Showing 54001 words to 57000 words out of 184937 words

Chapter 19 - KUDURAR ALLAH COMPLETE BY FATIMA Y ADAM

21 Jul 2024

16906

sake na kamaki daniyar cin amanata ko ƙoƙarin to na min asiri sai na yi miki mummunar illa A rayuwarki, bazance zan kasheki ba domin kisa A gurina ba hanyace ta ɗaukar fansa ba idan na kasheki kin samu salama to amma dai ina miki fatan kar hakan ta kasance!'cikin mugun tashin hankali Dije tace" ranki ya daɗe kin sameni da makamancin hakane?wani shu'umin murmushi tayi kana tace" Dije kar fa ki manta kifi naganin ka mai jarkowa,kina tunanin zakiyi wani motsine bada sanina ba? to indai kuwa hakan zata faru to lallai burina bashi da wani amfani da mahimmanci kuma bancika shu'uma ba, inaso ki sani Dije duk inda zaki shiga ki fita ina biye dake kuma!'Haɗuwar da kukayi da Bintu duk da tsarina ne amma kema dana ki tsarin A kwai abinda kuke shiryawa ke da ita wanda bakwa so nasani,shiyasa nake yi miki gargaɗi tun yanzu saboda duk abinda ya faru kiyi kuka da kanki, aiki kawai nace kiyi min ba fallasa ba!'daga haka bata ƙara magana ba ta wuce ta bar Dije san ƙame cikin matuƙar razana da tsinkewa da al a marin wannan shu 'umar mata kamar yadda takira kanta,to amma fa hakan baisa taji zata iya karya alƙawarin dake tsakanin su da Bintu ba sai dai dole zasu canja salon tafiyar,tasan Bintu tana da kaifin basira A sannu zasu haɗa ƙarfi da ƙarfe dan binciko wacece wannan mata,


Kwance take tayi ruf da ciki gaba ɗaya tunanin ta ya tafi kan abinda ta gani daren jiya bata taɓa tunanin cewa Yahh Abdallah zai iya bawa wata mace kulawa ba,sai gashi ta gani da idonta yadda ya ta rairayo Bintu A jikinsa,duk da tana tsammanin tausayine kawai da kuma matsayinta Na mai dafa masa abinci,yasa shi kulawa da ita,to kuwa indai har zai iyai wa mai aikinsa haka to matarsa fa? wani irin filling ta dingaji yana ratsata tare da wani irin so mai girma ji take inama ita yayiwa haka ba Bintu ba, tabbas indai har tana san mallakar Yahh Abdallah sai ta tashi tsaye dole tayi wani abu domin samun farin cikin rayuwarta,domin Abdallah da ita kawai ya dace ko ƴar uwarta Hauwa'u bata jin zata ƙyale in dai A kan soyayyar Oga Abdallah ne, Taufiƙa,tayi shirin mallakar Abdallah ta ko wane irin hali..

To shin hakan zata kasance kuwa?
Wace hanya zatabi dan mallakar gwarzan shekara kuma dodonsu ɗan zaki wato Abdallah?
Me kuma Anty Nafisa take shirin ƙullawa?
Shin Abdallah zai yadda kuwa ya haɗa hannu da Bintu ? Wai ma shin meyasa yake tsoron jefata cikin yaƙin?
Wai waye mutumin da fafi yace Bintu zata haɗu dashi zai tai maka mata?
Muje page na gaba yanzu aka fara wasan.......

COMMENT....

More typing...

Alƙalamin.

