Showing 69001 words to 72000 words out of 184937 words
haɗin kai ba wanda zai taɓa wannan lafiyayyar fatar taki idan kuma kikace gadda ma da taurin kai zakiyi yanzu zan farfasa lallausar fatar da kike tsoron kar ataɓa, cikin tsuke fuska yace"gaya min waya saka ki saka yin kisa?wani irin kuka ta fashe dashi tana wani irin girgiza kanta,tsawa ya daka mata tare da cewa ke nake jira ki bani amsa kuma ki faɗi gaskiya bazan ɗaga miki ƙafa ba idan kika yimin ƙarya!', numfashin ta har sarƙewa yake ta kuma kasa yin magana sai ruwan hawayen da da ace yana ƙare wa da yanzu na Bintu ya ƙare,kallon ƴar sandar yayi tare da yi mata alama Aikuwa ta dai daici kyakykyawar fuskar Bintu ta zabga mata mari wanda sai da taga giftawar wasu taurari,kamar zata shiɗe haka ta fixgo maganar daga bakinta,wal wal wal wallahi bani bace ban san komai ba kar ku dakeni bana son duka fafina kazo kabuge su kacire Ni anan gun ni ban san komai ba!'dalla Malama rufe mana baki duka kuwa kamar kin sameshi kin gama tunda baza ki gaya mana gaskiya ba!'cewar ƴar sandar nan,yace"rabu da ita yanzu zataci ubanta tunda bazata faɗa ba!'
Suna shiga cikin ainahin station ɗin ya dinga jin bugun zuciyar sa na ƙaruwa,da ƙyar ya iya sauraran ƴan san dan suka bin cika masa sunan Bintu, duk da sun san nan aka kawo ta amma sai suka farayiwa Abdallah ƴan kewaye kewaye na nuna alamun suna san wani abu daga hannun sa,ai tun da Abdallah ya tabbatar Bintu dai tana cikin wannan station ɗin ya wuce su cikin wani irin ƙaƙƙarfan taku irin na jaruman maza masu ji da da kuzari,da sauri wani yazo zai tare masa hanya amma kallon da Abdallah yai masa sai da yasa shi sakin acawi a wando,ci gaba yayi da tafiya batare da ya saurari ƙananan maganganun da suke ba,
Duka na farko da ya kaiwa Bintu akan idon Oga Abdallah, ya ɗaga zai kai mata na biyu,yaji anyi wata majaujawa dashi,wanda tashin farko yasamu karaya a hannun da yake dukan Bintu dashi,bai gama dawowa daga wannan azabar ba ya kuma jin wani uban naushi acikin sa wanda atake agurin ya zube,shi kuma Abdallah ya kuma samun damar take ƙafar sa itama atake tasamu karaya,kafin wani lokaci ƴan sandan sun gar zaya dan sanar da inspector lawan.
Da wani irin azama ta ƙara so duk da jikinta babu ƙarfi amma ita ba wannan ne damuwar taba, farin cikin ganin sa A raye yafi mata komai arayuwarta,saurin tarar ta yayi ganin tana shirin faɗuwa, wata irin runguma tayi masa mai cike da wani irin salo da ɗoki da wani irin gawur taccen farin cikin da baza ta iya musaltashi ba,tallafo ta yayi tamkar jaririya wani irin kallonta yakeyi kamar wanda yake bincikawa dan ya ga ko ancire wani abu ajikinta,cikin sa'a yaga shatin marin da ƴar sandar nan tayi mata,cikin wata irin murya mai cike da wani irin amo da ya gauraye da ɓacin rai yace"waye ya mareki tun yaushe suka fara dukanki?cikin ɓoye fuskar a ƙirjin sa tayi nuni da inda ƴar sandar take A tsaye tamkar wadda aka liƙa tun lokacin da taga an zubar da oganta cikin halin mutuwa ko rayuwa,bata gama shiga tashin hankali ba sai da taga Abdallah yayi mata alama da tazo batare dashi ya motsa daga inda yake ba,cikin rawar jiki ta ƙaraso kafin tasan abinyi taji ya ɗauke ta da wani zazzafan mari wanda lokaci guda ya ɗauke mata ji da ganin ta na wasu mintuna,duk da sun kasan ce ƴan sanda amma basu da ƙarfin gwiwar sa insa da Oga Abdallah, kwarjinin sa da ilhamarsa sun wuce ka tsaya yana faɗa kana faɗa, ƙoƙarin gyara mata zama ajikin sa