Showing 51001 words to 54000 words out of 184937 words
kusa dan gana da inda zata, sai kuma taja wani uban burki wanda saura ƙiris ta angije wani me napep bata kula da zagin dayake antaya mata ba ta gangara gefe tayi fakin wayar ta dake ta neman ɗauki ta raruma,ta can ɓangaren cikin muryar ƴan daba akace mata Mr Devid ya akayine naga kiranki Ina cikin ɗaukar saiti!'ajiyar zuciya ta saki kana tace"
Fire kana inane yanzu ina kan hanyar zuwa tsangayar ka!' yasa wata shegiyar dariya mai ban haushi, kana cikin maganarsa ta maye yace"hajjaju kenan kin so dakar gurbi saboda Ni yanzu bana Abuja na tafi ƙaddamar da ɗan wani aiki amma ba zan jima ba ki bani sati biyu kawai on my way!'momy Abigirl taja dogon numfashi kana tace"shike nan Fire Amma naso kana kusa saboda aikin na gaggawa ne amma babu damuwa zan jarraba wasu hanyoyin kafin dawowarka!'yauwa hajjaju sai nadawo ɗin!'kifa kanta tayi jikin sitiyarin tana maida numfashi,sai da ta ɗauki wasu ƴan mintuna kana taja motar A hankali kamar ba ita ta gama sheƙa gudu ba,
Can cikin baccinta taji kamar motsi ta bayan ɗakinta har ma da sautin magana ƙasa ƙasa,cikin sanɗa da san cire tsoro ta tashi ta nufi jikin window A hankali ta manna kunnenta, abinda taji ana faɗa shiya matuƙar tayar da hankalin ta zama tayi daɓar aƙasan ɗakin yayin da zufa take yanko mata ta ko ina tamkar babu fanka A ɗakin,kafin kace meye idanunta sun jiƙe jagab da hawaye,yadda taga rana haka taga dare sai dai bata bari daren ya tafi abanza ba saida ta rayashi da kiyamul laili.
Cikin mutuwar jiki ta gama haɗa masa karin kumallo,sai da ta gama komai ta jera,kana ta samu guri ta raɓe kamar munafuka,bata motsa daga inda take ba har ya dawo daga motsa jiki ya shiga ya shirya ya fito tsaf dashi tamkar wani fure sai ƙamshi yake zabgawa,sumar nan ta kwanta tayi luf sai ƙyalli takeyi, nan ma dai yayi mamakin ganinta amma sai ya share ta ya nufi dining,har ya gama karyawa bata tashi ba sai dai ido datake binsa dashi,ɗaki ya koma ya ɗauko jakarsa ya fito,zuwa yayi ta gabanta zai wuce, tayi saurin tashi tasha gabansa,idanunta cike taf da hawaye,tsayawa yayi yana kallonta cike da mamaki,har zai kuma wucewa sai kuma ya dakata jin ta biyoshi cikin ƙosawa da ganin yanayin da take ciki yace"lafiyarki kuwa? cikin kuka tace"karka fita zasu kasheka wallahi naji da kunnena suna faɗa jiya ta bayan ɗakina!'wani kallo yabita dashi kana A hankali ya taka ya koma ya zauna cikin kujera dubanta yayi da lumsassun idanunsa kana cikin taushin murya yace"zonan!'cikin sanyin jiki ta ƙara so inda yake ta durƙusa,A gabansa cikin nutsuwa sai dai fuskar nan a haɗe take ka tamau babu alamun ya taɓa sanin yadda ake murmushi,yace" ina jinki ki nutsu kiyi min bayani banason bana son hawayen Nan!'
Samu tayi ta dai dai ta nutsuwar ta da ƙyar kana tace"jinayi suna cewa za'a sace tayar motarka da zaka fita da ita kuma ina tunanin sun sace"saboda alokacin umarni ake badawa da aje a sace!'cikin san tabbatar wa, yace" zaki iya shaida muryoyinsu?girgiza kanta tayi tare da cewa Ni ban taɓa jin muryoyin ba!'jin jina kansa yayi tare da cewa tashi ki tafi!'ɗan kallonsa tayi amarairaice,kamar zata fashe da kuka,bai ce mata komai ba ya ɗauki wayarsa saboda ya fahimci abinda take nufi,wayar yakara A kunnensa,jim kaɗan yayi magana,kakawo mota yanzu ina jiranka!' daga haka ya kashe wayar tare da maida idanunsa ya lumshe,ganin haka yasa ta miƙe A hankali ta fita daga falon ta ƙasan ido yabita da kallo har ta fice,
Duban samuyal yayi bayan sun shiga office ɗinsa,yayi masa alamun yana sauraren sa, samuyal ya ɗan gyara zamansa kana yace sir wannan gida na Alhaji Nasir ne kuma an ta nade shine saboda zaman mitin da sukeyi idan hakan ta taso!'ya miƙa masa wata doguwar paper yana cewa ga bayanan waɗanda suke mitin ɗin da jerin sunayensu!'karɓa yayi tare da jinjina wa samuyal,daga nan kuma ya bashi umarnin tafiya da cewar sai ya neme shi.....
