Showing 75001 words to 78000 words out of 184937 words
ya shigo gidan nan ko ya fita? cikin rawar jiki mai gadin yace"wallahi yallaɓai babu wanda ya shigo sai dai bansani ba ko lokacin da nazaga baya wani ya shiga!'wani mugun kallo Abdallah ya watsa masa tare da cewa ka tabbatar idan banga yarinyar nan ba saikayi na damar sakaci da kayi na barin aikinka kuma kabar get abuɗe! daga haka ya koma ya shiga mota tare da yimata wata irin wuta,ganin haka yasa mai gadin ya kwasa da hudu ya buɗe masa get,da wani irin azababban gudu ya fita zuciyarsa tamkar zata kama da wuta har ya rasa wane irin tunanin zaiyi, ita ta fita da kanta ko zuwa akayi aka tafi da ita?cikin wannan tunanin ya hango kamar Bintun tare da maza biyu sun zagaye ta da alama ma kukan nata na fama takeyi, cikin sauri ya taka burki tare da fita daga motar wata ƙaƙƙarfar ajiyar zuciya ya saki lokacin da ya tabbatar da cewa Bintu ce.
Ita kuwa Bintu tun lokacin da ta fito ta shati hanya batayi wata tafiya mai nisa ba wasu samari irin ƴaƴan manyan nan sangar tattu suka tare ta wai suna sonta, shine take ta fama dasu kan su rabu da ita sai kuka take amma sun ƙi rabuwa da ita acikin wannan yanayi Abdallah ya ƙara so ya samesu, Bintu tana ganinsa ta gudu bayan sa tare da cukyikyi sa tana sheshsheƙar kuka,ɗaya daga cikin sune yace" kai kuzo mu tafi wannan daga ninsa mijin tane!'ɗayan yace"ai inaga dai tabbas matar sace kawai mu fece!'Abdallah dai yana kallonsu bai kuma ce dasu komai ba ya juya da sauri tabi bayansa,buɗe mata motar yayi ta shiga sam ya kasayi mata magana saboda takaici, yarinyar nan tana bashi ciwon kai da yawa.
Ganinsu a tan game man get ɗin ESTATE yasa ta kuma sakin kuka cikin tashin hankali tace"Ni kabarni na tafi bazan koma wannan gidan nakuba bazan iya rayuwa da mutanen cikin sa ba,dan Allah ka rabu dani na gode da taimakon ka bazan taba mantaka cikin rayuwata ba, wallahi idan nakoma kasheni zasuyi,ga su inno ma duk haushi na suke ji kowa bai yadda dani ba, kuma Ni bani bace wallahi ban san komai ba!' kuka takeyi sosai wanda har sai da yaji wani iri can cikin zuciyar sa,cikin wata irin taushin murya yace" da ita ki daina kuka ba wanda ya yadda da abinda ya faru har inno ma duk sun fahimce ki!',da sauri ta goge hawayen fuskar ta cikin farin ciki wanda ya nuna tsantsan ƙuruciya da yarintarta, tace"da gaske inno ta yadda dani Hajiya Babba ma ta amince ban aikataba?gyaɗa mata kai yayi kawai yanajin tamkar wani abu na faruwa da zuciyar sa sai dai bai san komeye ba,A hankali ya fita ya zagayo ya fito da ita tare da kama hannun ta, ji yayi ance kar kasake ka dawo mana da wannan annobar cikin ahlin mu bazamu zauna da ita ta dinga kashemu da ɗaɗɗaya ba, ka mai da ita inda ka ɗauko ta dan shi kaɗai ya fi dacewa da ita!' wani irin kallo mai cike da tsana ta kaici haushi shi Abdallah ya kewa Dady Mansur,batare da ya kulashi ba ya cigaba da tafiya dan shi baisa wannan mutumin cikin sahun masu hankali ba,haka ya barshi agurin yana kunfar baki tamkar wani zararre.