Fatima y Adam✍🏽
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕

*NA*


*FATIMA Y. ADAM*





_____________________________________*

*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*_____________________________________*



```Page 25 ```


Bintu sai da ta gama duk abinda zatayi kana ta nufi wajen inno dake zaune tare dasu Siddiqa A falo,durƙusawa tayi gabanta cikin yanayin tsoro tace" inno zan leƙa wajen Anty Nafisa tana kirana!'inno ɗauke kanta tayi cikin halin ko in kula tace" sai kin dawo!'ƙasa ƙasa su Siddiqa suka saka mata dariyar shaƙiyanci, su atunanin su yan zu inno ko fuskar Bintu bata ƙaunar gani,daga Bintu har innon babu wanda ya kulasu tashi tayi ta fita tana musu tata dariyar yadda suka maida su mahaukata ita da innon ta,ɗan kallon ɓangaren ɗakin tayi tanaji A ranta kamar ta nufi wajen yanzu amma sai wata zuciyar tace ki bari tukun har yanzu da sauran lokaci,gaba tayi tana mai ɗaukar shawarar zuciyarta,


Can saman ɗakinta ta sameta sai kaiwa da kawowa take ga dukkanin alamu dai Bintun take ta dakon jira,tana ganin shigo war ta kuwa tayi saurin ƙara sawa ta jawo ta cikin ɗakin sosai kana ta murɗa key ɗin jikin ƙofar,shigowa tayi sosai ta gyagygyara labulayen ɗakin suma, ita dai Bintu tana tsaye tana binta da kallo har sai da ta gama tazo ta ja hannun Bintun ta zaunar da ita gefan gadon itama ta zauna, cikin yin ƙasa da murya tace"Bintu ki saurare Ni da kyau wannan karon taimakon ki nake nema,ina kuma fatan zaki taimaka min,jinjina kai Bintu tayi cike da zaƙuwar san jin taimakon da zatayi mata, Anty Nafisa tace"Bintu ciki nakeso nayi!'wata irin zabura Bintu tayi tare da zaro manyan idanunta,bakinta har rawa yake tace" ban ban gane me kike nufi ba? Anty Nafisa ta miƙe tsaye tare da goya hannayen ta A hankali take zaga ɗakin, kana cikin nutsuwa tace"Bintu ki nutsu ki saurareni banason wannan tsoron naki domin zai iya ɓata min shirina,na yadda dake ne shi yasa har zan gaya miki wannan sirrin saboda ko babu ke zan iya aikata ƙudurina,to kawai dai nayi tunanin abin yana buƙatar hannu biyu, ko Hajiya ta bata san da wannan ƙudurin nawa ba,juyowa tayi tana kuma fuskantar Bintun tace"Bintu na gaji da zaman jiran gawan shanu ban san ranar da zan samu ɗan kaina ba shiyasa naga ya dace na fara shiryawa rayuwata abinda zai amfane ta,Bintu baki sake take bin duk inda Anty Nafisa tayi da idanu so take taji ƙarshen labarin domin ita A ɓangaren ta labarine ko kuma tatsuniya,Anty Nafisa ta cigaba da cewa Bintu zan ƙirƙiri cikin ƙarya!'bintu cikin mamaki tace" idan kika ƙirƙiri ciki shima ɗan ƙirƙirar sa za kiyi ko yaya? murmushi tayi nasamun Bintu da tayi mai dabara da fikira,kana tace" Bintu ai cikin ba zai zo da rai ba balle a ƙirƙiri ɗan! cikin tarin mamakin dake shinfiɗe saman fuskar ta ta kuma cewa to meye amfanin ƙirƙirar cikin idan baza a haifi ƙirƙirar ran ɗa ba? good kinyi tambaya mai kyau Bintu,haɗe fuskarta tayi sosai kana tace" Bintu kafin a haifi ɗan za akashe uban ɗan!'wata irin miƙewa Bintu tayi cike da tsananin razana duk da bata gama fahimtar maganar ba,Anty Nafisa kiyi min bayani dan Allah ban gane komai ba ban fahimci komai ba ban san inda maganar ta dosa ba,dafa kafaɗarta Anty Nafisa tayi tana cewa ke dalla ki nutsu sai kace wadda nace ke za'a kashe,ina so ki fahimceni sosai Bintu wannan hanyar ce kawai zata samar min da abinda nakeso,manufa ta ta kashe uban ɗa kafin na haifi ɗan ba rai kuwa shine dole ɗan cikina ya gaji dukiyar ubansa, idan aka haifeshi bai zo da raiba dukiyar ɗana ta zama tawa,kinga kema daga nan zaki samu duk irin kuɗaɗen da kikeso,