Comment.....
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
```Page 24 ```
Babbar mace ce, wadda baza ta gaza talatin da hudu ba,kyakykyawa ce bata da wata makusa,tana da kyawun jiki shiyasa idan ka kalleta zakayi tunanin bata kai shekarunta ba,A hankali ta zauna kan kujerar dake fuskantar sa,kana cikin girmamawa A matsayinsa na oganta,ta gaida sa,dubanta yayi cikin nutsuwa yace"Anty Samira ga wannan fayal ɗin kije ki duba shi ,A nutse,banaso A samu kuskure,saboda wannan aikin da zamu fara yana da ban banci da sauran aiyukan da muka saba fuskanta dole yana buƙatar shiri da kuma addu'a aikin yana da haɗari Anty Samira sai mun kula gaba ɗayan mu!'Samira ta ɗan ja dogon numfashi kana cikin nuna sadaukarwa tace"karkadamu sir,kafin na fara aikin nan nayi alƙawarin babu abinda zai tsoratani naji na karaya na sadaukar da rayuwata wajen kare rayuwar al umma dan haka zan je na duba insha Allah baza asami matsala ba!jinjina kansa yayi cike da gamsuwa,kana yace" shike nan zaki iya tafiya!' sallama tayi masa gami da fita daga office ɗin,shima kiran Yahya yayi,dan yana son shiga asibiti.
Lokacin da ya dawo gidan A ɓangaren sa ya sameta duk da bai dawo da wuri ba yayi mamakin abin da ya hanata kammala girkin da wuri amma sai bai bawa kansa damuwa ba ya barshi kawai a yanayin yau da gobe,ita kuwa Bintu ba komai ne ya hana ta girkin da wuri ba sai ciwon marar da yake ɗan tsun kulinta Lokaci zuwa lokaci,A dai dai lokacin da take shirin fita daga falon mararta tai wani irin murɗawa da sauri ta durƙusa gami da riƙe cikinta yayin da gaba ɗaya ƙafarta ta riƙe katamau sai wani irin danƙa da marar take mata,abinka dama da wadda kuka baya mata wahala tuni fara rera abinta,yana fitowa yayi karo da sautin kukanta girgiza kansa kawai yayi yana mamakin yadda sam kuka baya mata wahala,zama yayi yaci haɗaɗɗen danbun shinkafar da yaji zogala da kayan haɗi sai zabga ƙamshi yake,sai da yaci yay ƙat kana ya kora da kunun ayarsa me shegen ɗaɗi goge bakinsa yayi da tishu,kana cikin yanayin takunsa na isassun maza masu kwarjini da haiba ya taka har zuwa kan luntsumemiyar kujerarsa,wani irin zama yayi mai cike da burgewa kai komai Abdallah yayi sai yayi masa kyau komai nasa abin burgewa ne, cikin wani irin salo mai cike da burgewa,ya zuba mata lulu eyes ɗinsa masu haske da sheƙi,jin idanunsa na yawo ajikinta yasa ta ƙara sautin kukan ta tana mai jin haushin yadda ya shareta,to ba sai ya tambaye ta abinda yasa ta kuka ba amma ya mata shuru sai kallon da ya ishe ta da shi kamar wani maye,jin ya ɗan lafa mata yasa ta miƙe A hankali zata lallaɓa ta bar masa falonsa inyaso sai yaci kansa,wani irin rawa ƙafarta ta shigayi yayin da marar ta kuma juya mata ai batasan lokacin da tasaki ƙara ba gami da zubewa ƙasa tana wani irin juyi wanda yake nuni da tsananin azabar da take sha, A hankali ya miƙe cikin takunsa na nutsuwa ya isa inda take kwance tana faman juyi,wani ɗan tsuguno yayi na burgewa A gabanta,kana cikin kamilalliyar muryarsa yace"me yasa ki kuka? duk da halin da take ciki amma hakan bai hana ta jin haushin tambayar tasa ba,har sai da ta ɗan yi musu-musu da bakinta tana ɗan murguɗa shi,sharewa yayi kamar baiga abinda tayi ba,idan bazaki magana ba ki tafi min A falo kin dameni da ihu!'ƙasa ƙasa ta wulla masa wani shu'umin kallo wanda ita aganinta hararace,ganin ya tashi zai bar gurin yasa ta kuma sakin ƙara wadda har sai da tasa ya runtse idanunsa,har ya rasa me Yakamata yayi,dawowa yayi tare da miƙa mata hannunsa batare da ya dubeta ba, cak kukan nata ya tsaya,yayinda ta ke bin hasken tafin hannun nasa da wani irin kallo,kusan sakanni ashirin kafin a hankali ta ɗaga hannunta ta ɗora bisa tafin nasa hannun,kamawa yayi ya miƙar da ita tsaye ,kana ya shiga takawa A hankali yana nufar ƙofar fita da ita,wani irin kallo take bin kwantaccen gashin da ya ƙawata ƙeyarsa dashi har bata san ya akayi ta shiga taka ƙafar data riƙe saboda ciwo ba,
