Showing 66001 words to 69000 words out of 157890 words

Chapter 23 - ZAUJATU JINNUL-ASHIQ

03 Nov 2025

169

Allah kina ƙarasa warware wa za mu koma gida." Jinjina kai ta yi sannan ta ce, "Ina Daddy fa?" Mommy ta yi murmushi ta ce, "Oh Raihan wannan rai naki yana son Daddy ƙila da ni ce ba za ki tambayi inda nake ba ko?" Raihan ta tura baki gaba ta ce, "Kai Mommy wallahi a'a."

Abinci aka kawowa Raihan ta ci tana cikin ci Daddy ya shigo, ba ƙaramin daɗi ya ji ba ganin ta samu lafiya. Ya jima a zaune sannan ya tafi office ɗin Malam don ya ce yana son ganinsa. Da sallama Daddy ya shiga bayan sun gaisa Malam ya fara yi wa Daddy bayani, "Alhamdulillah mun samu nasara ya fita daga jikinta, amma za ta ci gaba da zama a nan tana karɓar magani na tsawon sati guda. Sai dai ya zama dole a kiyaye wasu abubuwa kuma koda komawa gida kuka yi dole ne a riƙa kunna karatun alƙur'ani akai-akai, a hanata jin kiɗe-kiɗe da yawaita bayyana tsiraci. Ta riƙa zama da alwala kuma so samu a farko-farkon nan kar a riƙa bari tana kwana ita kaɗai a ɗaki don shi shaiɗani binbini gare shi fiye da yadda kake tsammani. Sauran bayanin zan yi muku ranar da za a sallame ta, don a kiyaye Allah ya bata lafiya." Daddy cikin jin daɗi ya ce, "Amin Malam mun gode ƙwarai Allah ya ƙara ilimi."


Littafin kuɗi ne idan kina buƙata 300 ki min mgn 0706 206 2624

24


A wannan lokacin ganin halin da Huzaifa yake ciki ba ƙaramin ɗaga mata hankali ya yi ba, da farko ta so share shi saboda kishin Raihan da yake cinta a zuciya amma da ta tuna mijinta ne kuma uban ƴaƴanta akan dole ta yakice komai ta ƙarasa wurinsa da yake kwance kamar gawa. A hankali ta ɗago shi ba shiri ya saki ƙara sakamakon wani irin raɗaɗi da yake ratsa cikin jikinsa, ganin halin da yake ciki ya karya zuciyarta lokaci ɗaya ta rungumo shi a jikinta ta fashe da matsanancin kuka. Sai da ta yi mai isarta ta ɗago shi cikin kuka tana faɗin, "Ina amfanin irin wannan rayuwar Huzaifa, me ya sa ba za ka tsaya a iya matsayinka ba? Dubi irin azabtarwar da aka yi maka duk akan yarinyar nan meye take da shi wanda ba ni da shi. Haka kawai za su kashe min kai su illata ka su cuci ƴaƴana, gaskiya ya kamata ka sauya rayuwa Huzaifa wannan ba hanyar ce mai ɓulle wa ba." Huzaifa bai tanka wa Mugaza ba kasancewar yana cikin wani yanayi mai wuyar fasaltuwa, taimaka masa ta yi ta gyara masa jikinsa sannan ta shiga jinyarsa.