Cikin nutsuwa yayi sallama falon Alhaji Baba,wani irin ƙayataccen murmushi Alhaji Baba ya saki ganinsu Abdallahn,yace"maza ku ƙaraso ƴan albarka Allah Ubangiji ya haskaka rayuwarku dan alfarmar shugaban mu Annabi Muhammad s.w.a.atare suka amsa masa da Amin Ya Allah, bazan iya misalta muku farin cikin Bintu ba ganin tabbas maganar Oga Abdallah ta tabbata, ga wata irin ƙauna ta bawan Allah da take ƙara mamaye jinin jikinta,gaidasa sukayi cikin girmamawa wanda bai bari sun ƙara wani magana ba ya ɗauko kuɗi a ɗaure cikin wata kyakykyawar leda wanda zaka iya hango abinda ke cikin ta, yace"matso nan jikata Faɗima!'matsawa tayi gabansa ya kuma kiran Abdallah shima ya matsa gab da Bintu hannun su Alhaji Baba ya kama ya haɗa dana juna ya sarƙesu daga bisani ya miƙa wa Bintu wannan kuɗin na hannun sa tasa ɗaya hannun ta karɓa cike da wani irin faɗuwar gaba wanda bata san dalili ba lokaci ɗaya jikin ta ya hau rawa,Muryar Alhaji Baba ce ta ratsa dodon kunnuwansu,Fatima karɓi wannan, sadakin Auren ki ne da Abdallah Allah Ubangiji ya baku zama lafiya ya kawo haske cikin rayuwarku.
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
```Page 32 ``
Hannun tane ya fara rawa saboda tsabar ruɗanin da maganar Alhaji Baba ta saukar mata, ji tayi tamkar an ɗora mata wani gungume man dutse akanta,wai dama da gaske Alhaji Baba yake ita zai ɗaurawa Oga Abdallah?anya kuwa wannan haɗin yayi?ya zatayi da farmakin Taufiƙa? Sannan taya zatayi ta cimma burin ta alhalin da igiyar Aure akanta?shin Abdallah zai tallafa mata kamar yadda fafi yasanar da ita?idan kuwa har zai tallafa mata to kuwa dole ta haƙura da Auren sa domin shima wata babbar dama ce agareta, wannan muskilalliyar Muryar tashi me tsananin daɗi ce ta katse mata tunaninta, Alhaji Baba mun gode Allah ya ƙara girma da lafiya,in Sha Allah zamuyi maka biyayyar da zakayi alfahari damu!'kut kaji wai zamuyi wannan ai aran baki ne,wato yau darar Alhaji Baba zaiyi dan tasan wannan muskilin ba abinda ya iya banda nunƙufurci da tsirawa mutane allura,duk gungunin da take da zunɓura baki akan idanun sa dan salon kallon Abdallah abin burgewa ne amma ga Bintu wanda shi kansa bai san yanayi ba,(amma koni alƙur an kallon na bani citta)Alhaji Baba yace"to masha Allah Ubangiji ya yiwa rayuwarku albarka ya baku zuri'a me albarka, Allah yasa wannan Aure ya kasance fitila ga rayuwar ku! da Amin suka amsa kana Bintu ta miƙawa Alhaji Baba kuɗi tare da cewa, Alhaji Baba kabar kuɗin nan Ni ban san me zanyi dasu ba!'yace"a'a Bintu wannan haƙƙin kine dole ki amsa idan yaso ga mijinki nan sai kibashi ya ajiye miki!'gyaɗa kai tayi kawai batare da ta kuma cewa komai ba,har zasu miƙe Alhaji Baba yace"au na manta ban tambayeka ba zaka zauna a gidan nan ne ko zaka tafi da matarka wani gidan daban? Abdallah ya ɗan rusuna yace"zamu cigaba da zama a ɓangare na har muga abinda Allah zaiyi!'hakan yayi kyau kuje Allah Ubangiji yayi muku albarka!'suka amsa da Amin kana suka fita daga falon, murmushin farin ciki Alhaji Baba ya saki tare da binsu da kyawawan addu'oi.
Tarbar da Inno tayi mata ita tasaka kuka wanda dama a kusa yake,rungume ta tayi sosai tana ɗan bubbuga bayanta,cikin kalaman lallashi take cewa haba Batula to kuma meye na kukan bayan kina kusa dani, dan ban shiryawa rabuwa dake yanzu ba sai nayi miki biki irin na yargata amma ba yanzu ba akwai lokacin yana nan zuwa,idan kuma zan haɗa da suna ne shike nan!' Abdallah harara ya watsawa inno kana ya shigewarsa ɓangaren sa ya barta ita da sakalalliyar Bintun ta,hannun Bintun ta kama ta isa da ita har ɗakin ta da kanta ta haɗa mata ruwan wanka wanda sai da Bintu ta shiga taga kamar ba zallar ruwa bane dan sosai yake wani irin fitinan nan ƙamshi mai kama jiki da zuciyar wanda aka raɓa,sosai taji daɗin jikin ta, kwanciyar ta tayi saman tattausan gadon ta,ko minti biyu batayi ba wani nannauyan Bacci yayi awan gaba da ita.
