na ci gaba da tsiyaya daga jikinsa. Baki yake son buɗewa amma ya kasa, ganin haka ya sa ta sake bushewa da wata mahaukaciyar dariya sai da ta yi mai isarta sannan ta fashe da matsanancin kuka, ta jima tana yi sai ta tsagaita da kuka ta sake kallonsa ta ce, "Ba kai kana taƙama da addu'a ba ka yi ta mu gani, har za ka kashe min miji kana tunanin za ka zauna lafiya?" Macijiyar na gama maganar ta fara rarrafowa zuwa gaban Kabiru, ganin ta nufoshi gadan-gadan ya sa Kabiru ya ƙara yunƙura yana ja da baya, ya fara bude baki yana ƙoƙarin karanta addu'a haɗe da motsa baki sai dai ko kaɗan muryarsa bata fitowa, tana tunkararsa hushin numfashinsa ya doki gangar jikinta ba shiri ta ja da baya saboda wani irin zafi da ta ji yana fita daga bakinsa. Kallon-kallon suka fara yi a tsakaninsu, bata daddara ba ta sake yunƙurowa a kashi na biyu da niyyar hallakashi. Duk yadda Kabiru ya kai ga buɗe muryarsa ya yi addu'a abin ya gagara. Dabara ce ta faɗo masa ya fara biya ayatulkursiyyu a zuciyarsa, tana tunkaro shi ya fara tofa masa. Ganin tana niyyar hallaka ya sa ta sake yin baya, nan take macizan da ke gewaye da shi suka ɓace. Ƙaton da ya naɗe shi tuni jikinsa ya saki da ƙyar ya rarrafa ya bi ta jikin bangon ɗakin ya ɓace. Ɗakin Kabiru ya rage daga Macijiyar sai Kabiru, ya yin da ta sake kafe shi da ido tana ƙare masa kallo don ta fahimci makasar da za ta samu a jikinsa ta yi masa illa. A wahalce Kabiru ya faɗi can gefe yana mayar da numfashi, jikinsa gabaɗaya ya yi ja saboda irin tsananin matsar da macijin ya yi masa. A hankali jikinsa ya fara raɗaɗi, yana kai idanunsa kan fatarsa ya lura da yadda ta fara sauya launi zuwa fatar maciji. Macijiyar kallon Kabiru ta yi ta fara ƙyaƙyacewa da wata irin shu'umar dariyar ƙeta, hankalin Kabiru ba ƙaramin tashi ya yi da ganin abin da yake faruwa da fatar jikinsa ba. Yana tsaka da tunani ya riski muryar macijiyar tana faɗin, "Ka kashe min mijina ba tare da wani dalili ba, Huzaifa ya nemi tallafin mijina akan ya zo taimakonsa ka kashe shi, zafin mutuwarsa ta sa na ji tamkar na kashe ka amma ba zan kashe ka yanzu ba sai na gama wahalar da ruhina da gangar jikinka sannan na hallaka da hannuna. Ka je ko da wannan hallitar fatar macijin na barka ƙuncin rayuwar duniya ya ishe ka." Tana gama maganar ta sake naɗewa ta koma murtukekiyar macijiya, juyi ta fara yi daga wurin da take nan take ta baje a ƙasa ta fara nutsawa cikin ƙasa har ta ɓace ɓat. Ilahirin jikin Kabiru ban da rawa babu abin da yake yi, babban tashin hankalinsa yadda ya ga fatar jikinsa ta koma ta maciji illa iya fuskarsa, hannu da ƙafarsa ne kaɗai basu rikiɗa ba da yake macijin bai taɓa masa nan ba.



A fusace Hatsabibiya ta ɗago da ta sake kallon Intisar ta ce, "Idan ba mu kashe shi ba kina da hanyar da za mu ɓullo masa? Ko kuma kina da shawara akan yadda za mu kawar da tunaninsa akan Raihan?" Intisar ta yi shiru tana nazari don ita kanta ta san wanene Huzaifa da tsananin bincike irin nasa, ta san tun da ya kafa mata ƙahon zuƙa dole zai bi diddigin wacece ita da asalinta. Ta san muddin ya gano ta ba ƙaramar ƙura ce za ta tashi a tsakaninsu ba, a baƙar zuciya irin tashi yana iya hallakata. Don ma tana amfani da sirrin tsafi da sihiri ko a yanzu yadda ya ɗora ransa akan Raihan da tuni ya gama da ita. Tana cikin tunani ta sake riskar muryar Hataabibiya ta ci gaba da cewa, "Idan har baki da wata dabarar ga tawa shawarar." Intisar ta dubi Hatsabibiya tana sauke ajiyar zuciya ta ce, "Ina jin ki Uwargidana maganin kukana, da ke da Abar bauta ku kaɗai na dogara da ku duniya da lahira (Wa'iyazubillah) ke kika saba ɗauke min duk wata damuwata a yanzu ma ina biye da ke don jin mafitar da za ki kawo mana kafin abar bauta ta bayyana."

Hatsabibiya kanta ya sake girma, ta miƙe daga wurin da take ta ɗauki wani dogon ƙaho mai faɗi da tsawo ta kafa shi a bakinta sannan ta durƙushe a gurin. Ta kafa tsinin ƙahon a doron ƙasa sannan ta busa shi da ƙarfinta, lokaci ɗaya tsibirin ya ɗauka tsananin ƙararsa kamar zai tsaga dajin gida biyu. Tun bata rufe baki ba aljanu masu ɗauke da munanan hallitu suka fara fitowa wasu daga ƙarƙashin ƙasa wasu daga cikin duwatsu ya yin da wasu suka fara fitowa daga ɗakin tsafi. Kafin wani lokaci tuni sun taru suna masu sujjada a gabanta, tare da yi mata kirari kamar yadda suka saba sannan suka ƙame wuri ɗaya suna jiran umarninta.

Wani irin kuka haɗe da dariya ne ya fara tashi, lokaci ɗaya tsibirin ya fara girgiza suna nan tsaye wannan mummunar hallitar mai ɗauke da kawuna (Abar bauta.) Ta ziro kawunanta zuwa harabar wurin da take. Suna yin tozali da ita suka kwanta a wurin har hatsabibiya suna masu yi mata sujjada, haɗe da kirari. Kafin ƙiftawar ido Wani baƙin aljani ya dira a gabanta cikin girmamawa yana tambayarta.

"Ya ke uwargijiyata shin jariri kike buƙata, uwar jariri tsoho ko tsohuwa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login