Bashi ya tsayaba sai da ya dangana da ƙofar ɗakinta kana A hankali ya saki hannunta ya juya ya barta A tsaye,saida ta ga yashi ge falon sa kana ta ji ciwon ya dawo sabo, komawa cikin ɗakinta tayi ta waɗa kan gadonta tana juyi,tsit tayi lokacin da taji alamun an shigo ɗakin,ɗago kanta tayi cikin yanayin jin ciwo,ɗan lumshe idanunta tayi kana ta buɗe su A hankali ta zuba su kan kyakkyawar fuskar sa mai cike da kamala,ta kowa yayi har gaban gadon,kana ya miƙa mata robar ruwan dake riƙe A hannun sa,karɓa tayi ya kuma miƙa mata wasu magunguna, suma karɓar tayi sai juyasu take A hannunta ta kasa sha, dan tsakanin magani da allura bansan wanda Bintu tafi ƙi ba,ganin taƙi shane yasa ya ɗan zaro mata idanu wanda dole yasa ta runtse idanunta ta afasu A baki,da farko kamar zatayi amai sai kuma ta koma tana maida numfashi,atunaninta juyawa zaiyi sai taga yana haɗa allura,tofa anan akeyinta cikin rawar murya tace"Ni ba sai an yi min allura ba naji sauƙi!'bai kula ta ba ya gama haɗa allurar,yay mata alama da girarsa data gyara zaiyi mata,tura baki tayi tana magana ƙasa ƙasa,mutun duk abinda zaiyi sai ya haɗa da mugunta,ga kuma bazai yi magana ba sai dai komai yayi wa mutum alama kamar wani bebe shi ko gajiya bayayi da rashin magana,bata aune ba sai jitayi kawai ya riƙe hannayen ta duka biyu yana ƙoƙarin tsira mata allura,wani irin zillo tayi sai gata gaba ɗaya A cikin jikinshi hakan kuwa ya bashi damar riƙe ta gam ya tsira mata allurar,ƙanƙame shi tayi tana kuka wanda harga Allah kukan zafin allurane, yana gama yi mata ya tura ta saman gadonta,ya tashi ya bar ɗakin yana mai jin mamakin sangarta da tsoro irin nata,ko ta yaya zata iya taɓuka wani abu da wannan shegen tsoron,
Taufiƙa tana ganin zai fito tayi sauri tabar bakin ƙofar,sai da taga ya shige ɓangaren sa, kana ta shiga ɗakin,samun Bintu tayi tana kukan allura,tsayawa tayi A kanta tana fidda wani irin huci na tsananin kishi da tsana,tace" yanzu me zaki iya cewa game da wannan? sabo da sabon iskanci yau har sai da kikayi kisisinar da yashigo ɗakinki,wai Bintu me kike nufi da Yahh Abdallah ne?ɗan ranƙofawa tayi kana cikin tabbatar mata da abinda zata iya aikatawa taci gaba da cewa, Bintu idan har bakya son shiga tashin hankalin da baki taɓa tunanin zai kusan ci rayuwarki ba to lallai kar kibari zuciyar Yahh Abdallah ta fara sonki,san nan karki bari taki zuciyar tayi gangancin son Yahh Abdallah,wannan kashedi ne da nake miki saboda tsira da farin cikin ki, wallahi Bintu bantaɓa faɗar abu na karya shi ba muddin kika bari Yahh Abdallah ya soki to ki tabbatar da cewa zan iya saka wuƙa na yanka wuyanki, batare da nayi na dama ba,gara gara ma taki zuciyar tasoshi wannan ke zaki zauna cikin wahala,dan haka ina fatan zaki kiyaye!'daga haka ta fita ta bar Bintu sake da baki da wani irin maɗaukakin mamaki,meyasa wai bata gama da wani al ajabin ba wani yake danno kai, wai mace matashiya ce da irin wannan kaifin harshe,to wai shin gidan nan me yasa ɓara gurbin cikin sa sukayi yawa? meyasa mutanen kirki basu da yawa? wai waye silar gurɓacewar ahlin ALHAJI BALARABE ne,tabbas wannan shi ake kira da wata sabuwa,to amma ita ina ruwanta da Oga Abdallah meyasa take tunanin zai sota koda ita taso shi tabbas Oga Abdallah ba zai taɓa santa ba saboda babu gami babu alama wutsiyar raƙumi yayi nesa da ƙasa,miƙewa tayi ta ɗauro alwala ta fuskanci alƙibla domin miƙawa Allah kukan ta da kuma neman kusanci da shi.
