Showing 81001 words to 84000 words out of 134378 words

Chapter 28 - TUMUN DARE COMPLETE HAUSA NOVEL

28 Oct 2025

85

komai ba, ko ruwa ta sha sai ta ji jiki. Ganin jinyar ta saka ta gab a yasa ya tausaya mata ya kai ta chemist. Bayan lissafo symptoms ɗin da take ji mai chemist ya ba ta PT-strip ya kuma mata bayanin yadda za ta yi, ya kuma faɗa ma mai gidan yadda in sun gani za su gane akwai ciki ko babu. Bayan sun koma tayi gwaji, gwaji ya tabbata cewa ciki ne da ita. A haka dai ta ci gaba da rayuwar har lokacin laulayin ya wuce ta ci gaba da rayuwa a gidan mijin nata.

Haihuwarta ta fari ɗa namiji ne, bayan suna ta buƙaci ya kai ta gidansu yace mata a'a, da ta matsa sai ya faɗa mata gaskiyar cewa ba a san takamaiman ina iyayenta suka koma da zama ba, daga ƙarshe tace don Allah ya kai ta, bayan ya tuntuɓi uban gidansa da zancen yace babu damuwa ai, shine mijinta ai. Ranar da suka je suka ga wayam tun daga ranar Rahama ta fara nadamar rayuwarta da tayi a baya, ta san ba komai ba ne, haƙƙin Hamra ne kawai ke bibiyarta. Ta yi kuka kamar ba gobe tana roƙon ubangiji ya yafe mata. Hamidu na gefenta yace "Ai Allah ba ya yafe haƙƙin wani Rahama, amma na ji daɗi da kika fahimci gaskiya, ki ci gaba da addu'ar Allah ya bayyana Miki su Inna, daga nan ki nemi yafiyar Hamra da kika cutar a baya."
Hawayenta ta share tace "In Allah ya yarda, idan Hamra ba ta yafe min ba na sani ba zan yi kyakkyawan ƙrdhe ba sabkda na muzguna mata ba iyaka, sai dai duk ruɗin shaiɗan ne da kuma Inna da Baffa, gaskiya sun cutar da rayuwar Hamra fiye da Ni, sun kuma cutar da Nima ta hanyar saka min mummunar aƙida irin tasu, Allah dai ya yafe min."
Nan dai Hamidu ya yi mata ɗan wa'azi a iya saninsa sannan ya rarrashe ta, daga nan kuma sai rayuwar ta sauya, shekara na zagayowa sai ga Rahama da wani ciki. Cikin shekaru huɗu yaranta huɗu rus! Ga ɗawainiya ga kuma tsadar rayuwa da rashi, kafin me idan ka ga ga Rahama ba lallai ka gane ta ba ta zama kamar wata tsohuwa, yaran nan kuwa duk abun ƙyama saboda yanzu ba ta gyara su ma ake ba, ta abun da za a saka a bakin salati ake yi.

Wannan a taƙaice itace rayuwar da Rahama ke yi.

*Dawowa cikin labari*

Wani daga cikin magabatan ƙwarai yace, idan mutum ya saba da tashi sallar asuba to duk rintsi zai ke tashi da zarar lokacin ya yi sai dai kuma in ya tashi baccinsa ya ribace shi ya kasa yin sallar akan lokaci, tabbas wanda asuba ba ta wuce shi ya godewa Allah, don munafukai ba sa iya kiyayeta, da asuba Hamra ta tashi, kallon ɗakin da take ciki ta fara tare da mamakin ko ina ne? Me kuma take yi a ciki? A hankali ta fara tariyo abun da ya faru da ita a daren jiya, take ta runtse idanuwanta ta ƙara buɗe su kan jakarta da ke ajiye kan wani stool, a hankali ta shafa fuskarta zuwa jikinta sai kuma ta ji kamar mutum a gefenta, numfashi kawai ta sauƙe tare da fara ƙoƙarin sauƙa ƙasa, bin ko wace kusurwa tayi da kallo, bayan ta hango ƙofa kai tsaye ta nufe ta, a bayin kuwa ta tsinci kanta. Alwala tayi ta fito tana zazzare idanuwa, Prayin mata ta gani shimfiɗe can kusa da write closet ɗin da ke ɗakin, hamadala tayi da ta ga Hijabi a kai. Sakawa tayi tayi sallah, bayan ta idar ta koma kan bed ɗin ta kwanta da har lokacin bacci take ji.

