Showing 3001 words to 6000 words out of 157890 words

Chapter 2 - ZAUJATU JINNUL-ASHIQ

03 Nov 2025

140

mai yake faruwa?" Inno na jin haka ta rushe da kuka tana faɗin, "Audullahi ka dubi irin sitirar da ka yi wa Zinaru ita da ƴarta amma da yake sun samu wuri wai cin naman ka suke da ƴarka ɗaya tilo a gidan duniya. Don Allah ko don darajar haihuwa Abulle ai da ɗagawa yarinyar nan ƙafa ina dalili tana uwarta tana cin namanta?" Goggo ta ƙanƙance ido cikin masifa ta ce:

"Audullahi wallahi tun wuri ka san halin da kake ciki, kwarankwatsa dubi Rehanu ta shiga ƙungiyar asiri."

Kamar wanda aka zagi iyayensa haka Alhaji ya ɓata fuska sai da ya haɗiyi yawu mai ɗaci ya ce, "Goggo kin san wa kike faɗa kuwa? Raihan ɗina ce ta shiga ƙungiyar asiri?"

"Ƙarya na yi maka kenan Audullahi?" Goggo ta tambaye shi tana ɗage kai gefe. Shiru ya yi don ya san idan ya buɗe baki a kan Raihan za a iya samun matsala shi kuma yana ganin girman Mahaifiyar matarsa, ba zai so wani abu ya haɗa su ta sanadiyyar Raihan ba. Ganin haka ya sa Mommy ta riƙo hannun Goggo tana cewa, "Goggo ta so mu je ɗaki don Allah." Inno na ganin haka ta fashe da kuka tana faɗin:

"Allah ya fini sanin dalilin da ya sa bai bani ƴa mace ba, amma ya yi mini komai da ya bani Audullahi da ban haihu ba sai na rasa mai kaini ɗaki nima." Tana gama maganar ta kalli Alhaji ta ci gaba da cewa, "Audullahi nima ka kaini ɗaki ba sai an goranta min ba, kuma wallahi aure za ka ƙara don ba za ka zauna da macen da bata ganin mutumcina ba."

Daddy na shirin yin magana suka ji Raihan ta turo ƙofa ta fito fuskarta murtuk babu fara'a, da sauri Goggo ta fara ja baya tana leƙenta. Daddy na ganinta ya saki murmushi ya rungumota yana faɗin, "Barka da fitowa habibtyn daddy." ƙarasowa wurin ta yi ta ce, "Daddy ba dai fita za ka yi ba?" riƙo hannunta ya yi ya ce, "Yanzu ma kuwa don na gama komai."

Fisge hannunta ta yi ta koma kan kujera tana faɗin, "Na faɗa maka gaskiya za ka yarda?" Murmushi ya yi ya ƙarasa wurinta ya ce, "Faɗi babyna."

"Ka haƙura da fita da baƙar mota idan ba haka ba za a samu matsala."

Mommy ta kalle ta tana faɗin, "Raihan me ya sa bakinki baya furta alheri ne? Ke kin san gaibu ne da za ki yanke masa wannan hukuncin." Goggo da ke gefe tana son yin magana tsoro ya hanata. Daddy ya gyara zaman agogonsa yana faɗin, "Baby sai abin da kika ce da wacce kike son da ita." Daga wurin da take ta ce, "Kowacce ka yi niyyar fita da ita amma ban da baƙar." Daga haka sallama ya yi musu Mommy ta wuce raka shi, Raihan na ganin haka ta ƙarasa gaban Goggo ta tsugunna a wurinta tana faɗin, "Wallahi na kuma jin kin danganta ni da ƙungiyar asiri Allah za ki yi mamakina, sai na kaiki Daulatul Jinnul nariy na azabtar da ke." Inno da ke gefe ta karɓe zancen da faɗin, "Wallahi kema kya gaya mata ai ni wallahi ban yafe wannan ƙazafin da ta yi miki ba. Ni dai wannan larabcin da kika yi ne ban san me kika faɗa ba, amma idan za ki tafi da ita don Allah ki kaini na ga yadda Zinaru za ta yabawa aya zaƙinta." Raihan bata bi ta kansu ba ta wuce kan dianning table, saboda yadda yunwa take sasaƙar cikinta don abincin da ta ci babu in da yaje mata. Tana zama ta fara buɗe kulolin da ke wurin nan take ta fara tasa kulolin a gaba, ɗaya bayan ɗaya tana cinyewa, kuloli huɗu ne a wurin amma da zaman ta ko minti biyar bata yi ba ta cinye abincin ciki gabaɗaya, tare da shanye shayin da ke cikin fulas ɗin ta kora da ruwa sannan ta dawo falo ta zauna. Lokacin da ta dawo tuni su Inno sun wuce sashensu don haka basu lura da abin da Jabun Raihan ta aiwatar ba.