Abar bauta hankalinta ya kai matuƙar tashi don ganin irin illar da aka yi musu lokaci ɗaya kuma aka fatattaki wanda suke ganin shi ne bango madafarsu. Taron gaggawa ta sake haɗa musu don sanin makamar abin da za su gudanar dangane da Raihan. Ilahirin ƴan tawagar ƙungiyar asirin sun hallara a wurin Intisar ce kawai bata samu halarta ba sakamakon jinyar Huzaifa da take yi, wannan uzurin da ta kawo bai sa ta samu wata matsala ba saboda abar bauta ta san abin da yake faruwa. Sai da ta ƙare musu kallo sannan ta fara magana, "Ya zame mana wajibi mu tashi tsaye don mu yi yaƙi da hannuwanmu, tabbas an cutar da mu kuma ba za mu bari wannan cutarwar ta tashi a banza ba. Malam Usman ya fatattaki Huzaifa idan muka zura kanmu a yanzu muma za a iya fatattakarmu, me kuke ganin shi ne mafita a gare mu?" Abar bauta ta wurga musu tambaya, aljani batoyi ya miƙe tsaye ya ce, "Ni a ganina mu afka musu lokaci ɗaya don sarkin yawa ya fi sarkin ƙarfi." Abar bauta ta jinjina kai ta kalli sauran haka suka riƙa tashi suna faɗar ra'ayinsu sai daga ƙarshe Hatsabibiya ta miƙe ta ce, "A ganina mu sararawa Raihan na tsawon lokaci matuƙar ba ma son kwaɓarmu ta yi ruwa, jinkirtawar da za mu yi ba shi zai nuna gazawarmu ba sai dai don mu samu damar da za mu farfaɗo da ƙungiya idan muka ce gaggawa za mu yi tabbas za mu iya tsintar talatarmu a laraba. Mu ci gaba da gina ƙungiya idan ya so daga baya sai mu yi zaman shawarar da za mu sake jawo Raihan cikinmu, kin ga kafin lokacin ƙarfinmu ya dawo muna da jajircewar da za mu iya tunkarar Raihan ba tare da wata matsala ba." Abar bauta na gama jin haka ta fara ɓaɓɓaka dariya saboda shawarar ba ƙaramin daɗi ta yi mata ba, don haka a lokacin ta bada umarnin a fito don a samo mata jarirai biyar sababun haihuwa, sai jinin tsofaffai uku da na matasan samari biyu. Kafin wani lokacin tuni an aiwatar da abin da ta buƙata, nan take suka farke musu kayan ciki suka sha jini suka ci gaba da harkokinsu da tunanin yadda za su gyara ƙungiya su sake ƙafata ta tsaya akan ƙafarta.

Jikin Raihan na ci gaba da samun sauƙi saboda yadda take samun kulawa daga cibiyar Waraka islamic chemist, tana cin abinci sosai babu wani abin da yake damunta. Akwai magugungunan da ake bata safe da yamma da turarrikan da ake yi mata haɗe da wasu mayuka da ake shafa mata masu haɗe da magani a jiki. Ita kanta Raihan sai da ta ji daɗin jikinta sakamakon jinta wasai da take yi, duk wasu miyagun mafarkai ta daina yi. Ta daina mafarkin an biyota da gudu ko wani namiji yana saduwa da ita, hatta ɓacin rai da take yawan jin haka kawai ranta na ɓaci ta daina. Wannan sauyi da ta samu ba ƙaramin faranta zuciyar su Mommy ya yi ba, Daddy ne kaɗai yake komawa gida ya kwana shi ma a ranar farko da ya koma tsoro ne ya fara kama shi, sai da ya ɗauko laptop ɗin Mommy ya kunna karatun Alƙur'ani sannan ya samu bacci mai daɗi ya ɗauke shi. Haka ya ci gaba da zarya daga gida zuwa wurinsu Raihan duk wasu harkokinsa ya dakatar da su, don ko fita ya yi hankalinsa na wurinsu. Su Inno da suke garin Albasu ta waya suke kiran mommy ko ta kira su, don su ji sauƙin jikinta. Yadda suka ji jikinta ya yi sauƙi ba ƙaramin daɗi ya yi musu ba. Satin Raihan guda Malam Usman ya basu sallama, a ranar da za su tafi Malam ya jima yana yi musu nasiha da cewar:

"Masha Allah, dama an ce komai ya yi farko zai yi ƙarshe amma don Allah ina so ku bani aron kunnuwanku. Duk abin nan da ya faru da Yarinyar nan dama can rubutacce ne a wurin Ubangiji, amma kun san komai yana da sanadi." Lokaci ɗaya Daddy da Mommy suka gyaɗa kai sannan Malam Usman ya ci gana da cewa, "Kun yi sakaci matuƙa dangane da tarbiyar yarinyar nan musamman kai Mahaifinta, a mafi yawan maganar da Aljanin ya yi duka idan ka tattara maganganunsa yana nuna cewar kai Mahaifinta kai ne ka fi bashi goyon baya wurun samun zama a jikinta, ya nuna gazawar addu'a ƙarara don haka yanzu dole ku zage dantse. Duk Ɗan da ka gani yana da iyaye kuma duk iyayen da ka gani suna ƙaunar ƴaƴansu, amma muddin muka bari soyayyarsu ta rufe mana ido dole watarana kwaɓarmu za ta yi ruwa, kuma dama an ce ka so naka duniya ta ƙi shi ka ƙi naka duniya ta so shi. Idan har muna son ƴaƴanmu su taso da tarbiyyar koyarwar gidan Manzo dole mu tsaya kai da fata akan tarbiyya irin wacce addini ya bamu, daga ƙarshe ina mai ƙara jaddada muku da sa ido sosai akan yarinyar nan don kar wannan la'anannan ya sake bijirowa a jikinsa. Ina roƙon Allah ya bata lafiya ya tsare dukkan ƴaƴan musulmi kuma ya fito mata da miji nagari." Mommy da Daddy cikin haɗin baki suka amsa da Amin, suna sake yi masa godiya sannan suka yi sallama suka tafi.

Ana sauran kwana biyu za a sallami Raihan Daddy da kansa ya kira malamai suka yi saukar alƙur'an, a ranar da suka koma haka aka turare gidan da Habbatussauda Mommy ta kai kayan Raihan ɗakinta don ta gama tsara Raihan a wurinta za ta koma da kwana. Kwanan su Mommy biyu da dawowa aka ɗebo su Inno aka dawo da su, da ido suka riƙa bin Raihan da kallo. Har sai da Raihan ta tsargu ta ce, "Inno Lafiya wannan kallon fa." Inno ta yi tsumu kamar kazar da aka tsamo daga ruwa ra ce, "Haba Raihanu me kika gani?" Raihan ta taɓe baki ta ce, "Wallahi duk na ga kwana biyu kun zama wasu salihan bayi tsofaffin nan an ya ba wani abin kuke ƙullawa ba?" Mommy da ta kawo kai cikin ɗakin ta watsa wa Raihan daƙuwa ta ce, "Gidanku Raihan Iyayen nawa ne za su ƙulla miki wani abin?" Raihan ta yi dariya mai sauti tana nuna Goggo da ta rufe ido a zuwan bacci take yi, amma kana kallon yadda take motsa ƙwayar idonta za ka fahimci ba bacci take ba. Raihan ta ce, "Allah da gaske ki ga fa yadda Goggo take mintsina idanu kai da gani kasan baccin ƙarya take." Mommy ta kai mata dukan wasa ta ce, "Raihan wai yaushe kika raina su Goggo haka?" Goggo ta ɗago da kai ta ce, "Duk wanda ya raina uwar wani ta shi ya raina." Daddy ya shigo ɗakin ya zauna suka ci gaba da hira, ita dai Inno sai ɗari-ɗari take yi tana tsoron abin da kaje ya zo.

