Showing 45001 words to 48000 words out of 135404 words
nufar ta.
“Mami na oyoyo”
Murmushi matar tayi wacce fuskar ta ke zubi da ta prettyn.
“Oyoyo shalelen Daddyn ta, kin dawo kenan?”
Yamutsa fuska Pretty tayi tace
“Eh na dawo Mami”
Ƙura mata ido Mamin tayi ganin damuwa a fuskar ta.
“Lafiya mutanen Adamawa an dace dai?”
Kwaɓe fuska Pretty tayi kafin tace
“Mami wannan sai kin taimaka, wallahi mami kamar gunki yake, ko saurara ta baiyi ba”
Zaro ido Mamin tayi tace
“Ban gane ba”
Pretty ta ce “Mami nidai kisan yadda zaki yi na auri Captain Alee in ba haka ba mutuwa zanyi”
Cikin sigar rarrashi Mamin tace
“Is ok Shalele, Yau ba sai gobe ba zamu wuce wurin na kan dutse, shi ɗin wa da zai ƙi saurarar ki?, In kina so ma cikin one month za'a yi auren”
Cike da farin ciki tayi hugging Mami tare da kissing goshin ta.
“Thank u Mami na, bari na shiga ciki”
Kai Mami ta gyaɗa hakan yasa Pretty Jan trolleyn ta ta wuce ciki Mami kuma ta tsunduma duniyar tunani.
Cije leɓe yayi tare da faɗin “Fansar mu ce wannan lokacin!”
Daga haka ta miƙe.
*ƳAR IYA POV*
Tun bayan bikin A'i Ƴar Iya ta rasa abokiya amma duk da haka bata bar halin ba.
Yau ma kamar kullum tafe take tana waƙar ta sai ga wasu yara sun zo wucewa kowannen su da kaji biyu a hannu. Ƴar wuƙar ta da banyi tunanin daga ina ta same ta ba ta zaro tare da nufar yaran.
Dariyar mugunta tayi haɗi da kallon su sannan tayi shiru, jikin yaran in banda karkarwa babu abinda yake yi kowa sai addu'a yake cikin ransa.
Kamar ba ita ta gama murmushi da dariyar nan ba ta haɗe rai. Kallon ɗaya su tayi tace
“A! Ɗan Manunu ina zaku je haka da kaji”
Cikin rawar murya yaron da ta ƙira sa Ɗan Manunu yace:
“Ƴar Iya aikan mu aka yi mu siyar, don Allah kar ki mana komai”
Hararar Ɗan Manunu Ƴar Iya tayi tace
“Don ubanka nace zan ma wani abu ne?”
Jin ta ɗau zafi yasa Ɗan Manunu sunkuyar da kai ƙasa tare da faɗin
“Kiyi haƙuri don Allah”.
Dariya take abunta kamar ba wacce ta tsare gida yanzu ba, can kuma tayi shiru tana bin yaran da harara, Allah sarki su kuwa kawunan su ƙasa kamar bayi a gaban sarki.
“Kuzo nan ɗaya bayan ɗaya,saura ku gudu Aradu duk na san gidan iyayen ku, kuma Aradu wanda ya gudu har uwar sa sai na yanka”
Ƴar Iya ta faɗa tana fitar da ƴar wuƙar ta waje.
Ɗaya bayan ɗaya kowa yake zuwa, haka zata karɓi kazar a gaban idon su ta yanka , in ta yanka sai ta bayar sannan tace
“Wuce gida don ubanka, ai ana buƙatar naman a gida maza a je a ci”
Haka Ƴar Iya ta kammala yanka kajin nan tas sannan ta wanke jinin da ruwan rijiyar dake gefen su sannan ta wuce gaba hankali kwance.
Ba Ƴar Iya ce ta koma gida ba sai wajajen Ishã don kuwa sai da ta biya gidan A'i taci abinci duk da cewa bata ƙoshi ba tukun ta dawo. Dawowarta kuwa yayi dai-dai da dawowar Baffi daga masallaci. Jijjiga kansa yayi cikin ransa yana roƙawar Jikar tasa shiriya a wurin Ubangiji. A zahiri kuma murmushi yayi tare da faɗin
“Shalelen Iya an dawo kenan?”
Murmushin ta maida masa, ko ba komai in taga Baffi tana jin wata irin nutsuwa
“Eh wallahi Baffi, sannu halan daga. Masallaci kake”
“Eh daga can nake” Baffi ya amsa mata.
“Sannu to, mu shiga mana”
Bin bayan ta Baffi yayi suka shiga tare.
