Showing 159001 words to 162000 words out of 184937 words
Dady Mansur yayi sai yaga ya gyada masa kai alamun ya faɗi abinda yake son faɗa babu matsala,dan haka sai Abdallah ya maida hankalinsa kan Alhaji Baba tare da cewa,dama ina sone gobe idan Allah ya kaimu katara duk mutanen gidan nan acikin falon ka,hatta da surukai ban ɗauke su ba,idan nace kowa ina nufin kowa da kowa sai dai wanda baya nan,ƙarfe huɗu bayan sallar la asar akwai abinda nake son GABATAR muku dashi mai matukar muhimmanci,amma dan Allah acikin waɗanda basa nan ina buƙatar Abba Umar a wan nan zaman saboda zuwan nasa yana da muhimmanci!'jinjina kai kawai Alhaji Baba yake sai da yaji Abdallah ya kawo karshe a maganar sa, kana yace"wannan ba abin damuwa bane Abdallah fatana kawai Allah yajiyar damu Alkhairi Allah yasa taron da zai amfanemu ne baki ɗaya,gaba dayan su suka amsa da Amin,daga nan suka bar falon shida Bintu suka bar Dady Mansur.
Tun bayan dawowar ta daga gidan ta rasa sukuni gaba ɗaya cikin fargaba take,duk motsin da zataji sai ta zabura,ta kasa zuwa ko ina,ta kuma rasa ta hayar da ya kamata ta binciki su Abdallah ko sun gano makircin ta,duk da ko tasamu hanyar baza ta iya aikatawa ba saboda kar taje allura ta tono garma,sallamar Taufiƙa ce"ta dawo da ita hayyacinta,zama tayi akusa da ita tana cewa Hajja me yake faruwa ne naga kamar ba anutse kike ba? murmushin yake tayi tare da cewa bana dan jin daɗi ne kwana biyu!'Taufiƙa tace"ayya sannu Hajja Allah ya sauwaƙe!'tace"Amin tana ƙoƙarin miƙewa ta bar falon dan tafi buƙatar kaɗaici a wannan lokacin,kafin ta kai ga mikewar ta kuma tsinkayar muryar BINTU tana rangaɗa sallama cikin sassanyar Muryar ta,wani irin tsinkewa zuciyar Hajja tayi tare da komawa ragwab ta zauna ba tare da ta shiryaba, duk wan nan tashin hankalin nata baya rasa nasaba da shigowar Abdallah cikin falon ba,yanayin takunsa na isasshen namiji da kuma kwarjinin sa, shine abin da yaso rikita ta da saurin fallasa rashin gaskiyar ta,zama yayi ba tare da ya ce komai ba sai hankalinsa dake kan wayarsa, Bintu ce ta tsuguna a gefan Hajja ta gaida ta,amsawa tayi cikin fara'ar da bata taba yiwa Bintu irinta ba,gaba ɗaya a ruɗe take saboda bata shirya komai akan tuhumar da Abdallah zaiyi mata ba,da ace ba tariga tayiwa Jafar waccen ƙaryar ba ne,to da zata iya samun abin cewa dan kare kanta,shuru falon ya ɗauka sai da Abdallah ya gama shan ƙamshin sa, kana ya juyo yana fuskan tar Hajja tare da gaishe ta,amsawa tayi cikin wani irin bugun zuciya,wanda har mamakin kanta take saboda bata taɓa tsammanin a kwai wani mahaluƙi da zataji tsoron fuskantar sa ba, sai kuma gashi har tana jin fiye da zaton ta akan jikan ta, cikin haɗe fuska da dauke kai yace"Hajja ta ɗan bamu guri!'duban Taufiƙa tayi wadda tasan cewa da ita yake,tace"Taufiƙa tashi ki bamu guri!'cikin sanyin gaddama ga umarnin da aka bata,tace"Hajja mu tashi dai ai naga bani ka ɗai bace a gurin!'wani irin rikitaccen kallo ya watsa mata wanda yasa ta tashi babu shiri har tuntuɓe take ci da ƙafar Bintu,