Haka rayuwa ta ci gaba da tafiya a gidansu Raihan gwanin birgewa don a wannan lokacin sam ba su da wata damuwa, duk wasu hanyoyi da suke katange ɗan adam daga kaidin aljan su Mommy suna ƙoƙarin ganin sun bi. Hatta al'amuran yau da gobe Mommy ta fara nusar da Rainan, har aikin gida da girki babu wanda bata nuna mata saɓanin lokacin baya da sai dai a girka a bata ta ci. Daddy yana ganin duk abin da yake faruwa sai dai uffan bai ce ba don nasihar Malam Usman ba ƙaramin ratsa shi ta yi ba, kuma lokaci bayan lokaci suna ci gaba da karɓo mata magunguna da turarika. Babban abin da ya tsayewa Raihan a rai tun da ta kwanta jinya ko a waya Intisar bata kira ta ba balle ta je duba ta, bata kawo ƴan Department ɗin su za su je ba saboda da dama wasu ba mu'amala suke da ita ba. Mazan ajinsu uku ne suka taɓa zuwa gidansu Raihan, Kabiru ya kwatanta musu Waraka Islamic Chemist, lokacin da suka je duba Raihan Daddy da Mommy ba ƙaramin daɗi suka ji ba. Raihan na zaune ta dubi Mommy ta ce, "Ni kam na yi tsammanin ko kowa zai guje ni Intisar ba za ta guje ni ba, tun fa a Asibiti rabona da ita ko da muka dawo gida bata zo ba, babu waya ko text message yau fa sama da wata biyu da yin ciwona." Mommy ta dafa kafaɗarta ta ce, "Ki yi mata uzuri mana Raihan kin san ɗan adam jiki da jini kika san abin da ya hanata zuwa? Me ya sa baki kirata kin ji uzurinta ba? Ni fa ina ga haka kawai ba za ta ƙi zuwa dubiyarki ba kema kin sani." Cike da gamsuwa Raihan ta ce, "Haka ne Mommy amma duka layikanta a kashe idan na kira, kuma kin san tun kwanaki iyayenta suka koma Kaduna a hostel take da zama kin ga da sai na je gidansu na ji ko lafiya. Amma zan kira Farida hostel ɗin au ɗaya." Mommy ta jinjina kai ta ce, "Allah ya sa mu ji alheri." Raihan ta amsa da Amin.

Raihan ta warware garau har Daddy ya yi yunƙurin mayar da ita makaranta suka nuna ya yi wuri a mayar da ita, saboda da yin ciwonta da komawarta makaranta ko wata shida ba a yi ba. Ganin za a bata lokaci ya sa Daddy ya yi mata transfer zuwa wata Al-muwadda Privite University, babu ɓangaran da ba sa koyarwa. A tashin farko suna bawa ɗalibi zaɓi idan kai tsaye zai rinƙa ɗaukan darasi ko kuma ta online, saboda larurar Raihan ya sa Daddy ya cike mata karatu ta online. Duk wani abu da ya dace daddy ya yi mata, kuma ta ci gaba da karatunta daga in da ta tsaya. Wannan lamarin ba ƙaramin daɗi ya yi mata ba ita da Mommy su Inno kuwa sai mita suke, wai ita dai a boko za ta ƙare kullin tana abu ɗaya gara ta fitar da miji ta yi aure. A kullin bayan la'asar Khalid zai fito harabar gidan ya yi ta karatuttuka daga na Alƙur'ani har zuwa sauran littafan addini, ganin yana da ilimi mai zurfi ya sa Mommy ta yi masa magana akan zai riƙa ƙara wa Raihan karatu idan ya so sai a ƙara masa albashi. Wannan abu ba ƙaramin daɗi ya yi wa Kabiru ba kasancewar kuɗin da yake samu duk wata a wurin jinyar Mahaifinsa take ƙarewa, kuma a hakanma ba isar Mahaifiyarsa suke yi ba. Kuma ko da ganganci bai taɓa sanarwa da Daddy akan ya taimaka masa ba. Raihan sam bata da girman kai don haka duk yammaci take tafiya wurin Kabiru yana yi mata ƙarin karatu, don a lokacin ko izu talatin bata haɗa ba. Tun Kabiru yana ɗari-ɗari da Raihan ya fara sakin jikinsa da ita, don ta mayar da shi kamar kakanta kasancewarsa hausarsa ba ta daidaita ba yana magana za ka gane cikakken bafulatani ne. Da wannan take zolayarsa har take kiransa da suna Fillo, daga ƙarshe ma cewa ta yi bayan karatun addini har fillanci zai riƙa koyar da ita. Kwana Raihan biyu da fara ɗaukan Darasi suna zaune za su fara karatu sai ga Inno ta taho sanye da hijabi hannunta ɗauke da kur'ani. Raihan ta dube ta don ta fahimci sarai abin da Inno take nufi, tana shirin yi wa Inno magana ta ji Goggo ta ce.