Bayan sun shiga Iya ta kawowa Baffi langar tuwon sa da ta miya sannan ta ɗebo masa ruwa a kofin silver. Bayan ta gama da Baffi ta haɗawa shalelen ta ma nata abincin. A nan suka ci abinci dare can suka baje hira a wajen.
Ana cikin hirar Baffi ya ɗan yi shiru can kuma ya maida kallon sa ga Ƴar Iya. Baffi yace
“Shalelen Iya Ni kuwa kina zuwa gidan ƙawar ki A'i?”
Cike da basarwa ta ce
“Eh Baffi ɗazu ma naje, wani abun ne halan?”
Girgiza kai Baffi yayi yace
“Aah babu komai”.
Daga haka yayi shiru yanayin fuskar shi na sauyawa.
Jin shirun da Baffi yayi yasa Ƴar Iya ɗagowa ta kalle shi dai-dai lokacin da ta tura langar tuwon ta da ƙafa. Ƙwalalo ido waje tayi saboda yanayin hasken farin wata yayi dau, kana iya ganin komai ba tare da ka haska ba.
Tafi minti biyar tana kallon Baffi, iya kam dama bacci ya ɗauke ta bata ma san me ake yi ba. Hawayen dake zirarowa daga idon Baffi babu ƙaƙautawa shine yaja hankalin Ƴar Iya ya kuma sanya ta faɗawa duniyar tunani a karo na farko cikin rayuwar ta.
Ko me ya samu Baffin ta yake kuka? Nan da nan ita ma yanayin fuskar ta ya sauya izuwa mai nuna tsantar damuwa.
Wannan shine karo na farko da ta taɓa shiga irin wannan yanayin! Karo na farko da taji kukan wani mahaluki ya taɓa zuciyar ta har take jin rauni cikin ta! Karo na farko da taji zuciyar ta na bugawa ko me yasa?
Ba komai ne ya sanya Ƴar Iya shiga wannan yanayi ba sai jin ana mata magana cikin kunnuwan ta. Ba zata iya tantance Muryar waye ba ammah tanajin koma waye mai irin Muryar nan yana kashe mata jiki. Wannan ba shine karo na farko da taga damuwa a fuskar Baffi ba amma wannan ya tsaya mata.
Cikin kunnen ta na dama taji ana faɗin
“Ke Ƴar Iya baki ganin yadda Baffin ki yake hawaye ne?”
Cikin kunnen ta hagu kuma taji ance
“Yo ke Menene naki a ciki? Kin taɓa shi ne?”
Caraf a kunnen ta na dama aka ce mata “Ƙwarai kina da haɗi da shi, kin manta matsayin uba yake gare ki?”
“Amma ai ba uban bane” Muryar ta doke ta cikin kunnen ta na hagu.
“In kin faɗi haka baki kyauta ba, shi uban naki ya damu da ke ne?”
Toshe kunnuwan ta tayi tare da sakin wata irin ƙara sannan ta miƙe. Dai-dai wurin da Baffi yake
“Baffi na me yake damun ka”
Goge hawayen fuskar shi Baffi yayi yace
“Babu komai shalelen Iya, yau ba zaki fita dandali bane?” ya ƙarasa tare da sakin murmushi.
“A'ah Baffi, sai ka faɗa min me yake damun ka”
Murmushi yayi tare da faɗin
“Babu komai shalelen Iya”
Haɗe fuska tayi tana faɗin
“Allah Baffi duk cikin ƙauyen nan kowaye ya taɓa ka bana ƙyakewa Aradu rama maka zanyi”
Baffi yaji daɗin maganar hakan yasa ya ƙara yin murmushi.
“Ina roƙon Allah ya nuna min auren shalelen Iya ko ba komai akwai shagali”
“Hhhhh kaji Baffi”
Ta faɗa tana sakin wata mahaukaciyar dariya
“Baffi ai Ni ba zan yi aure ba”
Fuskar Baffi ta sauya ganin hakan yasa ta ce
“Kai ɗin so kake nayi aure?”
“Ehmana shalelen Iya kinga na kusa mutuwa”
“Aah Baffi na, to ai zanyi kafin ka mutu ɗin”
Murmushi Baffi yayi yace
“To Allah yasa!”
Ba tare da ta amsa ba ta cika bujen ta da iska daga bakin zauren tace
“Na fita zaga gari”
Washegari da safe bayan ta farka kamar kullum, ko fuska bata wanke ba ta jawo ɗumamen ta da Iya ta gama rabawa. Tana gama cinyewa ta cika bujen ta da iska.
