Showing 99001 words to 102000 words out of 184937 words

Chapter 34 - KUDURAR ALLAH COMPLETE BY FATIMA Y ADAM

21 Jul 2024

16878

ce mata maza kiyi addu'a,amma ina tuni ai Bintu ta sume masa saboda tsananin razana da tayi da wannan al'amarin,ɗaukar ta yayi cak tare da fita daga ɓangaren,yana ƙoƙarin saka Bintu a mota yaji muryar Dady Mansur yana cewa kai kam ka zama wahalalle kai kenan ɗaukar mace"a bainar jama'a,to ai ba sai ka nuna mana Kai ɗin dan zamani bane, tuni mun riga mun sani dan duk wasu alamu sun nuna atare da kai!'tsayawa Abdallah yayi tare da zubawa fuskar Dady Mansur ido,yayin da tunanika sukabi suka da baibaye zuciyar sa tare da zargi mai ƙarfi akan Mansur ɗin,me yasa yake yawan ganin sa ta wannan ɓangaren ne?me yake yi a wajen?meye kuma haɗinsa da wajen?meye ne kake kallo na haka kamar zaka cinye Ni Ni dai na fi ƙarfin duka a wajenka babu yadda zakayi dani,Tom kuma ina mai sanar da kai idan har dasa hannun ka cikin ɓatan ɗana to kayi gaggawar sakar min shi idan ba haka ba duk abinda ya faru kayi kuka da kanka!'yana gama faɗar maganar sa yayi ciki tamkar zai tashi sama,saboda fushi da kuma sauri.


A hankali Abdallah ya saka Bintu cikin motar, yana shirin shiga sai ga Anty Nafisa cikin sauri ta ƙara sa gaban sa tana cewa kamar Bintu na gani anan? me yasame ta?daƙyar kamar mai ciwon baki yace da ita,ta ɗan tsorata ne,shine ta suma!'da sauri Anty Nafisa tace"to ai ba sai an kaita asibiti ba ko ruwa aka zuba mata ya wadatar!'yahya ne yayi saurin miƙa masa gorar ruwa saboda alamar da yayi masa,ɗan zura kansa yayi ya yayyafa mata ruwan,bata wani jima ba kuwa ta sauke wata doguwar ajiyar zuciya sai dai amma a tsorace take,ganin haka yasa shi shiga cikin motar tare da tallafo kanta saman cinyar sa,shafa kanta ya shigayi A hankali, tare da ɗan hura mata iska saman fuskar ta,buɗe idanunta da suke rufe tayi,ta zubasu kan kyakkyawar fuskar sa,sai kuma ta ɗan maida su ta lumshe saboda yadda wasu maganaɗisu ke fitowa daga cikin idanun nasa suna shigewa cikin nata idan.

Anty Nafisa kuwa tana daga waje tana kallon sarautar Allah,ko tace wata iriyar ƙauna,wadda bata taɓa ji ko gani ba A tarihin rayuwar ta,ga kuma mamakin daya rufeta wai dama wannan muskilin mutumin zai iya tarairayar mace irin haka?to gashi dai ta gani da idanunta ba wai labari aka bata ba, duk da ta fahimci kamar Abdallah bai san da wannan zazzafar ƙauna da yake yiwa Bintu ba,fitowar Abdallah da Bintu ne ya katse mata tunani,bin su ta kuma yi da wani kallo saboda yadda taga Bintu tana wani narkewa Abdallah,shi kuma sai wani rirriƙeta yake duk da fuskar sa A haɗe take amma hakan bai hana damuwar halin da Bintu take ciki baiyana asaman fuskar tasa ba,ganin yana ƙoƙarin wucewa da Bintun part ɗin inno yasa tayi saurin ɗan matsawa kusa dasu tare da cewa,i can help her,ta faɗa tana duban Abdallah sama-sama batare da ta iya haɗa ido dashi ba,ci gaba yayi da tafiya batare daya kulata ba,ganin haka yasa Bintu ɗan dakatawa tare da duban sa tace"ka tafi kawai zamu ƙarasa da Anty Nafisa!'wani irin kallon yake mata wanda har saida ta kasa jurewa ta shige cikin jikin sa,ƙasa-ƙasa cikin miskilar maganar sa yace"kin tabbatar zaki iya babu wata matsala?ɗaga kanta tayi tana mai zamewa daga jikin sa,sakin ta yayi kana ya ɗanja da baya batare da ya ɗauke idonsa akanta ba,Anty Nafisa datayi mutuwar tsaye daƙyar ta iya ɗaga kafafunta tare da kama hannun Bintu suka fara tafiya dan shiga falon inno, Anty Nafisa ta shiga tsananin mamaki da irin wannan soyayyar da ta hango cikin idanun Abdallah da Bintu,anya kuwa soyayya zata bari Bintu tayi mata abun da ya dace akan wannan al'amari?to amma dai bazatayi saurin karaya ba tunda wannan tunanin tane ba tunanin Bintu ba,da haka suka dan gana har zuwa cikin ɗakin Bintu batare da kowa ya gansu ba saboda basu tarar da kowa A falon ba, inno tana sashen Alhaji Baba ita kuma Taufiƙa sun ƙule cikin ɗaki tana nemarwa kanta mafita,shi yasa suka shigo ba tare da kowa ya gan suba.



