Showing 30001 words to 33000 words out of 184937 words
faɗa ba.
Cikin rikecewar da kaifafan idanunsa masu tsananin maiƙo da sheƙi suka sakata,cikin yanayin fargaba da matsanancin tsoro da ya saukar mata A lokaci ɗaya, cikin sanɗa ta taka dan tsira daga waɗan nan shu'uman idanuwan nasa da suke neman kassara duk wata gaɓar da ke gudanar da jini A cikin jikinta,
Wata tsadaddiyar murya taji tamkar amsa sarewa acikin kunnuwanta,wadda ta saka gaba ɗaya ragowar kuzarin dake tare da ita ya ƙarasa malalewa,cak ta tsaya A inda take batare da ta ƙara wani ƙwaƙwƙwaran motsi ba, cikin yanayin maganarsa na fitar da magana ɗai ɗaya tamkar wanda akasashi yi dole,yace"karki sake ganina ki tsorata,numfashinta bai gama dai dai tuwa ba ya kuma rigirgizo mata tambayar da ta motsa ƴan hanjin cikinta, tare da wata iriyar juyowa sosai tana fuskantar sa, yayin da idanuwan nan suka kuma fitowa cikin firgici da tsoro,sai da ya gama karantar yanayin ta tsaf kana ya kuma mai maita mata tambayar,yace" dake nake jiya misalin ƙarfe biyu me ya fita dake waje har kina neman fasawa mutane kunnuwa da shegen ƙaranki,me kikeso kishiga kiyi A wannan ɗakin? hantar cikinta ya kuma kaɗawa, to ma wai miyene na jin tsoron bayan nasan ban yi komai ba,wata ƙila ma shine yake wani mugun abun A cikin ɗakin, idan ba haka ba me yasa da yaji ihun nawa baizo ya tai makeni ba?kuma ya akai yasan na fita? kai wannan mutumin A kwai baƙin mugu!' gigitacciyar tsawar da ya buga mata ne yasa ta dawo haiyacinta,ya nunata da yatsa yana cewa duk ranar da na tabbatar da rashin gaskiyar ki to ki tabbatar da cewa sai nayi gutsi-gutsi da namanki A cikin gidan nan,wuce ki fitamin A falo!tun kan ma ya gama rufe bakinsa ta arta da wani shegen gudu,bata tsaya A ko'ina ba sai tsakiyar gadonta tana maida numfashi me cike da razanar da tayi da Abdallah, Allah kafitar dani daga cikin wannan gida na mutane marasa tsoron ka, kowa munafiki ne A wannan gidan, duk basu da gaskiya, duba Irin kallon da wannan Ammin Rahiman takeyi min dagani itama so take tasani wani mugun aikin!'
Ammi ta dubi Rahima tace" auta ina ƙawarki kuwa zahra?Rahima ta saki dariya tare da miƙewa zaune tana cewa" wai ta gidan inno? ni wallahi ma banje ba tun washegarin da Aka kai Amare, faɗa mukayi da inno! ta ƙarasa maganar tare da ɗan turo baki, Ammi tace"to ai ba da ƙawar taki kukai faɗa ba ya kamata dai ki dinga zuwa kina ɗebe mata kewa!'to Ammi amma sai na huta sosai zan koma zuwa!' Ammi tayi murmushi kawai A ranta tanajin haɗa kusanci tsakanin Rahima da Zahra shine kawai hanyar da zata 'iya bi dan fahimtar abinda take so ta sani A game da Zahra,tasan ko bata tambayi Rahima ba zata dinga bata labarin Zahra,ita kuma zata dinga hankalta da inda yarinyar ta sa gaba idan A kwai wani Abu maka mancin na rashin gaskiya zata sani.
Duk tsarin da Hajiya ladidi tayi shine ya kasan ce, sau biyu ne tasa Alhaji munir ya kira Alhaji Baba,ba tare da wani shan wahala ba tsarinta ya tafi yadda take so koma fiye da haka tunda A cikin kwana biyu Alhaji Baba yaji san sha'awar ya mallaka wa Bintu waya,ko dan sudinga gaisawa da bawan Allah Alhaji munir, tabbas yana jin daɗin yadda Alhaji munir ɗin yake nuna kulawarsa A kan ƴar marainiyar Allah Bintu,shi yasa yaji A ransa gwara ya bata waya dan shi Alhaji munir ɗin yasamu damar kiranta kai tsaye,
Alhaji Baba da kansa ya kira Alhajin Nafisa, yasanar dashi ya bawa Bintu waya kuma layin da yaƙi rasa dashi shine layin Bintun, dan haka zai'iya kiranta kai tsaye, godiya Alhajin Nafisa yayi masa kana sukayi sallama, A lokacin suna tare da Hajiya ladidi ya kuma sanar da ita yadda sukayi da Alhaji Baba,yadda Hajiya ladidi ta nuna farin cikinta,har saida ya tsaya yana dubanta cike da mamaki,ganin haka yasa ta waske tare da cewa, kai masha Allah gaskiya Alhaji Baba ya kyauta,tare da ɗaukar wayarta ta bar falon.