Tana shiga ɗakinta tayi sufa saman gadon ta,tare da saka wani irin kuka mai sosa zuciya,ko yaushe ne Bintu har ta samu irin wannan soyayya mai zafi daga gurin Abdallah?karfa bakin da inno tayi mata ya tabbata dan kuwa gashi nan ta fara ganin alamu, Taufiƙa sai dai hakuri fa dan daga dukkan alama dai Abdallah ya rufe ƙofa,
A can falon Hajja kuwa bayan da ya tabbatar da Taufiƙa ta bar wajen,sai ya ɗan kuma gyara zaman shi cikin nutsuwa yace"Hajjah dama nazo ne akan maganar Dadyna!'yadda ta zuba masa ido da yanayin ruɗewa shine yaso bashi ƴar dariya,sai dai kuma yayi ƙoƙarin maida ta tunda dama ba al aldarshi bace,cikin ɗan ruɗewar da ta farayi tace"Abubakar ke nan?yace"wanda kika tafi dashi jiya!'ya faɗa idanun sa akan Bintu wadda ita kuma ta zubawa Hajja nata idon dan har yanzu al'amarin mamaki yake bata, bata taɓa yiwa Hajja kallon muguwaba amma sai gashi ya tabbata cewa itace makirar cikin zuri'ar Alhaji Baba,Hajja kuwa da kyar ta iya aro jarumta wanda duk da haka tsoran ta da rashin gaskiyar ta bai kasa bayyanuwa ba,cikin kasa haɗa ido da ɗayansu tace"Abdallah an samu akasi fa ban san ta inda abun ya juya ba saboda wannan mutumin ba Abubakar bane,kuma ina tunanin duk daga sharrin Habibu ne!'ta juya maganar dan san tabbatar da zargin ko sun gano makircinta,cikin dabi ar sa ta rashin gano ainahin abinda yake zuciyarsa,yace"Hajja yanzu kina nufin mun kuma rasa Dady?cike da mamaki take kallon sa,kana tace"amma ai na ɗauka duk ku kuka shirya hakan?ya akai kika san haka?ya kuma jefo mata wata tambayar,cikin ruɗewa da san kama kanta tace"ai shi ya faɗa da bakin sa!'a wannan karon Bintu ce ta jefo mata tata tambayar da cewa to Hajja ya akayi ya faɗa miki bayan wannan abun sirrine tsakanin su su uku?cike da tashin hankali take duban Bintu ta kasa bata amsar tambayar ta,Bintu bata saurari abinda zata ce ba ta cigaba da cewa,kinga hakan yana nufin an so yi masa wani abune da zai iya cutar dashi shi kuma yaga kawai gara ya bayyana cewa bashi ne Dady ba!'wani irin kallon tashin hankali tabi Bintu dashi kana tace"yanzu me kike nufi?nice zanyi ƙoƙarin cutar dashi?da sauri Bintu ta girgiza kanta tare da cewa abun ne akwai mamaki da ɗaure kai Hajja saboda mu ba irin bayanan ki Dady jafar yayi mana ba, hasali ma munzo ne dan sanar dake abin da ke faruwa,sai kuma muka ji saɓanin abin da ya kawo mu daga bakin ki,bayan kuma kince an ɗauke Dadyn!'Bintu ta ƙarasa maganarta da tsare Hajja da idanuwan ta irin na Abdallah,wata irin zufa ce ta shiga ketowa Hajja tana kuma mamakin yadda yara ƙananu suke son mozanta ta a fakaice,gashi sunƙi bata damar gano manufar su,ganin halin da tashiga ne yasa Abdallah miƙewa tare da cewa,shike nan Hajja yanzu ina shi wan can da muka saka a madadin Dady?da sauri tace"ai yana nan zan sa akawoshi!'Bintu tace"meyasa da kikaga ba Dady bane baki barshi yay tafiyarsa ba?a yanzu kam anzo gaɓar da take neman fito da kanta, kasa bawa Bintu amsa tayi saboda bata da amsar,dan haka shuru tayi tana rarraba ido, Abdallah ya kama hanyar fita daga falon ba tare da ya kuma tankawa ba.