Sanyin da yake busawa a wurin ne ya doki gangar jikinta wanda ya sa ta buɗe idanunta a hankali tana ƙarewa wurin kallo, cikin rashin ƙwarin jiki ta miƙe zaune har lokacin kallon wurin take yi da tsananin mamaki. A hankali wannan jaririyar hallitar ta fara matsowa har sai da ta hau cinyar Raihan, zamanta a cinyarta ya sa ta lura da wurin a zabure ta miƙe tana ƙwalla ƙara haɗe da ja da baya zafin buguwar ya sa hallitar yin can gefe wanda yake nuni da jin zafin da ta yi. Waige-waige ta fara yi tana ambatar sunan mahaifiyarta, kamar daga sama ta riski muryar Mommynta tana faɗin, "Ga ni nan zuwa Raihan."

Tafiya ta fara yi daga wurin da ta fara jin sautin muryar, ta wani lungu ta hango Mommynta ta fito cikin doguwar rigar shadda tana sakar mata murmushi, kallo ɗaya ta yi mata ta ji gabanta ya yu mummunan faɗuwa. Dafa Raihan ta yi tana faɗin, "Kin tashi Raihan?"

Kuka Raihan ta fashe da shi tana faɗin, "Mommy ina ne nan menene wancan abin?" Ta ƙarasa maganar tana nuna wurin da wannan hallitar take rarrafowa a hankali, Mommy ta kalli wurin tana murmushi ta ce, "Taho mu je ki rabu da wancen abin." Har sun fara tafiya Mommy ta kalli Raihan ta ce, "Amma duk wanda zai ce miki ki bishi kar kije wurinsa cutar da ke zai yi ni ce mahaifiyarki babu abin da zan yi miki." Har lokacin Raihan a tsorace take don haka ta kalli yanayin wurin ta ce, "Amma mommy ya aka yi muka zo nan?" A ɗan tsawace ta ce mata:

"Za ki taho ko tambaya ta za ki tsaya yi." Ba musu Raihan ta bi bayan wacce take gani da siffar Mommynta, har sun kusa fita sai gani ta yi Daddynta ya diro da ƙarfin gaske yana faɗin, "Raihan." Da sauri ta waiga wurinsa tana shirin yin magana mai ɗauke da siffar Mommynta ta fara fisgar hannunta tana faɗin, "Karki saurare shi wuce mu je." Da sauri ya ƙaraso wurin rai a ɓace ya fisgi hannun Raihan sannan ya dubi Mai ɗauke da siffar Mommy yana faɗin, "Mugaza ki shiga taitayinki fa, na gaya miki ki fita harkar yarinyar nan ba na son na hukuntaki a kanta amma wallahi idan kika illatata sai na baki mamaki." Lokaci ɗaya ta rikiɗa zuwa wata mummunar hallita mai ɗauke da siffar ƙadangare sai dai kawunanta goma kowanne ɗauke yake da wasu irin manyan harsuna masu kama da kaifin takobi. Da gudu Raihan ta rungume mai ɗauke da siffar mahaifinta tana wani irin kuka tare da faɗin, "Daddy tsoro nake ji." Ilahirin jikinta ban da rawa babu abin da yake yi, rumgume ta ya yi tsam a jikinsa yana shafa bayanta cikin wata irin soyayyarta da take fisgarsa, don karta fahimci wani abu ya sa ya iya riƙe kansa ba tare da kusanceta ba. Wannan abin ba ƙaramin ɓata ran Mugaza ya yi ba, a shammace ta kaiwa Raihan cafka da ɗaya daga cikin harshenta a ƙafa, da sauri Huzaifa ya janyeta amma sai da harshen nata ya samu ƙafarta. Wata uwar ƙara ta ƙwalla sannan ta faɗa jikin Huzaifa wanda yake nuna suma ta yi.