Ita dai Bintu kawai ganin inno tayi da ƙaramar waya ta bata,duban inno tayi tace"inno wannan wayar fa ta waye?inno tace nakine Alhaji ne ya baki saboda kurinƙa gaisawa da Alhajin Nafisa!'to inno kiyi masa godiya, yanzu zan ƙarasa aiki sai naje nayi masa godiya nima!'inno tace"aiko yace" karki sake kije da niyar yi masa godiya,yace kiyi masa addu'a kawai ita yake buƙata!'cikin sanyin jiki Bintu tace"inno ai addu'a tsakanina daku ba mai yanke wa bace, Allah Ubangiji yaja kwana me amfani!'inno ta amsa da Amin Batula,kana ta juya ta fita daga kiching ɗin.
Tunda inno ta fita ta kasa ci gaba da aiyukan ta, gaba ɗaya ji takeyi mutanen nan suna ɗaureta, wai yaya ita da take neman hanyar tserewa suke ƙara yi mata da baibayi da zaman gidan,anya kuwa zata iya ci gaba da zama A gidan tana cin karo da shaiɗanun mutane da kuma Aljanu?
Lokacin da Anty Nafisa ta shigo falon inno bata tarar da kowa ba,dan haka kai tsaye kiching tanufa, dan anan takesa ran ganin Bintu, cikin Sa'a kuwa tana shiga ta sameta tana kan tunanin mafita wa matsalar datake ta tun karo rayuwar ta,
Tana ganin Anty Nafisa jikinta ya fara rawa, cikin sauri ta durƙusa ƙasa dan gaidata, batare da ta amsa ba ta ɗora mata da tambayar, ina inno? Bintu tace"ta tafi wajen Hajiya Babba,zata dubata da jiki!'saurin kamo Hannun Bintu tayi sukayi can cikin kiching ɗin,hannu ta mikawa Bintu tare da cewa ina wayar da inno ta baki?cikin sauri tace gata can, tanayi mata nuni da kan prezer,da sauri Anty Nafisa ta ɗauki wayar tare da buɗe ta tasaka mata wani layin A ciki, kana tasata A babiratin, sai da ta gama sannan ta dubi Bintu tace"ki kula da kyau, baki wayar nan yana daga cikin shirin mu dan haka ki kula da'ita tamkar yadda zaki kula da rayuwar ki,kuma duk wani shiri da kike na guduwa muna sane da hakan,zaro manyan idanunta tayi wanda idan tayi hakan baƙaramin kyau yake ƙara mata ba, Anty Nafisa tayi murmushin mugunta,kana tace" kina mamaki ko? to inaso kisani duk yadda kika zacemu mun wuce haka, mun zarta tunanin babban kaima barantana wannan ƙaramin kan naki, inaso kuma ki dinga sarrafa wannan shegen tsoron naki dan watarana zai iya hhhh gaiyato mana matsala cikin aikin mu, inaso kuma ki iya bakin ki A cikin gidan nan dan duk wanda kika gani ba Abin yadda bane ESTATE ƊIN ALHAJI BALARABE YA WUCE TUNANIN MAI TUNANI munanan munajira muga yadda ƘUDURAR ALLAH zata tarwatsa mugayen zukata da ɓara gurbin IYALEN ALHAJI BALARABE dan nasan namu ba komai bane shiyasa bana tunanin yin na dama akan abinda nake aikatawa ko kuma nace na aikata,A da har na fara karaya, na fara tunanin makomata sai Hajiyata ta nusar dani tare da ɗorani bisa hanya mai ɓullewa.