Suna fita taji kamar an zareta daga cikin masifa,kai yaran nan sun iya tambayoyin da zasu saka mutum ya kama kansa sai kace wasu lauyoyi ko ƴan jarida,karma yarinyar nan taji labari,hatsabibiyar yarinya kawai,gaba ɗaya dai a wannan rana nutsuwar Hajja ta ƙare ta rasama ta kaimaiman tunanin da zatayi akan wannan al'amari,bata taɓa tunanin cewa akwai ranar da zata kwaɓe mata ba,bata taɓa tsammanin asirin ta zai iya neman tonuwa ba,kuma ko a yanzun ma bata tunanin haka a ranta dole zata san mafitawa rayuwarta,
Ɗan tsayawa yayi Bintu ta ƙaraso,kallon juna sukayi Sai kawai suka saka dariya,abinda ban taɓa gani ba a fuskar Abdallah,lallai yau farin ciki yay farin ciki,A hankali Bintu ta shiga gwada yadda Hajja tayi tun shigar su falon, Abdallah kuwa Binta kawai yake da wani kasalallan kallo yana murmushin gefan baki,da dai yaga ba da katawa zatayi ba kawai sai ya ja hannun ta suka cigaba da tafiya har zuwa sashen Hajiya Babba,
Kallo take binsu dashi wanda yake nuni da tsananin ƙaunar da take musu kuma har ta kasa ɓoyuwa cikin idanun ta,rungume Bintu tayi tana shafa kanta,ita kuma kamar wata mage tayi wani luf sai faman lum-lumshe idanuwa takeyi,sun ɗan daɗe a ɓangaren Hajiya Babba daga nan sukayi mata sallama suka koma sashen inno,sai da yaje yayi Sallah ya dawo kana ya samu Abincin inno najiran shi,ita Bintu tuni ma har taci nata saboda yunwar da take ji,shima zama yayi yaci, kana ya miƙe tare da ɗan kallon inda Bintu take zaune,so yake ya ɗan fita yaje gidan da yakai su Ummi,ƙarasowa yayi inda take zaune ta ƙurawa tv Ido kamar tanaso ta ciro mutanen dake ciki,zama yayi a kusa da ita tare da ɗan taɓa ta zabura tayi cikin tura baki tace"nikam ka bani tsoro ma!'yace"fita zanyi amma bazan jima ba!'da sauri tace"ba tare zamu tafiba?girgiza mata kai yayi tare dayi mata alama da girarsa, karyar da kai tayi kamar wata sabuwar marainiya,kana tace"ayya Yah Abdallah kasan fa ko ina tare muke zuwa meyasa yanzun bazaka dani ba? kai tsaye ya bata amsa da cewa nan ba gurin zuwan matan aure bane!'zaro idanu tayi tare da cewa to ai kai ma mijin aurene nikam tsoro nakeji bazan iya zama ba!'tashi ki tafi wajen inno!'ya faɗa yana miƙewa,tashi tayi jiki a sanyaye sai murza idanu da takeyi alamun dai tana son yin kuka,tsayawa yayi tare da zuba mata ido,shifa sam bashi da wata zarra akan abinda ya shafi BINTU,shi yasa yake kokarin ganin yayi abinda zai faranta mata,itace sanadin farin cikin sa da duk wata walwala da ya tsinci kansa aciki,kamo hannun ta yayi a hankali yayi mata masauƙi cikin faffaɗan ƙirjinsa,wani abu yake ji game da ita yana daɗa tsikarar zuciyarsa,mutsu mutsun da take ne yasa shi ɗago kanta sai yaga hawaye shaɓe shaɓe kan kyakkyawar fuskar ta,bakinsa ya kai kan fuskarta ya shiga share mata hawayen da harshensa, wanda ɗumin harshen nasa ya saukar mata da wata irin kasala da mutuwar jiki, cikin wata irin murya yake cewa ke Bint kin san zafin wannan kuwa kin san raɗadin zubar wayenki kuwa?bata fahimci mai yake nufi ba dan haka sai ta shiga girgiza masa kai,ɗan ware idanun sa yayi akan ta,daga nan kuma ya samu kansa da zura harshen sa cikin bakinta,take jikin ta ya shiga karkarwa,ganin ƙafafunta na san kasa ɗaukar ta yasa ta kuma rikoshi da kyau daga nan salon ya kuma sauyawa da wani irin mayataccen sumba mai ruɗa zuciya da gangar jiki,ba ga ogan ba,baga yarinyar ogan ba,wani irin mahaukacin salo yakewa Bint din tasa wanda shi kansa baibsan daga ina ya iyasaba,nema yake ya kasa control ɗin kansa akan Bintu,duk wani ƙarfin shi ƙare wa yake a duk lokacin da ya kasance da ita,suna cikin wannan halin basu ankara ba saijin kiran sallar magriba sukayi a tsakar kansu,wanda dole ta sa su rabuwa da juna,kawar da kanta tayi saboda kunyar abin da tayi,leƙa fuskarta yayi tare da cewa my ukty, na fasa fitar bazan barki ke ɗaya ba,da sauri ta juyo da fuskarta gareshi sai caraf ta kuma tsinkayar bakinsa cikin nata,amma ba sha yake ba tsayawa yayi yana kallon cikin idanun ta da ta kasa kallon sa,a hankali ya miƙe da ita ajikin sa ya nufi hanyar bedroom ɗinsa,sai da ya shiga kana ya sake ta tare da shigewa toilet,yana fitowa yace"kiyi alwala masallaci zanje yanzu zan dawo!'kai ta ɗaga mishi kamar wata ƙadangaruwa dan bakinta da jikin ta duka amace suke da irin zazzafan kulawar Abdallah agareta.