yake ɗan yaji daɗin tafiya,amma sai ta saki kuka ta saka tana ƙara cukume shi,dan atunanin ta tafiya zaiyi ya barta,ƙara sautin kukan tayi tare da cewa Ni bazan zauna ba duka na sukeyi tsawa suke min na ce musu ban san komai ba sunƙi yadda,gashi kaima baka yadda ba tafiya zakayi kabarni, wallahi bani bace,idan katafi kasheni zasuyi,idan baka yadda dani ba ban san wa zai yadda dani ba,yunwa nake ji basu bani abinci ba basu bani ruwa ba mugaye ne basu da imani,katai maka koda baka yadda dani ba kafitar dani daga nan na maka alƙawarin bazan koma gidan kuba!' Abdallah ya ɗan rumtse idanun sa saboda yadda kalaman ta suke dukan zuciyar sa, A rayuwarsa ya daɗe bai cikaro da abinda ya bashi tausayi ba kamar Bintu ba,wani ɗan danshi yaji cikin idanun sa wanda ya tabbatar ƙwalla ce amma bai bari ta zubo ba,saurin ɗaga ta yayi kamar wata ƴar tsana haka ya sunkuceta,
Cirko cirko yagan su tsaye sun kasa yin ko tari da kyar ɗaya daga cikin su yace"yallaɓai yace kaji ra shi yataho!'ko kallo bai isheshi ba,sai da ya fita ya farfajiyar station ɗin kana ya tuna babu mota A hannun sa,babu waya.
Motar da ta faka a gabansa ita tasa ya maida hankalinsa kan wanda ya fito daga motar, inspector lawan ne sai Dady jafar,ɗauke kansa yayi yana ƙoƙarin barin gurin dan baya bukatar ganin su balle yayi magana da su, inspector lawan ne yace"ka dakata wannan ba hurumin ka bane ya kamata ka barmu muyi aikinmu,dole kabamu ita saboda ka karya mana doka ka daki ma alokacin mu,dan haka bazan baka koda belin ta ba!cikin tsanaki yake binsa da kallon mahaukaci mara imani,wata Napep ce ta shigo dan haka ya daga ƙafa zai ƙarasa inda take sai yaga ashe ma wanda yakawoshi ne ya dawo karɓar kuɗin sa,shiga yayi ya kwantar da ita A bayan Napep ɗin,cikin hanzari yake ƙoƙarin shiga saboda yadda yaga Bintu bata numfashi saboda yadda ta gala baita ga yunwa da ƙishi duk A tare da ita, inspector ne ya kuma yi masa magana, Abdallah kar kasake ka fita da yarinyar nan batare da ka cika ƙa idoji ba!' cikin wata irin ɓacin rai Abdallah ya nuna lawan da yatsa cikin muryar sa dake fita ɗaiɗai yace"kar ka sake kakuma da Katar dani idan kuma ba haka ba zakayi da nasanin tsayawa agabana kana yimin umarni!'daga haka ya faɗa Napep ɗin ya bar inspector lawan da baki sake cike da mamakin kwarjinin Abdallah,saboda shika kansa ƙarfin hali yake wajen kallon idanun sa.
Suna tafiya ya dubi Dady jafar da ya tsaya kawai yana kallon su, inspector lawan yace"bai kamata ka tsaya kana kallon mu haka ba kamata yayi ka da Katar dashi tunda kaima kasan abinda yayi bai kyauta ba!'Dady jafar ya ɗan ɗage kafadar sa tare da cewa hakan da yayi shine dai dai matsayin sa na wanda aka yiwa wannan laifin yazo ya fitar da wadda akace ta aikata laifin to kuma kai meye naka aciki,ko bakasan cewa matar da zai aura bace? cikin tsananin mamaki inspector lawan ya maimai ta kalmomin, matar da zai aura kuma!' Dady jafar yace"ƙwarai kuwa ko kana mamaki ne? girgiza kansa yayi yace" ai dole nayi mamaki matar da zaka aura kuma ta nemi kashe ka? gaskiya abin da kwai rikitarwa,da matuƙar al'ajabi!'Dady jafar yace"shi yasa nace maka ka rabu da wannan case ɗin, na cikin gida ne saboda Bintu ba itace tayi wannan laifin ba kasan dai matsayi na amma banyi amfani da hakan ba a matsayina na uban Abdallah,dan haka ina baka shawara ka fita daga wannan sabgar dan kar kazo kayi nadama!'daga haka bai sake cewa komai ba shima ya wuce ya bar station ɗin.