Wata irin mahaukaciyar dariya Mugaza ta fara ƙyaƙyatawa lokaci ɗaya ta murtuke fuska tana faɗin, "Ki je ki da wannan damuwar zan baki rata kafin na sake waiwayo ki." Tana gama maganar ta ɓace daga wurin.

Cike da tausayi Huzaifa da ke ɗauke siffar Daddy ya shimfiɗar da Raihan, a daidai wannan lokacin jaririn hallitar nan ya ƙaraso wurin ya kwantar da kansa a jikinta. Hannu biyu Huzaifa ya sa ya ɗago jaririn idanunsa ɗauke da ƙwallah ya ce, "Mahaifiyarka na fuskantar ƙalubalen rayuwa, amma daga yanzu zan tsaya mata tsayin daka don kare martaba da ƙimarta." Yana gama maganar ya sake ɗora mata shi a kanta yana motsa baki, lokaci ɗaya jaririn hallitar ya ɓace.

Yana ganin ɓacewarsa ya kalli Raihan da ke kwance ya ce, "Daga yau za ka kasance tare da Mahaifiyarka ko baby komai za ka riƙa ankarar da ni kamar yadda ka ankarar da ni kafin Mugaza ta cimma ƙuduri a kanta."

Share hilis🌚

Ummou Aslam Bint Adam🌚

*ZAUJATU JINNUL-ASHIQ*


© *AMEERA ADAM*

Littafin kuɗi ne idan kina buƙata 300 ne ta Account 3090957579 Aisha Adam, First bank. Za ki turo evidence ta wannan lambar 0706 206 2624 Whatsapp only Idan kati ne 300 MTN.

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

FREE PAGE 3

Mommy na shigowa ta nufi wurin dianning sai da ta zauna sannan ta kalli wurin da Raihan take zaune ta ce, "Mama Uwani ta ce min kin yi breakfast ko?" Jabun Raihan da ke zaune a kan kujera ta ce, "Eh na yi ɗazu." Mommy na juyawa ta buɗe kular abinci sai ta ga wayam, sake buɗe ɗayar kular ita ma babu komai; haka ta riƙa buɗe kulolin abincin amma sai taunannun ƙashi a ɗan tsorace ta tashi tana faɗin, "Waye ya cinye abincin nan Mama Uwani?" Cikin rashin damuwa Raihan ta ce, "Yanzu na cinye su." A ɗan tsorace mommy ta ce, "Gabaɗaya abincin ke kika cinye har fa da abincin rana na ajiye mana." Raihan ta miƙe ta nufi ɗakinta tana faɗin, "Wanda Mama Uwani ta kaimin bai ishe ni ba shi ya sa." Mommy sororo ta yi jikinta a sanyaye tana bin bayan Raihan da kallo.

Jabun Raihan na shiga ɗaki ta ji Huzaifa na ƙwala mata kira, ta kusurwar bango ta wuce cike da ɗoki don zamanta a cikin gidan jin ta take kamar a kabari take.

Huzaifa da ke tsaye a gaban Raihan ya dubi Jabun Raihan ya ce, "Mugaza ta yi mata rauni zan mayar da ita ga mahaifanta amma zan ci gaba da bata kulawa kamar yadda na kwashe dubban shekaru ina tsaye a kanta. Ki je na sallame ki idan da yuwar wani lokacin na buƙace ki za ki ji ni." Cike da farinciki jabun Raihan ta rikiɗe zuwa siffar wani ƙaton tsuntsu mai ɗauke da manyan fuka-fukai ta ɓace daga wurin, daga wurin da yake ya ɗauki Raihan ya ɗora ta akan gadonta sannan ya ɓace daga wurin.

Bayan shigar jabun Raihan ɗaki ta fara kiran Mama Uwani, cike da girmamawa ta ƙaraso wurin tana faɗin, "Ga ni hajiya."

Mommy ta kalli kulolin kan dianning ta ce, "Mama Uwani yau mun wayi gari da wani abin almara, dubi kulolin nan wai Raihan ta cinye." Da mamaki Mama Uwani ta zaro idanu ta ce, "Hajiya duka ita Uwarɗakin nawa ce ta cinye?" Mommy ta taɓe baki ta ce, "Dama ke ba ta laifi a wurinki ai, yanzu a sake dafa wani abincin bari na haɗa cornflakes." Mama Uwani ta fara tattara kwanukan tana faɗin, "Hajiy ai kowanne laifi kika ɗauko cewa kike ita ce, ni kuma uwarɗakina bata laifi." Tana gama maganar ta kwashe kwanukan ta wuce kitchen da su.