"La'ilah'illahu Muhammada Rasulillahi Sallallahu AlaihiWasallam. Yanzu haka za ki min saboda Allah daga na ce miki zan fara ɗaukan darasi wurin Kabiru sai ki rigani?" Inno ta ja farar kujera ta zauna ta ce, "Shi dai karatu ba a yi masa masifa, ki bi a sannu Zinaru wallahi kika sa masifa ƙwaƙwalwarki ta ƙi ɗauka. Ina dalili don za a biya min karatu ki hau kaina da faɗa, Izifina goma sha biyar ke kuma kin ce goma Allah na tuba ko sauka sai na kusa shekara da yi kafin ki sauke." Goggo na daga wurin da take ta sauri ta ce, "Tuf tuf tuf bakinki ya sari ƙaton kashi, wallahi ko a albasu na haure izifi ashirin, sauka kuma kamar na yi na gama." Raihan ta kalli Inno ta ɓata fuska tana cewa, "To wai Inno wa ya ce ku zo a biya muku karatun?" Inno ta dubi Kabiru ta nuna shi da yatsa, Kabiru ya zaro ido don shi bai san lokacin da aka yi haka ba da shi ba, yana tsaka da tunani ya ji Inno ta ce, "Yanzu Kabiru samun ladan tsofaffi har sai an ce maka ka yi?" Kabiru yana murmushi ya ce, "Shi kenan Inno amma ku bari na gama biya mata sai na dawo kanku." Da wannan shawara ya samu ya shawo kan su har ya fara biyawa Raihan karatu, Goggo na ƙarasowa a ƙufule ta ce, "Wallahi idan ban yi wa mutum adda'u ƙwaƙwalwarsa ta toshe ba." Inno ta watsa wa Goggo harara ta ce, "Mutum yana surutu ana karatu idan ya zama daddawa babu abin da zai hana ni kai shi kasuwa na sayar, na sayi lamurje na sha na fitsarar da abin banza."

Littafin kuɗi ne 300 idan kina buƙata ki min mgn 0706 206 2624

25


Goggo na jin haka ta zabura za ta yi magana Kabiru ya katse karatun da yake yi ya ce, "Don Allah ku yi haƙuri Goggo idan ana karatun alƙur'ani ba a surutu saboda muhimmancinsa." Inno ta sa hannu a saitin bakinta ta ce, "In dai ni ce kabiru an bar maganar har abada." Murmushi ya yi mata ita ma Goggo ta ja bakinta ta yi shiru, sai da ya gama biya wa Raihan karatu sannan ya biya wa su Inno kowacce ya yi mata ƙari daga in da ta tsaya. Suna cikin karatu Daddy ya shigo abin ba ƙaramin birge shi ya yi ba, karo na farko kenan da ya ji Kabiru ya matuƙar birge shi. Sai da ya yi musu sannu da hutawa sannan ya wuce gida. Yana shiga Mommy ta tare rungumo shi tana faɗin, "Daddy barka da zuwa." Zagayo da ita jikinsa ya yi haɗe da ɗora kansa a jikin wuyansa ya ce, "Zainabuna bakya girma." Mommy ta juyo wa ta yi ta kashe masa ido ɗaya ta ce, "Addu'a nake Allah ya kawo wa Raihan mijin aure ta tafi gidanta ta ba ni wuri ta yadda zan ci duniyata da tsinke." Daddy ya yi dariya yana faɗin, "A gaban su Inno?" Mommy ta ɗaga masa kafaɗa cikin nuna rashin damuwa ta ce, "Su Inno tuni ai sun zama Kakannina don budurin da suke yi, yadda ka san a gidan Raihan haka suke yi." Daddy ya yi dariya har da ƙyaƙyatawa ya ce, "Ai ko baki faɗa ba na sani don diramar su Inno sai mai haƙuri ne zai iya jurawa." Ɓangaren Daddy suka wuce ta taimaka masa ya shiga wanka bayan ya fito suka ci abinci.

Akwana a tashi babu wuya a wurin Allah haka rayuwa ta ci gaba da gangarawa, wata rana Raihan ta fita shopping ɗin kayan shafe-shafenta da turarruka a WAHIDAH SHOPPING COMPLEX. Kayan shafa ta siyo har ta kusa zuwa wurin Accountant don ta biya kuɗi ta manta ba ta ɗebo da turarruka ba, da sauri ta juya don ta lura yamma ta ƙarato sosai ga shi Mommy ta ce karta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login