Washe garin ranar kuwa garau ta tashi sai dai al amarin da yake ɗan cizan zuciyar ta har yanzu shine mamakin Taufiƙa,tabbas taga matuƙar ƙoƙarin ta tare da ƙarfin halinta, haƙiƙa sai tayi hankali da waɗan nan mutane huɗu Taufiƙa Siddiqa Farida da kuma Oga Sayyid,dan tabbas ta fahimci mugayen marasa mutunci ne,kuma zasu iya kawo mata cikas gurin aiwatar da aikinta,da wannan tunanin ta ta fito daga ɓangaren Oga Abdallah,wanda kwata kwata basu haɗu ba dan sai yanzu taji ta na matuƙar kunyar haɗuwa dashi,saboda ta gano ya gane abinda yake damunta jiya,tunda gashi ya bata magani da allura kuma taji sauƙi,wato dai yana nufin yadda yake gane halin da mutum yake ciki, shima haka yakeso A dinga gane yaransa, na kurame,ai ko baze yuwu mutum da bakinsa yaƙi yin magana ba wannan kam sai shi Oga Abdallah.
Tana shiga ɗakinta ta ji wayar ta na ƙara,da sauri ta ƙarasa inda ta ajiye wayar a ƙarƙashin fulo ta ɗauka,sunan Aunty Nafisa taga yana yawo saman fuskar wayar,ɗagawa tayi tana tunanin me kuma ake shirin ƙullawa dan dukkan kiran da Hajiya ladidi zatayi mata ko Anty Nafisa,kirane na sabuwar buƙata na baƙar manufa,batare da Anty Nafisa ta saurari gaisuwar ta ba tace"lallai ina buƙatar haɗuwa dake yau dan haka kizo ɓangare na kisameni!' ido Bintu ta waro tare da cewa lafiya dai ko? ba tambayar ki nake buƙataba ganinki nake buƙata dan haka ina jiranki!'sauke wayar Bintu tayi daga kunnen ta tare da cewa Allah ya shiga tsakanin na gari da mugu sai na roƙi Allah ya bani ikon juriya akan sabon Al'amarin da zaki zomin da shi dan ina da tabbacin ba Alkhairi ne yasa kike nemana ba...
Anty Samira ta dubi oga Abdallah tace"na kammala dubawa yanzu dai sa hannun sir Adebayo muke buƙata da sa hannun Babban sakataren kungiyar Dss,daga nan sai mu shiga bincike ka in da na'in!'Abdallah ya cire na urar dake saƙale A kunnensa,kana cikin tsurawa computer dake gabansa ido yace"duk bamu da matsala da wannan tunda munsami babban sahannu daga manyan su wannan ma ba zai gagara ba tunda duk muna tare dasu,yanzu abinda ya kamata muyi shine,inason hada mitin ɗin sirri wanda acikin sane nakeso na tace waɗanda basu can canta da wannan aiki ba saboda ina tunanin an samu ɗan leƙen asiri acikin mu, ma ana dai wanda yake fitar da sirrin mu saboda jiya ankawo min hari har cikin gida, A yadda tunani na ya bani tabbas an fitar da wani shirin mu shiyasa har aka fara shawarar kasheni,kuma daga haka zasu iya canja wani tsarin, dan haka tunda nasan yanzu sun san abinda muka shirya musu to mu kuma zamu canja namu tsarin binciken,dan haka zamuyi mitin yau sai anjima duk zanyi muku test ɗin a ina kuma ƙarfe nawa, Aunty Samira Dan Allah ki kula da kanki saboda A kwai haɗari cikin wannan aikin duk abinda kikaga baki yadda dashi ba kiyi gaggawar sanar dani'zaki iya tafiya kisanar musu da maganar mitin ɗin cikin kula!' shike nan insha Allah zan kiyaye, Allah ya bamu nasara!' Amin Ya furta A saman laɓɓansa..