Tabbas alokacin nan da za'a tsaka jikin Bintu to kuwa baza asami jini na gudana ba ko mai nata ya tsaya cak hatta da numfashin ta da sauri da sauri yake fita tamkar ana fizgoshi, Anty Nafisa ta cigaba da cewa taimakon kuma danakeso kiyi min anan shine kece wadda zan bawa kwangilar kashe uban ɗan Bintu ke zaki kashe mijina!'waiyo masu karatu zan so kikaga yadda mutuniyar taku tayi a wannan lokacin,da ana mutuwa adawo to da sai nace Bintu mutuwa tayi ta dawo,idanunta ne suka tafi luuu kafin kace meye ta zube a gurin sumammiya,batare da wata fargaba ba Anty Nafisa ta shiga banɗaki ta ɗebo ruwa tazo ta sheƙa mata a fuska,wata doguwar ajiyar zuciya ta sauke tana mai buɗe idanunta tare da fatan ace duk abinda yake faruwa da ita mafarki ne zata buɗe idon ta ta ganta gata ga fafi ɗin ta da ummin ta tare da Baffa Jauro suna ce mata Bintu tashi daga wannan dogon baccin ya isa haka,amma kuma sai hakan bata samu ba dan tana buɗe idanunta sai caraf akan fuskar Anty Nafisa,tashi tayi da sauri tana ƙara murza idon amma dai still Anty Nafisa ce A gabanta ba fafi ba,wani irin kuka ne taji ya taho mata da sauri tasa hannu ta toshe bakinta, Aunty Nafisa ta zuba mata ido tana watsa mata wani mugun kallo tare da watsa mata tambayar da ta saka ta cikin tashin hankali tace" da kika damu haka ko ubanki nace ki kashe? duk da Bintu bata san waye ubanta acikin gidan ba amma sai da taji tambayar tamkar haka ne a cikin ranta sai takeji kamar uban nata akace ta kashe, katse ta tayi da cewa Bintu ki sani dole ne ki aikata abin da nasaki saboda kin riga kinji sirrina dan haka shawara ya rage naki ki aikashi ko kuma na kasheshi kema na kasheki sai ki zaɓa!'girgiza kanta take yi cike da tashin hankali mara misali, Aunty Nafisa tace" kije Ina jiran amsarki daga yau zuwa gobe,duk wanda kika gayawa wannan maganar shima zan haɗa dashi duk na aikaku inda ba A dawowa,cikin kuka Bintu tace" meyasa ke bazaki aikata ba tunda kuna tare a guri ɗaya? Anty Nafisa tayi wata shegiyar dariya kana tace"kema gashi kin faɗi dalili saboda muna guri ɗaya za ai zargina amma idan daga wani gurine babu wanda zaiyi zargina kuma kema ba wanda zai zargeki,ki sani mijina yana yawan cin masa a wajen Hajjah dan haka duk ranar da zai ci Ni zan sanar miki zan kuma baki gubar da hannuna kije can ki zuba ki gudu kinga babu wanda zaiyi zargin ki tun da ba zuwa ɓangaren Hajjah kike ba,idan kuma akayi zargin Hajjah fa? wannan babu ruwan ki tunda ke dai kinsha babu abinda yay miki zafi da wanda za azarga,maza ki tashi kije kar inno taga kin jima abinda kika zaɓa kiyo min test ba sai kinzo ba!nuna mata banɗaki tayi tare da cewa maza shiga ki wanke fuskar ki karki sake ki bar wata alama da zatai nuni da damuwarki!'cikin sanyin jiki Bintu ta tashi ta shiga banɗakin bata jima ba ta fito,batare da ta cewa Aunty Nafisa ko mai ba ta buɗe ƙoafar ta fice daga ɗakin,da wani irin murmushi tabita tana ji kamar burinta ya gama cika...


Tun da tashiga ɗakin ta tarufe kanta take kuka har sai da ya saukar mata da mummunan ciwon kai,ko kiching bata jin zata iya shiga, )su Oga Abdallah yau fa sai haƙuri dan baza ka samu haɗaɗɗen girkin Bintu ba)shin yaya zatayi da wannan babban tashin hankalin da ya kuma dannowa cikin rayuwar ta? gaskiya A wannan karon bata da wata dabara ko mafita dole tana buƙatar shawarar wani,to tayaya kenan? bayan ta yi mata gargaɗin kar ta faɗa wa kowa,to hakan yana nufin duk wanda na gayawa shima sai ta kashe shi? runtse idanunta tayi yayin da hawaye suka ƙi dai na zuba mata,ita kanta tasan tana cikin tsaka mai wuya,domin baza ta taɓa iya kashe koda kiyashi ba balle mutum sukutun guda,idan kuwa hakane dole tayi gaggawar neman wa rayuwarta mafita,harma da wanda Anty Nafisa take shirin cutarwa.