Tunda ya shiga ya gabatar da abubuwan da suka zama farilla agareshi, har ya kwanta saboda gajiyar dake tare dashi sai kuma wata gagarumar yunwa ta motsa masa, dan sai yanzu ya tuna rabon sa da abinci me nauyi tun kan wannan abin ya faru sai ƴan kame kame da yake dan bayajin zai iya cin kowane irin abinci idan ba na Bintu ba,ɗan tsaki yayi tare da tashi zaune ya dafe kansa dake ɗan sara masa,wayarsa ya ɗauka ya danna lambar inno bata jima ba kuwa ta ɗauka tare da yin sallama,amsawa yayi kana cikin takurawa kansa da magana yace"inno kisa yarinyar nan ta dafo ko noodles ne ta kawo min yunwa nakeji sosai!'inno tace"ai inaga sai dai Ni nayi maka dan Bintu tayi bacci!'ki tasheta inno yanzun nan!' saurin dafe kansa yayi saboda shikan sa bai san ya akayi ya faɗi hakan ba cikin san kawar da waccen maganar yace"inno bana son ki wahalar da kanki kawai ki tasheta bata da magagi!'murmushi inno tayi tare da cewa to gaskiya bazan sa ta girki daga farkawar ta ba sai dai idan na dafa maka in yaso na tasheta ta kawo maka, hakan yayi maka?shike nan inno yayi!'daga haka ya kashe wayar batare da yasan irin mamakin da yabar inno dashi ba,duk wanda yaga Abdallah ko yaji kalamansa dole zai gane halin da yake ciki amma a yadda ta lura sam shi bai san yanayin duk wannan ba,bai san yadda al'amuran sa suke tona asirin zuciyarsa ba,wani ƙawataccen murmushi ta saki gami da yunƙurawa dan zuwa kiching ɗin.
Cikin bacci taji kamar ana tashin ta, cikin nutsuwa ta buɗe manyan idanunta da a yanzu suka bada wata kala ta musamman saboda baccin dake cikinsu,inno tace"yi haƙuri Bintu ta shi ki kaiwa Abdallah abinci, waya ya yimin yana jin yunwa!'tura baki tayi gami da gyara kwanciyar ta zata cigaba da baccin ta,inno tayi saurin ruƙota cikin lallami tace"haba Bintoton inno kinga fa cewa yayi na tasheki ki dafa masa amma saboda kar na tasheki sai ni nashiga kiching ɗin,kuma kin san dai halinsa tsaf zai biyoki har nan idan baki tashi ba!miƙewa tayi tana gunguni,ga bacci fal idonta amma saboda mugunta ance tana bacci wai atasheta,karɓar tiren da Inno ta zuba abincin tayi ta zura silifas saboda ba dai dai take ba sam ta manta da kayan da ke jikinta,ita kuma inno batace ta canja ba saboda taga cikin bacci take.
Wani irin kuka ne ya kufcewa Taufiƙa lokacin da taga shigarta falon Abdallah daɗin abin baƙin cikin kuma kayan baccin da suke jikin Bintu wanda ko ita mace idan tacire hassada da kishi tabbas sai ta burgeta,gashi dai kayan ba wani nuna tsiraici sukayi ba amma yadda doguwar rigar mai shegen sulɓi da wani irin shep tabi lafiyayyan dirarran jikin Bintun shine abin kallo da burgewa, Siddiqa ce tayi saurin janye ta tare da toshe mata baki suka koma cikin ɗakinsu, Siddiqa tace"sai kin kawowa kanki maganar inno wadda itace zata iya fasa ƙahon zuciyarki!'cikin kukan fitar haiyaci Taufiƙa tace"wallahi bazan iya ba bazan iya kallon wannan macijiyar tana yawo tare da abinda nafi ƙauna arayuwata ba, tabbas Bintu kin janyowa kanki rigima da tashin hankali mara karshe dan sauna salwantar da rayuwarki!'