Around 6am Ra'isa ta farka, bayi ta faɗa ta yo alwala tayi salla, tana idarwa ta fara tunanin tashin Hamra ko me ta tuna sai ta bar ta. Tana zaune tana haɗa handouts ɗin da za ta fita da su yau Ammiey ta yi sallama tare da shigowa, da sauri Ra'isa ta miƙe tsaye ta ƙarasa kusa da ita tare da ba ta side hug. "Barka da safiya Ammiey" ta furta cikin harshen larabci.
"Barka yarinyata, ya baƙuwarmu? Ba ta tashi ba har yanzu?"
"Eh Ammiey, ba ta tashi ba, ga ta nan tana bacci." Shiru tayi can kuma tace "Ammiey kada a tashe ta, tana buƙatar huhu sosai."
Ammiey tace "Haka ne, ba dai school za ki fita ba?"
Idanuwanta ta juya tare da faɗin "Ai dole na yau na fita, akwai important tests da ba na so nayi missing."
Ammiey tace "To Shi ke nan, amma da na so ki zauna tare da ita ne, ba na so ta farka taga babu kowa a kusa da ita."
"Laa kin ga Ammiey ta ma tashi, in tayi breakfast kawai sai ki zauna da ita. She really needs someone close to her, Ina tsoron ciwon damuwa ya kama ta, ki ga fa yadda jiya tayi, Ni ta mugun tsoratar da Ni."

Numfashi Ammiey ta sauƙe tace "Shikenan. Ki zaɓar mata kayan da za ta saka kafin Ɗan'uwanki ya kai ku ta zaɓo nata."
"Māshin!" (Ok) Ra'isa ta faɗa tare da komawa wajen Hamra da jikinta ya mata nauyi Ammiey kuma ta juya saboda yadda fuskar yarinyar ke tuna mata da ƴar'uwarta Hibbatullah. Ra'isa ta kalli Hamra cike da kulawa tace "Ukhty kin tashi? Yaya jikin ki?"
Sakaka tayi tana bin Ra'isa da kallo kamar ta ga TV yayin da zuciyarta ta fara haƙaito mata wasu moments na rayuwarta ta baya, anya kuwa dai ba mutuwa tayi ba ta haɗu da Mom ɗinta? If not mutuwa then Mom ɗinta ba ta mutu ba ashe?






*React and share fisabilillah.*

Tap the link below to follow my TIKTOK account.*

https://vm.tiktok.com/ZSkBnbLM9/


_In a world where fate can seem sealed, one young woman's journey proves that destiny can be rewritten. Meet Hamra, a resilient orphan who faces unimaginable challenges, only to discover her true strength and find love in unexpected places._


°•° *TUMUN DARE* °•°
_(True life story)_
_Path made, fate sealed_
*© FATIMA ADAMU HASSAN*
*Diamond Bhatool 🦋*