Ranar yini tayi A ɗaki tana fama da tunani da matsanan cin ciwon kai.

Inno duk ta shiga damuwa ta rasa yadda zatayi ta duba Bintu, can sai wani dabara ya faɗo mata duban su siddiƙa tayi waɗanda suke ta buga game cikin ƙwarewa da nishaɗi yayin da Taufiƙa take can tana zurfafa tunani akan neman cikar muradinta,cikin haɗe fuska inno tace" dasu Farida wai ina yarinyar nan ta shiga ne ban ji alamar tafito shiga kiching ba? Siddiqa ta taɓe baki tana cigaba da sha'anin gabanta,Farida tace"yo inno kika sani ko yajin aiki ta tafi,yau tana muradin ɓatawa Yah Abdallah rai,miƙewa inno tayi ranta A ɓace ta nufi ɗakin bintu,dariya Farida da Siddiqa sukayi har da tafawa,

A hankali ta tura ƙofar tare da sallama,cikin sauri ta ƙara sa gaban gadon,ta riƙo hannun Bintu,cikin tashin hankali tace" subhanallah Bintu baki da lafiya amma baki sanar dani ba? duba jikin ki kamar garwashi!'ɗago kan Bintu tayi ta ɗora kan cinyarta ta shiga shafa lallausan gashin kanta da ya baje har bayanta,cikin tausayi tace" sannu kinji Bintu tun ɗazu nake son dubaki amma ina tunanin ta ya zanyi hakan saboda yaran nan suna tare dani!'Bintu ta kama hannun inno cikin ƙarfafawa kanta gwiwa tace" inno karki damu ai naji sauƙi jiki nane kawai babu ƙarfi shi yasa kika ga ban fito ba!' inno tace" a'a Bintu ga jikin ki nan da zafin zazzaɓi amma kice min lafiya kike bari na duba ko Abdallah ya shigo nace yazo ya dubaki ya baki magani!'ai da jin haka Bintu tayi wata iriyar zabura sai gata zaune tana rarraba ido cikin rawar baki tace" Ni dai inno karki gaya masa naji sauƙi bari ma ki gani miƙewa tayi ta shiga dan tsalle,inno sakin baki tayi tana kallon Bintu cike da mamakin wannan tsoron da takewa Abdallah,kawar da tunanin tayi da cewa ke kam Bintu ban san wace irin matsoraciya bace!' ma rai raicewa tayi tare da cewa Wallahi inno zuwa zaiyi yamin allura gashi kullum fuskarsa A haɗe babu fara'a Ni kawai ki bani magani xan ji sauƙi!'numfashi inno taja kana tace" ai shikenan bari na kawo miki maganin kisha sai ki kwanta idan kika samu bacci zazzaɓin zai sake ki,shi kuma Abdullah bari naje nasamar masa wani abu da kaina ke ma sai ki ɗanci kafin kisha maganin! to inno na gode amma da baki wahalar da kanki ba zan yi masa da kaina!' inno ta miƙe tare da cewa a'a Bintu bana son gaddama ki kwanta ina dawowa!' daga haka tasa kai ta bar ɗakin.a hankali Bintu ta koma ta jingina da window tana mai jin ƙaunar inno har cikin ranta da kowa na gidan nan halinsu yayo ita da sauran kishiyoyin ta da kuma mai gaba ɗaya wato Alhaji Baba da tabbas sun zama abin koyi,wannan shi ake kira da ƘUDURAR ALLAH,


Duk abinda ya kamata inno tayi mata sai da tayi mata ta kuma kaiwa Abdallah haɗaɗen jalof ɗin da tayi masa wanda yaji uban kifi sai gashin kaza da tayi masa mai shegen ɗaɗi,dan haka yaci abincin duk da dai bakinsa yaji cewar ba Bintu ce tayi ba, dake ya riga yasan ɗan ɗanon girkin inno sai bai damu ba amma ya ɗan yi tunanin abinda ya hanata yin girkin.


Dole washe gari ta sawa kanta ƙarfin jiki ko dan saboda damuwar inno,da kuma gudun allurar Oga Abdallah,sai da ta gama kimtsa masa ko mai kana ta bar falon batare da ta bari sun haɗu ba tun da tasan shi tamkar Aljani yake wajen gano mutum baida lafiya, Abdallah ganin tayi masa karin kumallo yasa ya dai na tunanin komai,cikin sauri ya kammala saboda shima kwana biyu yana cikin busy,