Bintu baiwar Allah bata san ma tanayi ba, ita haushin ankatse mata baccin ta a yanzu shi yafi damunta,dan haka da haushin ta faɗa falon bata ganshi anan ba,dan haka cikin sauri ta ajiye tare da juyawa dan barin falon,cikin ƙasaitacciyar muryar sa yace"nan zaki kawo min!' ashe har yaji shigowarta kuma yana da yaƙinin abinda take shirin yi, Ai kuwa buɗe ƙofar ɗakin da yayi yaga tana sanɗar ajiyewa,da sauri ta ɗago ta ɗan dubesa kana ta duƙa ta kuma ɗauka ta biyo shi ɗakin babu abinda takeyi azuciyarta sai mita,tana shiga ta ajiye zata kuma fita nan ma dakatar da ita yayi da cewa ki tsaya ki tafi da kayan dan bazan kwana da ƙazanta ba!'ƙazanta kuma lallaima wannan mutumin wato kwanikan ne ma ƙazanta?kallonsa take cike da takaici saboda yadda ya basar kai bakace shiyayi maganarba, A hankali ta samu guri ta rakuɓe tana jira ya gama yangar cin abincin nasa.
Wucewar mintuna huɗu zuwa biyar ya ɗan saci kallon ta sai yaga ta sheme ta cigaba da baccin ta hankali kwance,samun kansa yayi da zuba mata rikitattun idanun sa wanda har baisan iya tsawon lokacin da ya ɗauka yana binta da kallon ƙurilla ba,ɗan ƙaramin bakinta ya tsirawa ido haka nan yadinga jin wani abu na ratsa zuciyarshi wani irin mutuwa jikin sa yayi har wani sanyi-sanyi ne ke ratsa cikin jikinsa, lumshe idonsa yayi daga kallonta yayin da yarasa abinda ke damunsa wanda shi dai yasan bai taɓa jin Irin wannan yanayin tare dashiba,ɗan tsuka yayi tare da tashi ya shige toilet sabon brush yayi kana ya fito ya ɗauke kayan ya fita dasu kan dining table ya ajiye,
Dawowarsa cikin ɗakin yayi dai dai da wani irin juyi da Bintu tayi, lokaci ɗaya santala santalan fararen cinyoyin ta suka baiyana,wani irin hajijiya yaji tana ƙoƙarin kada shi da sauri ya samu gefan gadon ya zauna tare da dafe kansa,ɗan satar kallonta yayi cikin sauri ya runtse idanunsa shifa sam bai saba ganin irin wannan abun ba, haka kawai tazo ta wani baje min aɗaki!'(Abdallah kaji tsoran Allah kaifa kace ta zauna tajiraka ka gama) tsakin ya kumayi kana ya yunƙura ya tashi, inda take ya ƙarasa tare da duƙawa runtse idanunsa yayi ya shiga bubbuga ƙasan carpet ɗin,amma tamkar ma nauyin baccin yake ƙara mata sai ma ƙafa da ta kuma ɗora masa a jiki,(kai dai kace bata da magagi ehe)janye ta yayi yana mamakin nauyin bacci irin nata wanda shi sam bai zaci tana dashi ba,da ƙyar ya samu ta farka amma duk da haka cikin magagi take,kamata yayi ya miƙar da ita tare da saita mata hanya,yace" tafi kije ki kwanta Sarkin bacci!'kamata yayi dan taimaka mata amma sai yaji gaba ɗaya ta yi kansa kasancewar suna tsaye ne a bakin gadon hakan yasa basu sha wahalar fadawa saman gadon ba,gaba ɗaya ta sakar masa nauyin ta saboda baccin da take sosai dan bata san komai yana faruwa ba, Bintu da shegen san jiki tuni tasa hannu ta kuma kanainaye shi tare da cusa kanta cikin ƙirjin sa tana shaƙar dadda ɗan ƙamshin jikinsa, rumtse idanun sa ya kuma yi tare da cewa ya Allah!'buɗe idan yayi tare da zubawa kyakykyawar fuskarta ido yayin da ita kuma take kwance saman jikin sa duk tabi ta duƙunƙune shi kamar wanda take tsoron kar asace shi,kasayin kataɓus yayi saboda yadda gaba ɗaya ta saukar masa da wata irin kasala da mutuwar jiki ki yayi ko ɗan yatsan sa ya kasa motsawa, kawai sai ya rabu da ita tare da ci gaba da kallon fuskarta, ko A baccin ma bakinta a ture yake saboda da haushin sa ta yi baccin samun kansa yayi da ɗan jan ɗan ƙaramin leɓenta yana mamakin rigimar Bintu ita damuwarta ta lokacin da Abu ya faru ne amma sam bata barin damuwa aranta sai dai idan A lokacin damuwar tazo ko ta tuna amma sabgoginta take hankalin ta kwance, (Abdallah ba haka bane Allah ne yabawa Bintu baiwa da wani irin hali na rashin barin damuwa tayi mata tasirin da har zata hana ta walwala, duk da tarin ƙaddarorin ta sai Allah ya sakamata tawakkali da amsar ƙaddararta a duk lokacin da ta kutso rayuwar ta) hannunsa akan tattausan lip ɗin ta wani daddaɗan bacci yayi awan gaba dashi,Abdubint asuba ta gari ayi bacci lafiya amma kar amakara sallar asuba.