*® 🌙 Moonlight Writer's Association 🌙*
_We shine all over the world_

https://www.facebook.com/profile.php?id=100094397072466


*CHAPTER TWENTY SIX: opportunity escaped.*

*El-Mubeen's mansion, Victoria Island , Lagos State.*

Bayan CEO Mubeen ya daidaita parking Nihla ta fara ƙoƙarin buɗe ƙofar fita sai dai ya riga ta yi locking. Kallonta ta mayar ga mahaifin nata tana zumɓura baki, cike da shagwaɓa ta kira sunansa "Abieee" tare da jan ƙarshen sunan, shima dai fuska haɗe yace "Ba dai kin raina Ni ba Angel? Mu je ciki, i'll make sure that I teach you a lesson."
"Abie" ta ƙara kiran sunansa sanin ba za su wanye ƙalau ba in ba ta nemi sulhu ba. Cikin halin ko in kula da ya arawa kansa yace "out of my car!"
"Abieee" ta ƙara faɗa sai ga hawaye na zubowa daga idanuwanta, ba tare da ya ankare ba rauninsa ya bayyana, hannunsa ya miƙa mata alamar ta sanya nata cikin nasa, babu ɓata lokaci ta yi hakan. Shafa hannun nata yayi yace "Ba dai kin fara musu da Abie ba?" Kanta ta jijjiga tana faɗin "Ka yi haƙuri Abie, ba na ƙarawa, don Allah."

Fuskar mahaifiyarta kawai yake gani a irin yanayin da tayi magana, lokaci guda ya fara tunano irin moments ɗinsu shi da Marigayiyar matarsa wacce ya bayar da zuciyarsa gare ta, duk da cewa mutuwa ta musu yankan ƙauna amma har ila yau tana cikin ransa kuma ya gagara samun macen da za ta iya maye masa gurbinta.
Nana Khadijah! His only love, ɗiyar uncle ɗinsa ne wan mahaifinsa, kyakkyawa kuma wayayyar mace wacce ta san ƙima da darajar mutane, macen da san haƙƙin aure kuma take ƙoƙarin sauƙe su, macen da take daraja dangin mijinta ta kuma kasance wacce ake ƙira da macen ƙwarai. A tsarin da ya yi wa rayuwarsa, zai rayu da ita ne har numfashinsa na ƙarshe don shi ko a tunani bai raɓa kawo cewa ita za ta tafi ta bar shi ba. Sai dai kuma, kana naka ne, ubangiji na nasa, a lokacin da ta sauya rayuwarsa ya zama mutum kamar kowa, lokacin da take shirin ƙarawa rayuwarsu farin ciki ta rasa Tata rayuwar, sanadiyyar haihuwar Nihla, idan ya duba irin rashin da ya yi sai ya ga kamar shi kaɗai ne ubangiji ya jarraba amma da ya kalli fuskar yarinyarsu Nihla sai ya ji sauƙi da raɗaɗin rashin ta wanda ya gagara koɗewa tsawon shekaru goma sha biyu ya ragu. Tabbas yana so da ƙaunar Nihla fiye da komai idan ka cire Annabinmu, mahaifiyarsa...to ita ce gaba kuma, ita kaɗai ce ke tuna masa da matarsa, sanadiyyarta ko yaushe yana cikin yi mata addu'ar rahama da gafarar ubangiji tare da roƙon Allah ya haɗa su a gidan Aljanna.

Shirun da Nihla ta ga mahaifinta ya yi yasa ta ji babu daɗi, duk da cewa ba ta san mahaifiyarta ba, amma yadda mahaifinta ke nunawa yasa ta san cewa mamarta na da muhimmanci gare shi, sau tari idan ta tambaye shi a makamantan lokutan da yake faɗawa duniyar tunani idan yana kallonta, yakan amsa mata da cewa "Ina tuna Mahaifiyarki ne!"
Sajensa ta shafa tare da ƙoƙarin samar da eye contact tsakaninsu. "Abie" ya ɗago a ɗan firgice "I'm sorry, ba zan ƙara ba." Tana faɗar haka ta ɗauke hannunta daga sajenshi ta kama kunnuwanta biyu tana jansu"Ba zan ƙara ba, na tuba."
"Kamar dai mahaifiyarta" ya faɗa cikin ransa a zahiri kuma ya yi murmushi yace "Is ok, Amma idan kika ƙara babu ruwana da ke." Kafin ya rufe baki tace "ba ma zan ƙara ba, ubana mai share min kukana"
Ƴar ƙaramar dariya yayi don shi kullum cikin sabon mamaki take sanya shi.
"Yauwa Abie, na gode, Ina son ka, a kan ka tsaf zan iya kashe ɓera.."
"You said?"
Dariya tayi ta maimaita masa "A kanka tsaf zan iya kashe ɓera..."
Shima dariyar ya yi tare da jan kuncinta yace "Let's get in, Ammiey Kar ta gaji da jira ta shiga damuwa.." ba ta ƙarasa jin mai zai ce ba ta ɓalle murfin motar ta fita tare da shigewa da gudu, ko da ya fito ya ga har ta kusa shiga ciki sai ya harɗe hannayensa a ƙirji ya bi ta da kallo yana murmusawa, ganin ta shige yasa ya bi bayanta.