Raihan ba ita ta farka sai bayan azahar, a hankali ta buɗe idonta da suka yi mata nauyi dum! Tana ƙarewa ɗakin nata kallo. Lumshe idonta ta yi saboda yadda ta ji kanta yana sara mata kamar zai tarwatse, yunƙurawa ta yi zata tashi zaune ta ji jikinta ya yi mata wani irin tsami, ƙafarta ta hagu ta ji ta yi mata sanyi kamar ba a jikinta take ba. Da ƙyar ta samu ta fara dafa bango tana jan ƙafar tata da take jin ta yi mata nauyi kamar gungumen icce, tana zuwa falo ta fara yamutsa fuska tana bin ko'ina da kallo, a gefe ɗaya kuma ta fara wani shinshine-shinshine a haukace kamar mahaukaciya sabon kamu, da rarrafe ta fara watsi da kayan fallon cikin wani irin yanayi tana wani irin ƙaraji da gurnani kamar zakanyar da take tsaka da farauta. Ƙarar fashewar kayan ne ya fito da Mommy daga ɗaki a tsorace tana bin wurin da kallo, tana shirin yin magana su Goggo suma suka turo ƙofa suka fito don ganin abin da yake faruwa. Gilas ɗin center table da ta fasa ta fara ɗauka tana wurga musu tana faɗin, "Waye ya ɗauke min ɗana, ɗana ne wallahi duk wanda ya taɓa min shi sai na kashe shi." Inno da Goggo na ganin haka da rarrafe suka juya cikin ɗaki a tsorace, suna shiga suka bankawa ƙofarsu sakata jiki na rawa.

Mommy jiki na karkarwa ta ce, "Raihan lafiyarki kuwa?" Raihan ta sake wurgawa Mommy wata kwalba da sauri ta sa hannu ta kare, kwalbar ta yanketa a hannu jini ya fara zuba, jin ƙarnin jinin mommy ya sa ta fara wurga mata wani mugun kallo tana lasar baki. Ta ci gaba da surutai ba fasali, Mama uwani ta shigo a tsorace tana kallon abin da yake faruwa.

Hanyar kitchen ta nufa tana zuwa a haukace ta fisgo wata ƙatuwar roba wacce take ciki da ɗanyan kifi, tana zuwa falo ta rungumeta da hannuwa biyu tana sauke ajiyar zuciya.


Mommy na shiga ɗaki hankali a tashe ta ɗau waya ta fara kiran Daddy, ba a jima ba ya ɗauka ko jiran cewarsa bata yi ba ta fara faɗin, "Alhaji muna cikin tashin hankali, da alama ciwon Raihan na shekarun baya ne ya dawo sabo don Allah ka yi maza ka zo." Amsa mata ya yi sannan suka yi sallama ya katse wayar a gaggauce, Mommy na daga wurin da take a ɗaki tana jiyo ƙarara fashe-fashen kayan da Raihan take yi. Bayan wani lokaci shiru ne ya biyo baya, jin shirin ya sa Mommy ta miƙe a hankali ta buɗe ƙofar ɗakin. A falo ta hango Raihan zaune rungume da ɗanyun kifi, gabaɗaya ta ɓata jikinta da falon da ruwan kifi ban da ƙarninsa babu abin da yake tashi. Daddy ne ya turo ƙofa ya shigo yana gaba Dr Hamza na biye da shi, sai dai ganin yanayin falon ya sa ya fahimci wannan ciwon nata har ya ninka na baya. Jin sallamar Daddy ya sa ta ɗago da jajayen idanunta tana yi masa wani irin kallo, a haukace ta zaburo kansu tana faɗin, "Kar wanda ya taɓa mini ɗana jinina ne ba zan laminta a raba ni da shi ba." Tana rufe baki ta wurgowa Daddy wata kwalba saura kaɗan ta same shi a fuska ya kauce, Daddy ne ya fara kiran Yunusa mai gadi yana zuwa suka shiga kiciniyar riƙe Raihan sai da ƙyar suka samu nasarar riƙeta Likita ya yi mata allurar bacci, a take bacci ya ɗauketa ta faɗi gefe.