Labarin da Anty Nafisa taji na dawowar Bintu yayi mata daɗi sosai tana ganin matsalarta kamar tazo ƙarshe tanayiwa Bintu kallon maganin damuwar ta,ita Auren Bintun sam bai dameta ba dan aganinta bata ga abin damuwar ba wannan muskilin yaron da ba gane gabansa da bayan sa ake ba tsaf watarana zai iya sako Bintu,kuma da ɗin da ɗawa shi ba ahlin ALHAJI BALARABE bane balle abun ya dameta,kawai dai abinda ta sani ne dole a wannan lokaci Bintu tayi mata abinda take so dan haka ita kawai take jira ta gabatar da cikin ƙaryarta,daga tasamu abinda take nema babu wanda zai kuma jin ɗuriyarta sabuwar rayuwa zata buɗe ita da sabuwar soyayyar ta.
Cikin juyi da tsananin daɗin bacci takuma shigewa jikin sa tare da ɗora kanta saman ƙirjin sa tan shaƙar dadda ɗan ƙamshinsa alokacin tuni ya farka saboda kiran sallar da aka ƙwala,shi da yake tashi kafin kiran sallar dan gabatar da nafila, amma yau shine da wannan nauyin baccin gashi idan baiyi da gaske ba zata iya sawa ya makara,a hankali yake ƙoƙarin zare ta daga jikinsa amma da ta kuma yin wani juyi sai gata gaba ɗayanta a ruwan cikin sa tare da zagaye hannuwan ta a ƙugunsa,runtse idanunsa yayi tare kiran Ya Allah!'wannan yarinyar so take ta kashe shi, bai mutu da guba ba gashi nan zata kasheshi da wannan juyin data keyi a ruwan cikin sa,daya ga dai da gasken makara yake neman yi kawai sai ya saka hannu ya ture ta kana ya miƙe,ita kuma a daidai lokacin ta farka tare da ware manyan idanunta ganin a inda take yasa tayi wata wuntsilowa daga kan gadon tare da zaro manyan idanunta, tace"na shiga uku anan na kwana?shine bai tasheni na koma ɗakina ba!' harara tabi bayansa dashi lokacin da ya fito daga toilet ya nufi ƙofa dan fita,bata daina hararar saba har ya fita daga ɗakin,tashi tayi ta ta fita, cikin sanɗa ta shige ɗakinta dan kar wani ya ganta amma Taufiƙa wadda tun daren jiya da taga Bintu ta shiga part ɗin Abdallah ta kasa ta tsare ko da rintse bata rintsa ba shi kuma wan da takeyi domin sa ma baccin sa yayi tare da matar sa hankalin sa kwance,komawa ɗakinsu tayi tare da ƙarfafa mummunan alwashinta akan Bintu.
Alhaji Mansur ne zaune a falon Hajjah sai masifa yake zubawa kamar zai aro baki ya daɗa,Hajjah cikin takaici ta dubeshi tare da cewa kai kam Mansur ban san abinda yake damunka da yaran nan ba, duk kabi ka damu kanka kashiga cikin sabgar da ba taka ba kayi kane kane,shi Abdallah n da ya fito da ita bashi taiwa laifin ba? ina ruwanka da yaran da Ako da yaushe zai iya barin cikin ahlinka babu abinda ya tare maka wanda sai kaso zaka ganshi cikin gidan nan amma duk kabi ka damu kanka,Ni bana son wannan halin naka Mansur ka canja hali na gaya maka!'shuru tayi tana maida numfashi yayin da ran nan nata idan