Alhaji Nasir cikin tashin hankali yace" abinda na gaya muku tun farko shi ne yake san tabbata kunga dai wannan damar ta kufce mana dolene mutashi tsaye yaƙi biyune ya samemu kunga dai gashi nan mun tsaya wasa mu ba ga cimma burinmu ba,kuma baga tsira da rayuwar mu ba tunda gashi an fara bibiyar mu za adinga yi mana ɗauki ɗai ɗai!'ya dire maganar sa yana sakin wani zazzafan huci,Baba Nura ya ɗauki xan cen da cewa Baba Nasiru karka ta da hankalin ka yaƙi ne fa tsakanin mu dasu kuma idan ya tserewa wannan farmakin kana da tabbacin zai iya tsererewa na gaba? Alhaji Salisu ya ɗan ja numfashi kana cikin ta raddadi yace"nifa ina mamakin yadda akayi yaran nan ya mamayemu haka da sauri ashe kwantan ɓauna yayi mana!'Baffa Hashir da tunda aka fara maganar baice komaiba ya ɗan numfasa kana cikin yanayinsa nagirma yace"duk Habibu ne ya cuce mu da ya kawo mana jafar cikin ahlin mu,abunda ya ke ɗauren kai kuma bai wuce abinda ya haɗamu da wannan yaron ba ban san dalilin da yasa yake son tona mana asiri da kuma ƙoƙarin san yaga ya dakatar damu daga cikar burinmu ba,Alhaji Kabir da shima har lokacin bai ce komai ba ya ɗan gyara zaman sa kana yace"Ni ina ganin sashi akayi saboda idan kukayi la akari da cewa bamu kaɗai ne masu nema A duhu ba A kwai waɗanda mu bamu san su ba wata ƙil kuma su sun san mu kuma sun fimu shiri shi yasa suka haɗa da hannu da wannan shu'umin yaron!'amma kana ganin Abdallah zai iya amincewa A haɗa baki dashi dan cutar da BALARABE? cewar Alhaji Nasir kenan, Baba Nura yace kun san tunanin da nayi? duk suka zuba masa ido suna sauraran sa,ganin sun bada hankalin su gareshi yasa yace" bakwa zargin da haɗin bakin Habibu cikin wannan al'amari? Baba Nura yace tabbas ka kawo zance mai ma'ana kasan kuwa irin kallon zargin da Habibu yake yawan yi mun idan zama ya haɗamu?kuma ina zargin Habibu yana bibiyar mu dan duk cikin ƴaƴan Baba Alhaji yafi nuna masa tattali da ƙauna,kuma shi kaɗai ne halinsa yake daban da sauran ƴaƴan Alhaji Baba,dan ina ganin daga Abubakar sai Habibu A yaran sa masu tsananin ƙaunarsa da nuna kulawa A kan sa,dan haka babu haufi idan ance Habibu yana ƙoƙarin ganin ya kare mahaifinsa daga komar maƙiya!'dukkan su sun gamsu da wannan bayani na Baba nura kuma suna ganin A kwai ƙamshin gaskiya,Alhaji Salisu yace yanzu dai mu jira bayani daga wajen ɗanleƙen asirin mu idan yaso duk bayanan da ya bamu sai mubisu mu shirya tsari na gaba!' da wannan shawarar suka samu matsaya A tattaunawarsu,
Tsaye take ta juya bayanta, fuskarta kamar ko da yaushe sanye take cikin liƙabi,magana takeyi amma kana jin maganar kasan ba itace ainahin Muryar mamallakiyar me maganar ba,cikin kaushin lafaxi take jaddada rantsuwarta ga Dije, wallahi wallahi Dije duk ranar da kika