Duk da cewa zuciyar ta ba anutse take ba hakan bai hanata son aiwatar da niyar ta ba,shirinta takeyi ta haɗa duk wani abu da zai iya zame mata arziki dan wucewa dashi,jira takeyi kawai gari ya waye ta fece,tana cikin wannan shirin kuma katsaham ta samu waya daga Alhaji Baba cewa yana buƙatar ta gobe da misalin goma a falonsa,(kasancewar Abdallah ya dawo da taron da safiya saboda wani tunani da yayi)jikin ta asanyaye ta amsa tare da ajiye wayar,ta gumi ta zabga tana tunanin abinda yasa ake hada taro rana tsaka,wata zuciyar tace mata ko dai mutuwar Umar ce ta samesu shi yasa ake son sanar da ita cikin nutsuwa, wannan tunanin da tayi ne yasa ta kwashewa da wata shegiyar dariya,wadda ita agurin ta ta cin nasara ce,yanzu hankalin ta ya kwanta sai kuma tsimayin abinda zai faru gobe.
Yana cikin filin jirgin sama na malam Aminu Kano ya samu wayar mahaifin sa,nasan kasancewar sa a gobe ƙarfe goma na safe cikin falon sa,cikin ladabi ya sanar da Alhaji Baba ai yana Kano saukar sa ke nan dan haka insha Allahu zai halarci taron,daga nan jirgin da zai kaishi Abuja ya wuce,yana sauka bai wuce ko ina ba sai gidan dasu Hajja suke,cikin girmamawa ya sanar da Hajjo cewa su shirya zai zo ya ɗauke su gobe dan zuwa estate zai gabatar dasu a wajen Alhaji Baba,
Duk wanda ya kamata yasan da wannan gagarumin taron ya sani har ma waɗan da Abdallah baicewa Alhaji Baba ya sanar dasuba, duk saida yasanar dasu ƴaƴan Hajja waɗan da suke nesa da yawa ne kawai bai ce lallai sai sunzo ba,Hajja kuwa ba ƙaramin tashin hankali ta shiga ba,babu yadda batayi da Alhaji Baba ya sanar da ita ko taron na meye,amma yaƙi cewa da ita komai, hasalima sai ya ɓoye mata cewa Abdallah ne ya haddasa taron,ganin yaki sanar da ita dalilin kawai sai ta rabu dashi dan bata son ta tsaurara bincike har ya ɗora mata ayar tambaya,waɗan da basu razana da kiran Alhaji Baba sune masu zuciziyar zinare, zuciyar da babu komai acikin ta sai Alkhairi,to Allah dai ya jiyar da mu Alkhairi a wannan zama na falon Alhaji Baba cewar da yawa daga cikin ahalin wannan estate ke nan.
A wannan rana da yawa daga cikin alhalin Alhaji Baba baccin su ragaggene daga na cikin gidan har na wajen irin su Baba nura kenan dasu Alhaji Hashir waɗan da kowa yasan da wannan taron dan duk da cewa suna garƙame amma saƙon ya tarar dasu,dan Abdallah bai bari Alhaji Baba yasan cewa ƴan uwan sa da ƴaƴan sa basa cikin gidan ba shi yayi uwa yayi makarbiya yace"zai sanar dasu,dan haka gaba ɗayansu hankalin su atashe yake, dukkanin su suna cikin halin nadama domin babu wanda ya tsammaci zuwan wannan rana agaresu, Alhaji Hashir kuka yake da idanun sa yana kaicon rayuwarsa da tsufan sa da gemun sa amma yabi ruɗin zuciya da kiɗan shaiɗan,yana matuƙar tsoro da jin kunyar haɗa ido da ɗan uwan sa,ji yake yi inama Allah zai ɗauki rayuwar sa kafin wannan rana ta jin kunya da mozanta ta waye,
Shi kuwa Dady Habib, bai san komai da yake faruwa ba, Abdallah bai bi takan sa ba,dan yasan shu'uman cin sa zai iya neman hanyar kufcewa daga garesu,tunda har yanzu baiga alamun nadama atare da shi ba,shi yasa ya rabu dashi sai agoben zaisa arufe masa idanu a shiga dashi har cikin falon Alhaji Baba,