Har cikin gidan sa na area 1 me Napep ya kaisu,kuma har lokacin Bintu bata farfaɗo ba ɗaukar ta ya kumayi a kafaɗa ba tare da ya tsaya ba yace" da me napep ɗin ya biyo shi, jiki na rawa yabi bayansa ko tsoro bayaji ko ɗan yankan kaine,suna shiga tangameman falon da ya kusa zautar da me Napep, Abdallah ya kuma cewa da shi ka dakata A nan ina fitowa!' amsawa yayi jikin sa na ɓari,shi kuwa Abdallah kai tsaye saman haɗaɗɗen benan da aka ƙawata shi a tsakiyar falon ya hau Bintu shimfiɗe A kan kafaɗar sa,kai masha Allah abinda nace kenan lokacin da naga ya kwantar da ita cikin wani lafiyayyan gado mai rai da lafiya tabbas idan kashiga ɗakin nan idan bakayi sa a ba sai kamanta a duniyar da kake,komawa yayi ya sallami me Napep da ɗaurin dubu hamsin bai tsaya sauraran doguwar godiyar da yake masa ba cikin gaggawa ya koma ɗakin tare da fara bata taimakon gaggawa,duk da shima har yanzu bajin daɗin cikin sa yake yiba amma saida ya tabbatar Bintu ta dawo hayyacin ta duk da dai bata farka ba,saboda allurar baccin da yayi mata bata cikin hayyacinta,dan da a dai dai take yasan sai yasha daru,gyara mata kwanciya yayi bayan yasa mata ruwa,
Sai lokacin hankalin sa ya dawo jikin sa fita yayi ya koma ɗaya ɗakin shima ya ɗan watsa ruwa kana ya zura doguwar jallabiya me ruwan toka,san nan ya nufi wajen daya killace shi dan yin ibadarsa cikin nutsuwa.
A can ESTATE kuwa Anty Nafisa ce zaune cikin ɗakinta tagumi hannuwa biyu,babu abinda take sai tunanin hanyar da zatabi tacika burinta, yanzu idan akace Bintu gidan kaso za a kaita wa zata samu ta maye mata gurbin ta?san nan taya zatayi tasan wanda yasa ta wannan aikin meye kuma dalilin da yasa ita batayi mata irin wannan aikin ba taje tayiwa wani?tabbas dolene ta samu waɗan nan amsoshin daga bakinta,domin taga haɗamammun gidan kullum ƙaruwa suke dole tayi hanzarin cika burin ta,to amma yanzu fatan da take yi Allah ya dawo da Bintu saboda A yanzu ne zata fiyi mata amfani dan tasan tabbas Bintu zata iya karɓar aikin ta yanzu,to kuma idan taji tsorofa?duk yanda zatayi dole sai tayi dan rufin asirin ta da kuma samun burinta,ɗan kashingiɗa tayi tare da tsurawa hotan mijin nata ido haƙiƙa tana matsanancin son mijin ta, A baya tayi tunanin bazata iya wata rayuwa ba idan babushi har tana tsoron ranar da asirinta zai tonu saboda gudun samun tangarɗa A cikin zamansu, sai kuma gashi katsam Hajiyarta ta nusar da ita tare da ɗorata A hanya wanda har ma ji take A yanzu tafi Hajiyartata sanin matakan aikin,kawar da kanta tayi daga kallon hotan dan bata so taji tausayi ko ɗugon imani A cikin dukan niyarta ta samun duniyar ta.