Suna shiga ɗakin Anty Nafisa ta maida ƙofar tare dasa mata key,zama tayi gefan Bintun wadda ta shiga duniyar tunani, gaba ɗaya tunaninta yana kan wannan ɗakin itafa tasha alwashi ko zata rasa rayuwarta sai tagano sirrin ɗakin nan, wannan abin da akayi mata ba komai bane ba kuma ba zai sa taji ta karaya ba,ji tayi ma tamkar an zaburar da ita akan al'amarin,dafata Anty Nafisa tayi tare da cewa Bintu wai mai yafarune? tun ɗazu nake jiranki ganin bakizo bane yasa na biyo bayanki!'Buntu tace"ba wani abu bane ba fa Anty, A hanyar zuwa wajenki ne fa na ɗan samu tsautsayi,sauri tayi ta kawar da zan cen da cewa Anty Nafisa me yake faruwa ne kike nemana haka da gaggawa?take fuskarta ta sauya saboda motsuwar abinda yake ranta,cikin kama hannun Bintun tace"haƙiƙa ina cikin tashin hankali mara adadi,a hankali ta shiga zaiyanawa Bintu duk abinda ya faru ta ɗora da cewa,tashin hankali na bai wuce yadda zanyi nasan abinda Umar yake shiryawa ba,ban san me yake nufi da mallakawa, gaibu dukiyar sa ba,na shiga matuƙar ruɗani tare da duhun da naka sa ganin haske ko yaya yake!'tun da Bintu ta fahimci inda labarin Anty Nafisa ya dosa ta manta inda take saboda ruɗewa da tunani,me yake shirin faruwa ne?ba dai mijin Anty Nafisa shine mahaifin ta ba?wata irin zufa ce ta shiga keto mata,yayin da ƙwaƙwalwarta ta cigaba da yin zagaye tana auna abinda sa hannun yake nufi da labarin rayuwar ta,da kuma sunan mahaifinta da fafi ya gaya mata cikin labarinta wanda duk ta mantasu Abaya sai yanzu komai yake dawowa cikin ƙwaƙwalwar ta,ga sunan da ta ambata yayi dai dai da sunan da mutumin nan ya ambata, hakan yana nuni kenan mijin Anty Nafisa ita ya mallakawa dukiyar sa?to yasan da ita ne?kuma waya bashi labarin an haifeta,?tunanin tane ya kai kan matar Baffan ta fafi da mahaifiyar su,to ko mahaifinta ya same su dan ta hanyar sune kaɗai zai iya samun labari akan su ta hanyar sune ka ɗai zai san cewa Laila ta haifa masa ɗaya mace,to hakan yana nuni da cewa suna raye?idan suna raye to suna ina?Bintu fa ta ruɗe lallai tana buƙatar waɗan nan amsoshin a kusa,to amma ai zata iya samun wasu amsoshin wajen Anty Nafisa duk da tasan baza ta gaya mata ko mai ba,amma tabbas tana da yakinin Aunty Nafisa tasan wani abu akan mahaifiyar ta Laila,idan ba haka ba me yasa ta tashi hankalinta, saboda sa hannun?wata zuciyar tace Bintu ki nutsu kar Nafisa ta ganoki dan agurinta zaki samu,rabin amsoshin ki dan kuwa tasan abinda ke baki sani ba wanda kuma zai iya kasancewa wani ɓoyayyen sirri da batason kowa yasani,tabbas dole kiyi ƙoƙarin binciko wannan sirri, Anty Nafisa ta zaman miki tsanin hawa wanda zaki taka dan cimma kyakkyawar manufarki, da wannan tunanin ta juyo tana daɗa fuskantar Anty Nafisa wadda ta zuba mata ido ba tare da ta katse mata tunani ba dan atunanin ta ita take lalubowa mafita, ɗan numfasawa Bintu tayi tare da cewa"gaskiya wannan al'amari yana buƙatar dogon nazari!'cikin yanayin damuwa tace"haba Bintu Ni da nake ta sauri dan zuwa gareki ki bani shawara amma sai kice sai Anja lokaci,idan wani can shawarar baibgagareki ba me yasa wannan zai gagareki?kai tsaye Bintu tace"saboda ban san makamar zaren ba,bani na fara labarin ba dan haka ƙarƙareshi zaiyi min wuya!'cikin tashin hankali Anty Nafisa tace"me kike nufi Bintu?kai tsaye ta kuma cewa ban san ko mai akan batun yarinyar da aka mallakawa dukiya ba,ballantana nabaki shawarar yadda zaki ƙwaci dukiyar da A kasa hannu domin shaidar ta zama tata!'