Misalin ƙarfe takwas na safe Abdallah ya fito cikin shirin sa tsaf,sai zabga ƙamshi yake kamar wanda yayi ɓarin turare ajikin sa,Bintu dake ta sharar baccinta hankali kwance sai buɗe idanu tayi taga yana shirin fita,ai kuwa wata irin wuntsilowa tayi daga kan gadon tare da fara murza idanun ta,dan ba sai yayi mata bayani ba tasan cewa fita zaiyi ya barta,bai san ta farka ba sai takunta da yaji abayansa,tsayawa yayi tare da juyowa,kallanta ya shiga yi tun daga sama har ƙasa sanye take cikin wata ƴar figigiyar riga iya gwiwa gashinta kuwa duk yabi ya baje a kaɗarta,kana ganinta kaga wadda ta tashi daga bacci,da gira yayi mata nuni da jikinta,sai tashiga bin jikin nata da kallo amma dai ita bata ga komai ba,dan haka ta ɗago ta kalleshi da alamar tambaya,ɗan lanƙwashe kansa yayi a kafaɗarsa kana cikin taushin muryarsa yace"ba bina zakiyi ba?da sauri ta ɗaga mashi kai,yace"A hakan zaki bini me yasa yanzu bakya son zama a gida?tura ɗan bakinta tayi tare da cewa aiya nikam tsoro nakeji!'matsowa yayi gab da ita kana yace"Dady zanje na ɗauko kafin ki shirya ko kin manta da taron da muke dashi anjima?girgiza kai tayi tare da cewa to amma ka tsaya nayi wanka sai mu fita tare Ni sai na zauna wajen inno kafin ka dawo!'jan hannun ta yayi har zuwa cikin toilet ɗin kana ya shiga zare mata rigar jikin ta,duk da ƙoƙarin hanashi da tayi amma hakan ya gagara a wannan rana kuma a wannan lokaci sai da Abdallah yagane mata sirrin jikin ta, dan kuwa wanka yayi mata mai sunan wanka,tare da nan naɗota a tawul ya fito da ita,kana ya shirya ta kamar wata ƴar baby, ko da yake shi baby ce awajen sa, Bintu dai ta kasa haɗa ido da Abdallah har sa ilin da ya kaita ɗakin inno shi kuma ya juya ya bar gidan,dan zuwa ɗauko Dady Abubakar.
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
```Page 58 ```
A FALON ALHAJI BABA.
Damisalin ƙarfe goma daidai falon Alhaji Baba ya ɗauki haramar al'ummar da suke zaune a ƙarƙashin sa,ciki kuwa har da Dady Habib wanda yayi tsumu-tsumu,dan shi sam bai taɓa tsammanin zai fuskanci wannan rana ba,tunda asirin sa ya tonu bai taɓa jin wani abu mai kama da jin kunya da nadama ba sai yanzu, wannan dalilin ne yasa ya kasa haɗa ido da kowa dake zaune cikin falon,a ta ɓangaren su Alhaji Hashir da Alhaji Nasir ma kusan hakane a gurin su,da sauran ƴan tawagar su ma baki ɗaya,Bintu dake kallon su ɗaya ɗaya,duk ta fahimci abinda ke zukatansu,abinda ya so bata dariya kenan wai kunyar duniya sukeji,bata lahiraba,kunyar Alhaji Baba sukeji ba ta ubangijin su ba,kaico da irin wannan rayuwar,da babu tsoran Allah acikin ta,kallonta ta maida kan Anty Nafisa wanda tana kallonta ta fuskanci tana farin ciki acan cikin ƙasan zuciyar ta,yayin da kuma azahirinta fuskar ke ɗauke da alhinin abinda take tsumayin ji cikin kunnuwanta, rashin ganin Umar shi ya kuma tabbatar mata da abinda take fata ne yake son tabbata,falon yayi tsit baka jin ƙarar komai sai ta na'urar sanyaya ɗaki da kuma fankokin dake kaɗawa,sai fitar numfashin waɗan da suke da nutsuwar yin sa.
Gyaran muryar da Alhaji Baba yayi yana tafe ne da bugawar zuciyar wasu da kuma samun nutsuwar wasu,A hankali ya fara gabatar da addu'a cikin tsananin nutsuwar sa da kamalarsa,bayan shafa addu'oin ne ya kuma gyara zaman sa tare da maida hankalinsa kan Abdallah kana yace"to Alhamdulillah Abdallah na cika maka alƙawarin ka kamar yadda nayi maka gashi nan na tara maka duk al'ummar dake cikin ESTATE ɗin nan,dan haka yanzu