Babu abinda zuciyar Bintu take sai wani irin bugu mai tsanani, Anty Nafisa idon ta ya rufe ko lura da yadda yanayin Bintu ya koma batayi ba,dan tana gama zantukanta ta juya ta fita da sauri tabar kiching ɗin,yayin da ta bar Bintu tamkar butun butumi A daskare, tuni ƙwaƙwalwar ta tafi hutun wuccin gadi,ji tayi an jijjigata da ƙarfi,wata Irin ƙaƙƙarfar ajiyar zuciya tayi tare da fashewa da wani kiɗimam man kuka mai razanar da zuciyar mai imani, dije ta zuba mata ido cike da mamakin meye yasa ta kuka kuma? ko dai irin matsalar su ɗaya? tabbas ta daɗe A laɓe tanajin Anty Nafisa sai dai bataji komai ba, tunda bata daɗe da shigowa ba Nafisan tafita,tsoron irin kukan da Bintun takeyi shiya kama dije,tsoron biyune ya haɗe mata na farko kukan Bintu wanda har yi take kamar zata shiɗe, na biyu tsoron kar A zo akamata ace ita tayiwa Bintun wani abu, wannan tunani da tayine yasa tayi saurin juyawa zatabar kiching ɗin, Amma kuma sai taji ta kasa wani irin tausayin yarinyar ne ya dinga kewayawa har cikin ɓargonta wasu zafafan hawaye ne suka shiga zubo mata, cikin sauri ta durƙusa inda Bintu take ta kama hannun ta tare da miƙar da ita tsaye,A hankali ta jawota jikinta ta shiga bub buga bayanta tana shafa kanta tana bata baki cikin taushin murya,tace" haba ɗiyata ko mai yayi zafi fa maganin shi Allah kiyi haƙuri ki daina kukan nan kowa kika ganshi yana da matsalarsa, wannan kukan da kikeyi ai sai ya cutar dake ki dena ki miƙa dukkan lamuranki ga Allah shine zai yaye miki kinji!'Bintu da yanzu ta riga tayi shiru sai ajiyar zuciyar da take fitarwa ajejjere,sai da dije ta tabbatar Bintu ta samu nutsuwa kana ta janye ta daga jikinta tace maza jeki ɗaki ki wanke fuskar ki kar inno tazo ta ganki A haka baza taji daɗi ba!'A hankali Bintu ta fara takawa sai da ta kusan barin kiching ɗin kana ta juyo cikin muryar ta da ta dashe tace" mama na gode Allah ya biya ki dukkanin buƙatunki na Alkhairi ya kareki daga sharrin maƙiya!' da sauri ta ƙarasa fita daga kiching ɗin saboda wani kukan dayake ƙoƙarin kufce mata,
Da ido dije ta bita tana ta nanata faɗin Amin akan harshen ta,haƙiƙa idan tace bata ji daɗin addu'ar da Bintu tayi mata ba tabbas tayi ƙarya, itama fita tayi jikinta A sanyaye, zuciyar ta kuma cike da tunanika iri-iri.
Tana shiga ɗakin ta waɗa kan gadon tare da kecewa da wani sabon kukan, zuciyar ta cike take da ƙunci wanda bata san ranar gushe war sa ba,yau tayi da tasanin zuwa garin Abuja,
Ashe dama wannan baƙin ahlin shine ahlina da fafi yake gayamin?tabbas iya abubuwan da na gani kawai sun isa tabbatar min da abinda fafina yake gayamin, yanzu wannan bawan Allah Alhaji Baba shine kakana? to wacece kakata kuma? wane ne mahaina?ya Allah hhhh kafitar dani duhu ka kawo min ɗauki, to ita Anty Nafisa wacece"?kuma matar waye?me yaya Abdallah yayi musu suke san cutar dashi?shi ɗan waye ne? wacece mamansa?ɗakin nan mallaki waye menene A cikinsa?shin me dame ake shiryawa da waye da waye masu shiryawar ?su waye suke neman halakani?suwaye suka ɗauke min mamana da fafina?ya Allah ka kawo min agaji, yanzu ta ina zan fara fuskantar wannan gagarumin yaƙin, fafi abin ya wuce zaton ka bazan iya ba bansan ta ina zan fara ba.
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
```Page 16 ```
Hhhh sautin dariyar sa kawai kakeji amma baza kataɓa gane waye ba saboda yadda ya juya bayansa,waya ce kange A kunnen sa,ya kuma gyara zaman wayar yayi A kunnen sa,kana cikin wata murya me ƙarfi da wani irin sauti,yace"da kyau ɗan kaka aikin ka yanayin kyau,inaso kaci gaba da ɗora mun ladidi A kan hanya ita kuma tana ɗora mana yarinyar A saiti yadda zan samu biyan buƙatata batare da tasan mai nake shirya wa ba,kar kasake kayi abinda zata gane shirin mu A kanta!'