Tayi yawo sosai sai da Azahar ta wuce gidan A'i, guntun abinci taci bata wani daɗe ba tace zata tafi.
Da yammaci Ƴar Iya ta nufi fada, a can ta zauna gaban Arɗo. Cike da tsoro Arɗo ya gaida ta.
“Ƴar Iya ina wunin mu”
Babu kunya ta amsa da “Lafiya ƙalau”
Nazartar ta yayi na wani lokaci kafin yace
“Lafiya dai ko wani abun kike so halan”
An zo wajen, dariya tayi don ranta kafin tace
“Arɗo akwai fahimta Aradu, ƙwarai abu nake so”
Gyara zaman shi yayi yace
“To ina jinki Ƴar Iya, menene kike so haka?”
Itama sai da ta gyara zaman ta sannan tace
“Ina so zanyi aure ne”
Arɗo bai yi mamakin jin hakan ba saboda dama ita bata ga kunya ba duk da kasancewar ta jinin Fulani.
Dariya yayi tare da faɗin
“Masha Allahu, abu yayi kyau, ai haka ake so, shekaru sha uku ai kin ɗana ya kamata ki huta”
Murmushi tayi sannan ta fara magana
“To Arɗo ai ba iya maganar da ta kawo Ni ba, ba kuma ka tambayi waye mijin ba”
Ta ƙarasa tana fari da idanun ta.
“O oo ai dai kam, to wanene angon?”
Dariya tayi sannan tace
“Nima ban sani ba, sai dai yau ina so ka sanar bayan sallar magrib duk wani saurayi dake cikin Gallara ya iso fada ana neman sa, daga nan sai in zaɓa”
Cikin farin ciki arɗo yace
“To to to ai shikenan yanzu za'a sanar, wannan ai abun farin ciki ne”
Cikin ranshi yace “Zaa rabu da Bala'i da yardar Allah ”
Tun daga wannan lokaci Ƴar Iya ta baro fada bata tsaya ko ina ba sai gidan Iya.
Hajiya Iya lokacin tana kwashe tuwo taji shigowar shalelen nata. Kallon ta Iya tayi ganin farin ciki kwance a fuskar ta yasa itama tayi murmushi tare da faɗin
“A! Shalelen Iya har kin dawo yau ɗin”
“E Iya na dawo, yau kam farin ciki nake kuma zaku shiga in kun san dalili”
Cike da mamaki Iya tace
“Affafai! Halan kuɗi kika samo?”
“Yo Iya in kuɗi ne ai da sauƙi, to na kisa komawa birni saboda aure zanyi”
Farin cikin ya hana iya magana can dai tace
“Naji daɗi sosai, Shalele aure fa kika ce?”
“Eh mana Iya aure nace! Ko baki so ne?”
“A'ah Shalele na, Ni kuwa nake so kiyi aure baki ga duk sa'annin ki ma sunyi auren ba, basu har da ɗa ko ƴa”
Iya ta faɗa tana murmusawa.
Ɓangaren Ƴar Iya ma haka kawai take jin wannan auren a ranta, zata yi ko dan Iya sa Baffi su ji daɗi.
COMMENT, LIKE and SHARE FISABILILLAHI!
Ina matuƙar alfahari da ku masoya na, wannan shine wasa farin girki 😄 kuci gaba da kasancewa sa alƙalamin DIAMOND LADY 💎 don jin ci gaban labarin _Ƴar Iya_
Kuyi sharhi da yawa ɗin nan thanks alot.
[6/13, 7:21 AM] Diamond Bhatool💎🩷✍️:
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸 🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
*ƳAR IYA* *(Mai hannun ɓarna)*
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
_NA_
*Fadimatu Adamu Hassan*
*Diamond Lady 💎*
SHAFI NA “““47&48”””"
Washegari da sassafe Mami ta shirya musu tafiya. Ta haɗa komai tun daga kan abinci har zuwa abun sha kasancewar tafiyar zata yi tsawo zasu kwashe kwana guda da yini kafin su isa.
Zuciyar Pretty tayi wasai, farin ciki kawai take Sweetheart zai so ta kuma zata mallake shi. Duk wannan shirin da suke Daddy bai sani ba, sai dai tun ranar da Pretty ta tayar mishi da gyambon dake zuciyarshi ya kasa sukuni, wutar ɗaukar fansa ce ko yaushe take ruruwa cikin ranshi.
Misalin ƙarfe goma na safe suka ɗauki hanya sai wajen Natoli aiki yanzu magani yanzu. Mami da kanta take driving nasu har suka yi tafiya mai nisa. Wuraren Azahar suka yada zango tare da cin abinci daga nan suka yi gaba babu batun sallah a ransu.