Farida ta zubawa Taufiƙa ido tana sauraran ta cikin azalzalar da zuciyarta take mata take cewa, Wallahi Farida da zan samu dama saina bita har cikin station ɗin na kashe rayuwar ta ɗan bata da wani amfani!'Farida tace"Ni kuma ai atunanina an wuce gurin yanzu dan na tabbatar yanzu shi kansa Alhaji Baba bazai yadda da wannan auren ba, balle kuma uban gayyar bazai taɓa yadda ya auri matar datake son raba shi da rayuwarsa ba, Farida ta ɗan kalli ƙofar ɗakinsu sai da ta tabbatar babu wanda yake ƙoƙarin shigowa kana tayi ƙasa da muryar ta tare da cewa,dan Allah niko Taufiƙa na yi maki wata tambaya mana!'Taufiƙa tace"inajin ki"yauwa Dan Allah Taufiƙa bake kika haɗa wannan tuggun ba saboda kar Bintu ta auri Ya Abdallah?wani kallo Taufiƙa tayiwa Farida amma batace komai ba, saida Farida ta dafa ta tare da cewa kiyi haƙuri idan tambayar ta ɓata miki rai kawai dai abin da na sanine zaki iya aikata komai akan cikar burinki,shi yasa nayi miki wannan tambayar!'miƙewa tayi zata fita daga ɗakin cikin sauri Taufiƙa ta ruƙo hannun ta tare da cewa Wallahi Farida ban sani ba ban san waya aikata ba kuma banji haushin tambayar ki ba, kawai dai nayi mamaki ne duk wannan shedun da suka bayyana amma keda Siddiqa kuke san sawa zuciyar ku yadda da Bintu bayan kuma duk irin cika bakin da kika gamayi na ɗaukar fansa akanta,abu na biyu kuma banyi zatan zakiyi tunanin zan iya kashe abinda nake ƙauna da hannu na ba, koda kisan ne sai dai na kashe Bintu dan wannan alƙawarina ne indai Bintu ta auri Abdallah sai na hana rayuwar ta zama lafiya sai ta gwammaci mutuwar ta akan rayuwa,dan haka ki dai na tunanin Ni nayi wannan haɗin babu ruwana wannan macijiyar da take son mamaye dangin mu da salon ta na yaudara to itace ta haɗa komai,dan haka ki cire zargina da kika fara sawa A ranki!'tana gama faɗa ta saki hannun Farida tare da kwanciya saman gadon ta, Farida ta jin jina kanta tare da cewa na yadda da maganar ki Farida saboda nasan bazaki ɓoye min duk wani al'amarin da ya shafe kiba.
Tunda asuba Bintu ta farka sai dai babu ƙarfi sosai a tare da ita, kasan cewar har yanzu bata ci ko mai a cikin ta ba yanzu ma da taimakon ruwan da yasa mata samu ɗan ƙarfin jiki,tana idar da salla ya shigo ɗakin hannun sa ɗauke da wani ɗan madai daicin cop sai madai daicin kwalanda,ajiyewa yayi A gabanta batare da yace"mata komai ba yayi mata nuni da takarya yanzu,miƙewa yayi ya fita yayin da Bintu ta ɗauki cop din nan da yake shaƙe da kakkauran shayi wanda yaji haɗi,tunda ta kafa shi abakinta ba ita ta ajiye ba saida ta shanye shi tas kana ta janyo kwalandar da take ɗauke da soyayya dankali da uban ƙwai sai zabga ƙamshi yake ta hau ci so sai taci tayi ƙat,daga nan kuma ta fara tunanin wanka dan har wani ƙayƙayi taji jikinta nayi saboda rashin wanka,tashi tayi ta shiga haɗaɗɗen banɗakin da sai da taja wasu mintuna wajen ƙauyanci da kalle kalle kafin ta fara gabatar da wankan ta sai da taji fatar jikinta har zafi take saboda gurza haka gashin kanta kana ta haƙura ta fito,kamar wancan lokacin yauma doguwar A baya ta samu saman gadon murmushi tayi tare da cewa,yau dai bazan ce wataran ne kake da kirki ba kana da kirki, kullum kai mai kirki ne mai tausayawa rayuwata Oga Abdallah kai na musamman ne gaskiyar fafina ne da yace" kai zaka zama jagora kuma garkuwa a gareni tabbas na haɗu da mai sharen hawayena,inayin ka ogana over!' tayi waɗi ɗan juyi mai cike da nishadin dake tattare da farinciki.