Daga ɗaya ɓangaren, na kaka yace"ranka ya daɗe Hajiya ladidi baza taba gane dawa take aiki ba, saboda duk wata hanya na tosheta A binda kawai nasan tasani shine tana aiki da ɗaya daga cikin ahlin ALHAJI BALARABE, amma baza ta taɓa gane da waye ba in dai ba gaya mata A kayi ba, kuma ina da tabbacin babu yadda za'ayi ta sani dan mun toshe hanyar, kaga mun jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya saboda mun haɗa kifayen mu A guri ɗaya, ba ƙaramar nasara nake ganowa A tafiyar nan ba,
Ogan nasa ya sheƙe da wata muguwar dariya kana yace"naga fa kifayen nan suna da matuƙar wayo yaƙin suka fito da gaske, sai dai kuma ta yaro kyau take bata ƙarko basu san suna tun karar masifa da kansu bane, mutuwarsu suke kira, dan dazarar munci moriyar ganga zamu yada gauranta,ƙit ya yanke wayar tare da cire layin ya taune,cikin alfahari da kansa da yadda yake wasa da ƙwaƙwalwar mutane yace"shi yaƙi ɗan zanba ne idan baka iyashi ba zai kife da kai.
A hankali ta tura ƙofar falon saida ta tabbatar baya ciki kana ta shiga, kimtsa falon ta farayi kamar yadda ta saba, sai da ta tabbatar da komai yayi daidai kana ta faɗa bedroom ɗinsa saida ta gama wanke toilet ta gyara ɗakin, tana cikin sharewa taji wani zumm zumm A ƙugunta,zabura tayi dan sam ta manta da wata waya A jikinta,cikin sauri ta ciro wayar ta danna ok A lokaci ɗaya tana ɗorawa A kunnen ta, muryar Hajiya ladidi ta doki kunnenta, cikin rawar murya tace" Hajiya ina kwana!'ta can ɓangaren cikin yin ƙasa da murya Hajiya ladidi tace"ke kina ina yanzu ina san zanyi magana dake? kamar zata yi kuka Bintu tace" ina falon ya Abdallah ina gyarawa!'Hajiya ladidi ta saki wani uban tsaki, tare da cewa kaji banza ƴar shishshigi A yaushe ya zama yayan naki? in dai har zaki fara tunanin ya zama yayanki ashe bazaki saki jiki kiyi mana yadda mukeso ba,to bari jiki da kyau inaso kisa A ranki wannan aikin da zakiyi shine rayuwarki gazawar ki A aikin yana daidai da ɗaukewar numfashinki, dan haka ki gaggawar fita daga inda kike zan magana dake!' tana gama faɗar haka ta kashe wayar,A dai-dai lokacin da Bintu take ƙoƙarin maida wayar ma adanarta shi kuma ya sawo kai cikin ɗakin,A matuƙar firgice Bintu take kallonsa ƙirjinta babu abinda yake sai wani irin bugu da ƙarfi tamkar zai fito waje,
Abdallah sam bai gane me Bintu take ciki ba, Amma yanayin firgici da tsoro da ya gani akan fuskarta yasa ya gane bata da gaskiya, zuba mata ido yayi yana so ya ƙara karantar yanayin ta, A yayin da Bintu tayi ƙasa da kanta tana ɗan jajjan zara zaran yatsun hannunta,jikinta kuwa da za A ɓula baza a sami jini ba,saboda tsabar fargaba, (Allah sarki Bintu Abinka da wanda bai saba aikata rashin gaskiya ba)
Cikin maganar shi ta ɗaukar hankali yace" da ita ina breakfast ɗina?wata sassanyan Ajiyar zuciya ta sauke cikin ƴan sakanni ta dawo haiyacinta,cikin shagwababbiyar muryarta tace" yanzu zan je na kawo!'cikin janye jikinsa daga bakin ƙofar yake cewa A ransa, meye wannan yarinyar take shiryawa suwaye ne suka turota? ƙwafa yayi hmm ko meyene zan kamaki da hannuna,ranar kuwa ta tabbata bata da mai ceto.