Har maghrib basu ƙara tsayawa ba sai da suka ga sun shigo wani ɗan ƙauye, hakan yasa suka yada zango ba tare da sun fice daga motar ba, a nan suka ƙara cin abinci suka sha abun sha. Mami da ta riga ta gaji ta koma seat ɗin mai zaman banza tare da kwantar da kanta, nan bacci ya kwashe ta.
Ba su suka bar ƙauyen nan ba sai da Asubahi sannan suka ƙara yankar hanya, sunyi tafiya sosai kafin suka kai ga wata hanya da ta rabe biyu, ɗaya abushe take ƙaraf yayin da ɗayar kuma alamun damshi da ni'ima suka bayyana tattare da ƙasar. Hanyar da ta bushe Mami ta umarci Pretty da ta ɗauka, babu musu ta yanki hanya.
Tafiya suke amma babu ko alamar ƙuda da ke rayuwa cikin wannan sahara, har sai da yamma tayi tukun suka fara hango hayaƙi na tashi, nan Mami tayi murmushi ta kalli Pretty dake tuƙi cike da gajiya sannan tace
“Kuka ya ƙare, Captain Alee zai so ɗiyata”
Ɗaga ido Pretty tayi tare da maida hankalin ta kan tuƙin da take yi tace
“Wayyoh! Can't wait”.
Daga wurin sukayi packing sannan suka fito tare da ɗaukar jakar kuɗaɗen sa suka zo dashi suna tunkarar wurin da hayaƙin yake tashi. Sunci uwar tafiya kafin su kai ga wani ƙatoton dutse wanda ke ɗauke da wani wankamemen kogo, nan da nan jikin Pretty ya fara rawa.
“Mami nikam mu koma”
Harara mami ta Banka mata
“Baki da hankali ma” ta faɗa tare da jan hannun Pretty suna tunkarar kogon.
Tun daga baƙin ƙofa suke jin wani sauti, shi ba kuka ba sannan shi ba dariya ba, a haka dai suka daure tare da kutsawa ciki. Wata mahaukaciyar tsawa mai razanarwa aka yi ana faɗin
“Ba'a shiga da ƙafar dama”
Da ƙyar suka shiga aikin yadda suka kiɗime. Suna shiga wata guguwa ta tashi yayin da wani duhu ya mamaye wurin. Can bayan waɗansu daƙiƙu haske ya dawo, guguwar nan ma ta ɓace nan da nan!.
Basu tsinci kansu ko ina ba sai a wani ɗaki wanda ke ɗauke da fatotin naman daji, kura ne, zaki ne, damisa ne! Da makamantansu. Tun daga nan bakin su ya mutu.
Can daga wata kusurwa ya fito, baƙi, jibgege mummunan gaske wanda fuskar shi ke ibi da ta shanu.....Natolu kenan! Suka ce sha yanzu magani yanzu. Cikin dariyar su irin ta rikaƙƙun bokaye ya zuba musu ido tare da zama gaban kayan aikin sa.
“Maraba da zuwa Hajiya Salima uwar ɗakin Ɗan Hambali”
Bokan ya faɗa yana murmushi
Sunkuyar da kai tayi don ta san dokar shi ba'a haɗa ido da shi.
“Kinzo ne batun ɗiyar ki ko, ba sai kin min bayani ba na ga zuwan ku tun jiya cikin madubi na, sai dai wannan aiki zai yi matuƙar wahala amma in kin sake kuɗi zai tafi dai-dai”
Shiru mami tayi boka yaci gaba da bayani
“Zai so ta, zai aure ta ammah kuma akwai wani abu da baya nunawa wanda da gani matsala ce, akwai abun da zai bayyana cikin rayuwar shi wanda zai zama katanga ga wannan aiki, har yanzu ban samu fahimtar menene ba ammah dai aure tsakanin ɗiyarki da yaron ba fashi”
Haka dai boka ya zance su su kuwa tsabagen farin ciki suka zuba masa kuɗin tare da fecewa abun su.