Kan kujera suka ɗorata Likitan ya fita yana yi wa Daddy bayani.

"Wato Alhaji da alama ciwon yarinyar nan ya dawo sabo, domin idan har abin da mahaifiyarta ta faɗa ne za mu iya cewa ya ninku a kan na da, saboda a da tana surutai kawai idan abin ya tashi, amma a wannan karon tana nuna kifi a matsayin ɗan cikinta. Akwai issue mai girma a game da lamarin ciwonta, za mu yi bincike mai zurfi a kai, sannan kar a riƙa wasa da magungunanta ta riƙa sha akai-akai." Jikin Daddy a sanyaye ya miƙawa Dr Hamza hannu yana faɗin, "Na gode sosai Dr don Allah a yi wani abu kai, ka san ina matuƙar son Raihan ba zan iya jure rashinta." Dr Hamza ya jinjina kai ya ce, "Insha Allah Alhaji kuma a ci gaba da addu'a everything will be successfully." Daga haka suka yi sallama da Likita. Yana komawa ciki tuni ma'aikatan gidan suka shiga hada-hadar gyaran falon, kusa da ita ya je ya zauna ya zura mata ido, hannu ya ɗora a kan goshinta zuciyarsa babu daɗi ya ce, "Wish you quick recovery dear, me ya sa al'amuranki basa zuwa da sauƙi why? Allah ya baki lafiya my baby." Mommy na ƙarasowa wurin ta dubi Alhaji cikin damuwa ta ce, "Habibi ni kam wata shawara gare ni." Bai furta mata komai ba ya ɗago yana kallonta ya yi mata alamar yana sauraronta. Jingina ta yi da bango ta ce, "Gani nake yi mai zai hana ciwon yarinyar nan a haɗa shi da na islamic chemist ko akwai shafar aljanu a ciki..." Tun bata dire zancenta ya buga mata tsawa da cewar, "Ba na son na ƙara jin kin danganta min Raihan da wani jinsin bayan bil'adam, idan ba haka ba ranki zai yi mummunan ɓaci. Me ye wani islamic chemist malaman da kaje wurinsu sai dai su fara yi maka turare da hayaƙi, da sun samu wuri za su fara yi maka maula. Idan ba za ki taya ni mu nema mata magani ba don Allah ki cire hannunki daga cikin maganar, ni kaɗai na isa na nema mata lafiya." Ran mommy ba ƙaramin ɓaci ya yi ba, amma babu yadda ta iya haka ta ja bakinta ta tsuke don ta san akan wannan maganar sai su haura sama su faɗo. Daddy ne ya cicciɓi Raihan zai kaita ɗaki da sauri Mommy ta nuna masa ɗakinta tana faɗin, "Ka kaita Toilet ɗina zan gyara mata jikinta a can sai ta kwanta." Bai tanka mata ba ya wuce ya kaita ɗakin Mommy don har lokacin fushi yake yi.

Mommy da kanta ta gyara Raihan ta kwantar da ita a kan gadonta, zama ta yi a gefe tana kallon ƴartata cike da tausayawa. Idanunta ne suka ciko da ƙwalla, ta sharce ƙwallah ta furta, "Wannan ita ce kalar tamu ƙaddarar, Allah ya baki lafiya Raihan."

Raihan ta jima tana bacci sai bayan wani lokaci sannan ta tashi, ɗingisawa ta ci gaba da yi har ta fito zuwa falo. A lokacin an gyara falon sai ƙamshin turare yake. A zaune ta hango Mommy Mama Uwani na zaune a ƙasa tana matsawa Mommy ƙafa, cike da farinciki Mama Uwani ta ce, "Uwar ɗakina kin tashi?" Kafin Raihan ta yi magana Mommy ta furta, "Barka da tashi My Princess." A ɗingishe ta ƙaraso wurin cikin damuwa mommy ta ce, "Me ya samu ƙafar taki?" Raihan ta yamutsa fuska ta ce, "Wallahi haka kawai na ta yi min nauyi. Mommy kamar mun je wani wurin ko? Ko dai mafarki na yi ne?" Mommy a tunaninta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login