Cikin hanzari ta gama shirya masa karin ta koma ɗaki tare da sawa kofar key,sauri tayi ta zaro wayar ta dannawa Hajiya kira, ko gama ringin batayi ba ta ɗaga tare da cewa,uban me kika tsaya yi tun dazu? cikin sauri tace" Hajiya ai ya kusa kamani ina waya,kuma kinga idan na tawo ban gama masa aikin ba dole inno zatazo nemana kinga ai da ta ganni ina waya zata tambaye ni dawa nakeyi! Hajiya ladidi ta katse ta da cewa na fahimta bar dogon sharhin nan ki buɗe kun nan ki kiji Abinda zan gaya miki,Bintu tace tom Hajiya ina sauraren ki!' Hajiya ladidi tace" kinsan dije ƴar aikin matar mansur?tace ban santa ba!' Hajiya ta ɗora da cewa zaki santa kuma dole kisanta saboda so nake ki shiga jikinta ki gano mun matar da take wa aiki A cikin ESTATE ɗin ALHAJI BALARABE,shine aikinki na farko na biyu shine Abdallah lallai inaso nasan abinda suke shiryawa shida ubansa daga nan zan ɗora miki babban aiki, zahra kiyi ta ka tsantsan da aikin nan duk ranar da kika yi sakaci wani ya gano ki to shike nan kin kaɗe, dan ina tabbatar miki bazaki taɓa iya ambatar ko da harafin L ba bare ƙarshen sunana dan haka ki kula da aikinki rayuwarki ina kuma jaddada miki shine rayuwarki (dake rayuwar A hannuku take ba.)
Tunda suka gama wayar take kai kawo A cikin tsakiyar ɗakin sosai ta fara jin ƙwarin gwiwa,tana ganin Allah ne ya dubeta ya kawo mata mafita ta tsanin da zata hau dan kaita hanyar da zatabi dan binciko ƙullellen ƙulli mai cike da mugun zarge,cikin ƙarfin zuciya tace" Hajiya ladidi bani ce da kuka ba kece da kuka har da birgima kin jawo wa kanki da kanki tashin hankali shekarar tonon Asirinki dake da mabiya bayanki da sauran mutanen munafukan cikin estate ɗin nan yayi Ni ɗin nan sai na zame miki ciwon ido dake da duk wani azzalumi, ku shirya domin ƴar zakanya ta girma, gani nan gareku maƙiya Allah duk sai na binciko gaskiyar datake A binne, yanzu ne za a fara wasan.
Inno ce zaune Bintu kuma nayi mata tausa yayin da Hauwa'u da Rahima ke zaune saman kujera, Rahima hira take ta zubawa inno da Bintu Ita kuwa Hauwa'u gaba ɗaya hankalin ta da tunanin ta yana kan scring ɗin wayar ta wanda ba komai take kallo ba sai hoton Abdallah,inno tace zahra ku tashi na aike ku wajen Hajjah dama baki taɓa zuwa kun gaisa dasu ba Rahima daga nan ki rakata wajen Hajiya Babba ta gaidata!'tun kafin ta rufe bakinta Rahima ta miƙe tsaye tana cewa ku taso muje, Hauwa'u da sai yanzu hankalin ta ya dawo kansu, ta wani taɓe baki gami da cewa Ni bazani ba!Rahima itama taɓe bakin tayi tana cewa Mutum dai wallahi ya gamu da aiki A rayuwar sa,tayi saurin jan hannun Bintu suka fita inno tana kiranta basu karɓi saƙwan ba, amma ina tuni sun ƙule,inno ta riƙe baki tare da cewa oh Ni zainaba jikar mutum biyu kome zasuje su faɗa oho.
A hankali cikin nutsuwa suke ta kawa har suka kai ɓangaren Hajjah, da sallama suka shiga falon tsarinsa iri ɗaya da falon inno komai iri ɗaya ne sai dai kala ta ban banta,
Hakimar macece kanuriyar asali mai matuƙar riƙo da Al'adunsu, tun daga yanayin ƙamshi na musamman da ya cika falon, tana zaune cikin kujerar ta ta alfarma, jikinta nan naɗe da lafaya mai asalin kyau da tsada,sai kuma Dady ane (Alhaji mansur)dake zaune kan kujerar data ke fuskantar ta, ga dukkan nin Alamu dai tattaunawa suke mai muhimmanci.
Amsa sallamar sukayi A tare suna mai zubawa Bintu ido dan ganin baƙuwar fuskace A garesu,kamar yadda ya kasance ɗabi ar Bintu durƙusawa tayi har ƙasa ta