Wani irin gumi ne mai tafe da wani irin yaji ya shiga sauko mata tako ina,gaba ɗaya miyan bakinta ya ƙafe har wani ɗaci-ɗaci take ji saman harshen ta,hannu tasa ta ɗan share gumin kan goshin ta,kana cikin sarkewar da harshen ta yayi tace"yanzu kina nufin in dai zaki warware min wannan matsalar sai na gaya miki wani abu daya dan ganci yarinyar?jinjina kanta Bintu tayi cikin bata tabbaci,Anty Nafisa ta kuma cewa to idan kuma ban san komai ba fa?wani irin kallo Bintu ta wurga mata a fakaice,kana tace"ai nasan ba zai yiwu ace baki sani ba,kinga fa Anty Nafisa Ni taimakon ki nake yi kuma ina nema miki hanyar da zaki samu abinda kike nema batare da kinsha wahala ba,idan kina ganin wannan ba hurumi na bane babu wata damuwa sai mu canja shawara!'ta faɗa tana mai fargabar kar ta ɗauki maganarta ta ƙarshe,ai kuwa cikin sauri Anty Nafisa tace"gaskiya Bintu gwara mu canja shawara,saboda Ni kaina ban san komai game da wannan al'amari ba,kawai ki taimaka ki kawo shawarar yadda zan ɓullawa Umar ya faɗa min wani abu da yake ɓoyemin!'Bintu dai ba dan ranta ya soba Amma tasan a sannu zata samu abinda take so gurin Anty Nafisa,kuma ko ba komai itama samun bayanai daga wajen Abba Umar ɗin zaiyi mata amfani,dan haka cikin nutsuwa tace"shike nan amma ki ɗan bani nan da zuwa gobe,gaggawa bazai mana amfani ba a wannan gaɓar amma kiyi haƙuri zuwa goben idan Allah ya kaimu!'Anty Nafisa dai ba dan ranta yaso ba haka ta haƙura...


Tana fita Bintu ta ƙwatar da kanta jikin gadonta tare da lumshe idanun ta,tana mai tasbihi ga Ubangiji tare da ƙara gine masa akan baiwa da Ni imar da yayi mata,ita da kanta tana mamaki idan ta duba taga yadda take juya rayuwar Anty Nafisa,duk da ba ason ranta ba,amma Allah mai ƙudura ya ɗora mata shakkar Bintu tare da bin duk abinda ta faɗa mata cikin hikimar sa tasan fidda gaskiyar mai gaskiya,gashi dai yabata ƙwaƙwalwa da tunanin abinda ta tsarawa Nafisan kuma har hakan ya zamo mata alheri,tunda gashi ta sanadin shawarar da tabawa Anty Nafisa ta san abubuwa da yawa wanda su yakamata tasani tuntuni amma bata sani ba saboda wani abu da Ubangiji ya ɓoye wanda babu wanda yasan shi sai shi mai kowa da komai,sai kuma wani irin farin ciki da ya mamayeta saboda kasan cewar ta samu mahaifin ta a raye, kuma wanda ya kasance kamili cikin wannan har gitsatstsen family mai abubuwan al ajabi iri da kala.