_(Ina ƙira gareku Ƴan uwa mata ku tuna cewa zuwa wurin boka haramun ne a musulunci, ku tuna duk wanda ya aikata hakan kuma toh ya aikata mafi girman laifi wurin Ubangiji kamar yadda Annabi Sallallahu Alyhi wa Sallam ya faɗa. Duk wanda ya halarci wurin boka to haƙiƙa ya kafurcewa abinda aka sauƙarwa Annabi Muhammad)_
_(Har ila yau iyaye mata ya kamata musan cewa ƴaƴan mu amana ce da Ubangiji ya bamu, ya zama dole mu kula da su mu kuma basu tarbiyya mai kyau kamar yadda yazo cikin Alqur'ani, haka nan annabi ma ya ƙara nanatawa Muminai a kan irin girman da amanar yaro take da shi a wurin iyayen shi!)_
_(Kada ki kasance cikin iyayen da zasu banzatar da yaran su, iyayen da basu damu da tarbiyyar yaransu ba! Kada ki kasance cikin su don kuwa ki sani Ubangiji zai tsayar da ke ranar alƙiyama ya tambaye ki a kan kiwon nan tun daga haihuwa, girman su zuwa mutuwar su? Wace rawa kika taka cikin rayuwar su?, Shin kin basu tarbiyya ko akasin haka)_
_Allah ya shiryar da mu sannan ya bamu ikon kiyaye amanar da ya bamu na yaran mu_
Tunda suka dawo tayi wanka ta huta washegari tabi Flight ɗin da zai kaita Adamawa. Tana isa ta wuce army barrack na su Hamma Zaki, tana isa ta tambayi office nashi aka nuna mata.
Dai-dai corridor na office ta tsaya tare da fitar da wata kwalba mai ɗauke da wani jan abu a ciki. Murmushi tayi tare da buɗe ta ta juye ta kaf a jikin ta, nan take wani irin mahaukacin ƙamshi ya tashi a wurin.
Sai da Pretty ta daidaita kanta sannan ta yi knocking, “Yes come in” ya faɗa cikin kamammiyar Muryar shi.
Shiga ciki tayi tana wani rangwaɗa shi kuwa hankalin shi na kan wata takarda da yake karantawa. Ƙamshin da ya bugi hancinsa ne ya dawo dashi daga duniyar tunani.
Murmushi ta aika masa tare da faɗin
“Hi Sweetheart!, Na dawo gare ka Please wannan lokacin kada kace a'a in ba haka ba zan iya rasa rai na”
Lokaci ɗaya ya ɗago da niyyar balbaleta sai dai ƙamshin da ya ƙara ziyartan hancinsa ya dakatar da shi.
“Say something sweetheart ko na koma?”
Samun kanshi yayi da jijjiga mata kai, murmushi tayi tace
“Alright bari na zauna”
Wuri Pretty ta samu ta zauna tare da kafe shi da Mayun idanuwan ta. Cikin ranta kuwa murna ce fal haka tayi ta masa zuba shi kuma ya kasa hanata sai ido kawai yake Binta da shi.
Lokaci azahar ya shiga toilet tare da ɗauro alwala yayi sallah Pretty kuma lokacin ta fice, abinci tayi musu order tare da dawowa. A nan suka ci har Yamma.
Lokacin tashinsa ma da yayi tare suka wuce a motar shi kowa sai mamaki yake ganin Captain Alee da mace. Wanda hakan ɗin duk shirin ta ne da kuma roƙon shi da tayi ya barta ta sauƙa gidansu.
Bayan sun koma gida Mom ta jima tana mamakin dawowar Hamma Zaki da mace! Haka dai sauran mutanen gidan. Ita dai Sarah Bata kula ta ba haka ta ishi mutane da iyayi da feleƙen tsiya.
Washegari ma tare suka fita coz tace mishi zata koma gida washegari ne ammah tana so ya tura iyayen shi a sanya ranar auren su. Kamar wani gaula kuwa ya sanar da Daddy da Mom, duk irin yadda Daddy ke son Hamma Zaki yayi aure kawai taji abun ya fita mishi a rai saboda yarinyar amma babu yadda zai yi tunda shi yake so. Ita kuwa Mom a matsayin ta na baindiya tasan sihiri iri-iri coz duk wasu shu'uman sihirhiru daga India yawanci suka samo tushe, a lokacin ta tabbatar ɗan ta yana cikin kogin asiri ne sai dai ta ɗauki alwashin ɓata aikin nan gaba saboda wani dalili.
Bayan Pretty ta wuce gida haka tayi ta damun Hamma Zaki da ƙira, dare, raba, safiya kamar jaraba, babu laifi kuma tana ɗagawa duk da cewa baya jin komai game da yarinyar kawai dai shima ya ji ya amince da buƙatar tata ce.
Su Dr Faruq sunyi mamaki sosai haka su Nenne, Mommah, granny Kai duk iyalen Muhammad Naira sunji a jikin su.
Bayan sati ya zagayo uncle Suraj da