Shi kuwa Abdallah bayan gama shirin sa Yahya ya kira yace"masa zasuje can office ɗin sirri saboda akwai buƙatar zuwan sa A yau ɗin,bayan gama wayar tasa ne ya koma ɗakin da Bintun take ciki,sai da ya ɗan yi knoc ta bashi izinin shiga kana ya shiga ,cikin wannan yanayin nasa na kirnewa wanda ita a yanzu bai dame ta ba, ya nufi wata durowa kai tsaye taga ya ɗauko magunguna har da allurai cikin sauri ta tashi zata shiga banɗaki, wanda kanta kai ga buɗewa ya danƙo hannun ta cikin zafin nama irin nasa na ƙarfaffan namiji,waro manyan idanunta tayi saboda ita tsoro ma ya bata dan bata san lokacin da har ya ƙara so ba,kwaɓe fuska tayi tana shirin sakin mai kuka saurin ɗora yatsun sa yayi kan jajayen laɓɓansa yayi mata alamar tayi masa shuru,batayi kukan ba amma bata saki fuskar ba, jawo ta yayi ya zaunar da ita gefan gadon,kana ya nufi ɗan ƙaramin frige ɗin da yake ɗakin ya bude ya ɗauko gorar ruwa ya ɓalle maganin ya miƙa mata tare da ruwan,karɓa tayi ta shiga juya sa cikin hannun ta,tunda ya shigo sai yanzu bakinsa ya motsa,Malama kina ɓatan lokaci ina da abinyi!'cikin tura baki tace"to kayi tafiyar ka zan sha!'kawai gani tayi ya shiga haɗa allura, cikin rigimammiyar Muryar ta tace"Ni dai banason allura zansha maganin ko kallon ta baiyi ba ya cigaba da abinda yakeyi,da taga dai da gaske yakeyi allurar zaiyi mata kawai sai ta miƙe zata gudu daga ɗakin, cikin azama ya fizgota ta faɗa jikin sa dama ya gama haɗa allurar riƙe ta yayi sasai ya tsira mata allurar kuka takeyi sosai hadda su kai masa duka a ƙirji amma bai rabu da ita ba sai da ya tabbatar allurar ta gama samun mazauni cikin jininta kana ya saketa yana watsa mata harara,juyawa yayi ya fice yana aiyana rigima da sakalci irin na Bintu A ransa, A nan kan gadon ta gama birgimar ta daga ƙarshe kuma bacci yayi awan gaba da ita.
Tacan ɓangaren Alhaji Baba kuwa A safiyar yau ne ya A kuma cikin masallaci bayan idarwarsu daga sallar asuba ya umarci liman da yasanar da akwai ɗaurin auren da za A gabatar yanzu in Allah ya amince, tare da miƙawa Abba Umar kuɗi dubu ɗari biyu cif tare da ce masa Umar inaso kazama wakilin wannan marainiyar Allah Bintu nasan kai kaɗai ne zakayi min biyayyar yin haka batare da son jin ba asi ko kuma gar dama ba!' Abba Umar wanda ya sauka da asubahin ranar daga tafiyar da yayi duk da dai ba da ɗewa zaiyi ba, yasa hannu biyu ya amshi kuɗin da mahaifinsa yake miƙa masa,haka nan ya tsinci zuciyar sa cikin wani irin maɗaukakin farin ciki tamkar anyi masa bushara da aljanna,sauran yaran Alhaji Baba da ƴaƴan ƴan uwansa da jikokin sa da duk wanda yake zaune cikin wannan ESTATE kuma yasan abinda ya faru da Abdallah da Bintu saida ya shiga cikin tsananin mamaki da kuma tashin hankalin wannan al'amari,basu taɓa tsammanin cewa Alhaji Baba bai yadda da abinda yaji kuma ya gani akan gubar da Bintu ta zubawa Abdallah ba,sai gashi ya basu wani irin rikitaccen mamaki da ɗaurawa Bintu da Abdallah aure.
A wannan rana ta juma'a da misalin ƙarfe bakwai nasafiyar ranar mutanen da suke cikin ESTATE da maƙota da masu gadi da direbobi da ma sauran manyan mutanen da Alhaji Baba duk ya riga yasanar musu, wanda wasu sai bayan idar da salla suka dinga shigowa wanda daga cikin su har da manyan Aminan sa su Alhaji Nasir Wanda su basu san kiran nasa na meye ba sai da suka zo,duk sun shaida Auren Fatima Bintu Zahra da kuma angonta Abdallah Jafar,kai wannan rana na kuma sakan kan cewa, imani ya kuma ratsani na kuma sallamawa ubangi ƙadiran Ala manyasha'u, na kuma jinjinawa ƘUDURARSA, da ikon sa tare da buwayar sa, abinda yaso ya kasan ce ko ta yaya sai ya kasance Alhaji Umar ya ɗaura Auren ƴarsa ta cikin sa da hannun sa batare da shima yasani ba,batare da sanin kowa ba Allah ya zartar da ƙudurar sa