A hankali Hajjah ta ɗora hannun ta saman kan ɗan nata, tare da cewa Habibu me yake damun kane? tun ɗazu kazo ka sanyani gaba da tagumi idan da wata matsala ba sai ka faɗa min ba!'ta ƙare maganar cikin yanayin damuwa da da muwar ɗan nata,ɗagowa yayi kana yace"wallahi Hajjah ba komaine yake damu na ba sai lamarin Yaya Mansur,na rasa me yasa idan zaiyi abu baya tunanin mai zai je ya dawo?cikin san jin abinda ya aikata Hajjah tace"me kuma yayi sababben?cikin jin takaicin abun yace"zuwa yayi har sashen Baffa Hashir ya ci masa mutumci wai yasan sune suka ɗauke masa Sayyid, to maza suyi gaggawar fito masa da ɗan sa ko ya ɗauki matakin da bazai yiwa kowa daɗi ba!'ya ƙarasa maganar yana ɗan huro iska ta bakinsa,shuru Hajjah tayi saboda tsabar takaicin halin ɗan nata,Dady Habib ne ya kuma cewa Ni abinda ya bani mamaki ma bai wuce yadda ya ɗorawa ɗan uwan mahaifin namu sharrin satar mutum ba,ko ta ina hakan zata faru?kuma duk yara sa wanda zai ɗauka sai Saiyyid ɗan Mansur mutumin da kusan shine ya raineshi da hannun sa,Hajjah da sai yanzu ta iya furta wani abu tace"anya kuwa Mansur baya shaye-shaye?idan kuwa har baya shan komai to tabbas yana da taɓin hankali,saboda abin nasa ya wuce makaɗi da rawa,kuma wan nan magana har gaban Alhaji dan wannan hauka ne da rashin kamun kai!'Dady Habib yace"nima abinda nayi tunani ke nan shi yasa na fara sanar dake dan kar yaje yayi abinda zai ɓata musu zumunci!'hakane Habibu Allah yayi maka albarka ya kuma shiryaku baki ɗaya kai da ƴan uwanka,da Amin ya amsa cikin jin daɗin addu'ar mahaifiyar tasa.


Kallon ta take ta cikin miƙab ɗin dake sanye a fuskar ta,kallon da take mata kallone na tsana da ƙyashi, da kuma uwa uba baƙin cikin da take son yi mata na toshe mata hanyar samun burinta,tunda taƙi gaya mata inda Abubakar yake wanda ita kuma tayi yaƙinin cewa Laila tasan inda Abubakar yake kawai dai taurin kaine ya hanata faɗa mata,wanda tasan a ƴan kwanakin nan zata sauke mata shi,sunkuya wa tayi ta danƙi gashin kan lailan tare da cewa zaki iya gaya min ko har yanzu baki shirya ba?karfa ki manta kece kika dawo dani kan hanyar da da na kauce mata,wanda dama shine sanadin satoku daga wan can gurin amma sai wani dalilin ya sha kaina na sauka daga kan hanyar da nake da farko, amma sai gashi cikin tabbatuwar samun nasara ta sai ya zamana ke ɗin ke kika dawo da tunani na,to amma me yasa bazaki yi min abinda nake so ba?nace miki in dai kika gayamin suwaye mutanen dasuka ɓoyeku da kuma inda suka ɓoye Abubakar,to nayi miki alƙawarin zan kula da rayuwar Bintu ba zan bari wani abu ya cutar da ita ba!'tana direwa Laila ta ɗauka da cewa ke baki isa ki kare rayuwar wasu ba,tun da kema baki iya kare taki ba,kuma Bintu bata buƙatar kariyar wani bawa kariyar ubangiji take buƙata kuma ta riga tasamu,dan haka sai ki bi wani sarkin Bintu ta riga tafi ƙarfin shu'umancin ku gaba ɗayan ku macuta azzalumai insha Allah ƙarshen ku yana nan zuwa,Ni na gaya miki sai kun to zarta ke da duk wani mai kwatankwacin irin mugun halinki!'kafin ta gama rufe bakin ta matar ta ɗauke ta da wani mahaukacin mari,tana wani irin huci kana tace" ki kiyayeni Ni ba A faɗa ina faɗa,sai kinyi nadamar waɗan nan kalaman naki,dani kike zancen,daga haka ta fita daga ɗakin tamkar kububuwa,tana mai jin baƙin cikin yadda takasa samun abin da takeso,duk faɗi tashin da tayi kuma take kan yi,ko a iya binciken neman Abubakar ta tsaya ya isa a jinjinawa namijin ƙoƙarin da tayi,saboda ita farko neman ABUBAKAR takeyi amma sai tayi kacibus da su Laila,wanda sam da farko batayi niyar ɗauke su ba,amma sai ta canja shawara ta yaudaresu da nufin taimakon su zatayi sai da suka bata labarin su kaf ba tare da sun ɓoye mata komai ba,tun alokacin ta so su gaya mata ko waye ya ɓoye su sai kuma tayi rashin sa a suka gano nufinta,shine dalilin da yasa ta kwashe su gaba ɗaya ta killace da nufin zata iya gane ko waye ta hanyar neman su Lailan da zaiyi,amma sai taji shiru wanda hakan ne ya kuma tabbatar mata da cewa wannan mutumin baƙaramin shu'umi bane,saboda ya kulle duk wata hanya da zata sa agane shi, wannan shine dalilin da yasa tasan tarihin Laila da fafi kuma shine dalilin da yasa take faman ajiye dasu tsawon shekaru,gane Bintun bai yi mata wahala ba tunda tayi binciken ta yadda ya kamata,to kuma sai gashi itama Bintun tana yaƙin neman mahaifiyar ta,abu ɗaya ne yasa ta rabu da Bintu shine tana so ta gano musu wannan mutumin,da zarar tasame shi ita kuma lokacin zata samu kyakkyawar dama akan su su duka,dole tana buƙatar sanin waye wannan mutumin saboda shi kaɗai ne yake da fawar riga ta samun abinda take nema kuma tana ganin kamar Abubakar yana hannun sa,shi yasa take da tabbacin su Laila sun san inda yake tunda sun zauna tare da mutumin,duk da cewa ita bata yar da da wani zuwa wajen boka ba tafi yadda da kaifin basirar ta to amma alokacin sai da ta dangana da wani hatsabbin boka wanda shine ya bata tabbacin anan aka ɓoye Abubakar sai kuma gashi a maimakon ta samu Abubakar sai ta samu su Laila,wan nan abin shi yake matuƙar ci mata rai, kuma tana da tabbacin sun sani amma shegen taurin kansu ya hana su faɗa mata gaskiya,amma babu komai tunda ta haifi ɗiyar da zata nuna mata komai, batare da tasha wahalar da tasha a baya ba,