Aunty Samira tace"sir me yasa aka fasa miting ɗin jiya kamar yadda kace? cikin yanayin nutsuwarsa yace"Samira jiya an sanarwa dasu Alhaji Nasir zamuyi mitin hakan ya ƙara tabbatar min da akwai munafiki A cikin mu,dan haka yanzu inaso duk ki kira minsu a kwai binciken da zanyi akan ko wannen mu! ok sir Bari na sanar dasu!'


Kallon su yakeyi ɗaya bayan ɗaya gaba ɗaya su goma ne suke ƴan team ɗin sa, sune Amin tattun da ya zaɓa dan yin aiki dasu sai dai bai san a cikin su wanda ya ke kware masa baya ba, amma dai yana da yaƙinin A cikin ƴan mintuna zai fito da ko ma wanene,ɗan gyaran murya yayi tare da gyara zamansa cikin haɗaɗɗiyar kujerar sa, kana ya fara magana cikin ƙasai tacciyar muryarsa wanda kana ji kasan babu wasa cikin dukan Al'Amuransa,yace"abinda yasa nace A yimin kiranku shine jiya nace zamuyi mitin amma hakan bata samu ba dalilin cin dunduniya da muka samu ɗaya daga cikin mu nayi mana!'shuru yayi tare da zuba musu ido ɗaya bayan ɗaya yana mai karan tar yanayin su,ci gaba yayi da cewa amma kusani na riga da na gama bin cikena A kan wanda yake fitar mana da sirrin mu na kuma gano kowanene!kallon kallone ya shiga giftawa tsakanin su kowa na tunanin waye? yayin da me aikata laifin ya fara fidda kansa wanda dama wannan duk shirin Abdallah ne yayi niyar kama kowaye A hannu shiyasa yay musu wannan hikimar,kuma Alhamdulillah yasamu abinda yakeso dan cikin hikimarsa da basirar da Allah Ubangiji ya fuwace masa ya gano mai laifin a cikin mutanen goma da ya amince dasu,ya ɗan daki table ɗin gabansa cikin wasu sakanni office ɗin yayi tsit,razanan nun idanunsa ya ɗora kan fuskar safyanu yana mai san ƙara tabbatar da zaton sa,mara gaski ance ko A ruwa gumi yake tuni safyanu ya shiga rawar jiki,cikin tashin hankali ya sauƙa ƙasa idanun sa na fitar da hawayen na dama yasan in dai a wannan harkar ne Oga Abdallah baida sassauci yana matuƙar girmama amana da gaskiya,cikin rawar baki ya buɗe baki zaiyi magana amma hakan bata samu ba saboda jin yadda wasu manyan ƙarti majiya ƙarfi suka da baibayeshi tare da sa masa sarƙa,ko su jabir baza suce ga lokacin da suka ga Abdallah yayi waya ba balle shigowar su Majid, kallon su Abdallah yayi fuskar nan babu alamar sassauci yace" ku tafi dashi karku saurara masa har sai na neme ku!'hankaɗa shi sukayi waje suka yi gaba dashi.

Dukkansu nutsuwa sukayi dan babu wanda jikin sa baiyi sanyi ba,sun riga da sun san hukun cin Oga Abdallah ba mai sauƙi bane,sai da yaga ma shaƙar ƙamshin sa kana cikin kakkausar murya yace" ina so duk wanda yasan zai ci amanata A wannan tafiyar salin alin ya fita daga office ɗin nan idan kuma ba haka ba duk wanda na kama da makaman cin abinda safyanu yayi hukuncin sa sai ya nunka nasa sau goma!'shiru yayi yayin da office ɗin ya ɗau shiru na wani ɗan lokaci kowannen su zuciyar sa cike take da tsoro sai dai kuma akwai sadaukar wa tsakanin su saboda suna san ogan nasu,shima safyanu dan badashi aka fara tafiyar bane bai san irin gwagwarmayar da ogan nasu yayi dasu bane,shi yasa har yaci amanarsa.

Dukkanin su sunyi alƙawari da kuma rantsuwa bazasu ci amanarsa ba, kuma zasu tsaya akan tabbatar da gaskiya ko mai runtsi komai wuya,daga nan ne kuma ya sallame su tare da sanar musu lokacin da zasuyi mitin ɗin ƙarfe shabiyu na daran yau in Allah ya kaimu da haka suka rufe tattatunawar.


Haka nan taji tana buƙatar ganin Dide ko da baza ta iya gaya mata halin da take ciki ba to tasan zata iya samun

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login