Tun da ya shiga office ɗin bai huta ba,saboda aiyukan da ya tarar,sai dai lokaci lokaci tana yawan faɗo masa a rai,da tunanin ko ya take?ko wane hali take ciki yasan ta da shegen tsoro,shi yasa duk yake jin damuwa aransa,yana fatan dai Allah yasa bata cikin firgici, wayar dake salular dake cikin office ɗin ce tayi ringin ɗaga wa yayi tare da amsawa da ok ya ƙara so!'ajiyewa yayi tare da cigaba da duba wasu manyan fayal dake gaban sa,sallama akayi tare da turo ƙofar officce ɗin, Abdallah ya amsa sallamar yana mai ƙurawa mutumin da yashigo idanu dan san tuna inda yasan shi,har mutumin ya zauna Abdallah bai ɗauke idanun sa daga kansa ba,cikin tsuke fuska Abdallah yace"me ya kawoka officce ɗina? ƙoƙarin tashi yake ya bar officce ɗin saboda fes ya tuna fuskar mutumin idan bai manta ba wannan mutumin yana daga cikin tawagar su Alhaji Nasir,to me yake nufi da zuwa har cikin officce ɗin sa?Alhaji Rufa'i kamar yasan tambayar dake zuciyar Abdallah yace"Abdallah ka tsaya ka saurare Ni a kwai tarin manufofi da kuma ma ana da muhimmanci cikin wannan ziyarar tawa, wanda banyi wannan ziyarar kai tsaye ba har sai da na nemi izinin Dadyn ka jafar!'tabbas kuwa Abdallah sauraran Rufa i Abune mai matukar mahimmanci,dan haka ina baka umarni daka tsaya ka saurari abinda yazo dashi!'Dady jafar ne yake wannan furucin a yayin da yake sako kansa cikin Officce ɗin na Abdallah,zama yayi ba tare da yayiwa Dadyn nasa musu ba sai dai zuciyar sa cike take da mamakin yadda akayi zai samu wani abu mai muhimmanci daga bakin ɗaya daga cikin abokan gabarsa, wanda shi dai baya raba ɗayan biyu cewa yaudara ce,amma dai bari ya saurare shi ɗan yaji shi kuma da wace irin al mara yazo ko kuma tatsuniya...


Tuna sarwa Alhaji Rufa'i shine babban yaron Alhaji Baba dake kula da kasuwan cin sa na Kano,kuma shike auren daya daga cikin ƴaƴan Alhaji Baba wato sakina,kuma ɗaya daga cikin ƴan kungiyar su Alhaji Nasir,

To gashi dai yayi tattaki yazo har inda Abdallah yake, kome yakawo shi? Wannan duk sai mun haɗu cikin nest page....

Fatima y Adam✍🏽
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login