Kamar yadda suka yi tsammanin kuwa, Ammiey ce sai Ra'isa a katafaren parlourn suna kallon news wanda lokacin kuma hankulansu ya bar wurin kallon ya koma ga Nihla da ke jikin Ammiey tana mata shagwaɓa.
Ƙarasawa yayi wurinsu ya zauna gefen Ammiey tare da kwantar da kansa jikinta kamar wani ƙaramin yaro, can ƙasan maƙoshi yace "Barka da gida Ammiey."
Fuska sake Ammiey ta saki Nihla ta mayar da hankalinta ga yaronta "Kun dawo lafiya?"
"Alhamdulillah Ammiey."
"Ma sha Allah, sai ka yi wanka za ka ci abinci ko kuwa?" Yamutsa fuska ya yi yana faɗin "Bari dai na fara wankan."
"Ok, Babu damuwa."
Jim ya yi shiru yasa Ra'isa da ke danna laptop ɗinta ta mayar da hankalinta ga yayan nata tace "Masā'ul khair akhy."
Kamar ba zai amsa ba can yace "Masā'ul ward, kaifa yaumuki?"
"Bikhair...."
"Māsha Allah." Daga haka kuma bai ƙara cewa komai na. Ƙwalla kiran maa'aikaciyar gidan Ammiey tayi sau ɗaya "Taqiyya!"
"Na'am Sayyidaty" ta amsa daga madafar abinci tare da ƙarasowa parlourn, kanta ƙasa ta miƙa gaisuwarta cikin harshen Hausa ga CEO Mubeen kasancewar ta san bai fiye son yin larabci ba kamar mahaifiyarsa. Amsa mata yayi daga nan ya miƙe ya bar wurin, ganin haka yasa Taqiyya kiran Nihla don watsa mata ruwa...kamar dai yadda take ɗawainiya da ita.

Bayan sun bar wurin Ammiey ta murmusa. A tare suka fito kamar haɗin baki, Dining kai tsaye ya nufa, Ammiey ta yi wa Ra'isa alama ta hanyar taɓa ta, bayan ta Yi serving ɗinsu kuma ta dawo ta ci gaba da abinda take. Har suka gama ci babu wanda ya ce uffan sai hamdala, daga nan suka dawo cikin family ana surutu wanda duk Nihla ce da Ra'isa ke jan ragamar hirar sai kuma Ammiey da ke tsoma bi lokaci bayan lokaci. Kamar wanda aka tsikara Nihla ta duni Ra'isa tace "Ammiey Ra'isa..."
Ɗago kanta tayi tare da ɗage mata gira
Mayar da kallonta ta yi ga Ammiey ta ƙira sunanta itama "Ammiey"
"Ina jin ki Nihla"
"Dama can ashe ba iya Ammiey Ra'isa ce kika haifa ba ashe su biyu ne????"
Jujjuya maganar Ammiey ta fara jin wani batu da Nihla ta zo musu da shi.
Jin Ammiey ta yi shiru yasa tace "Ammiey Ra'isa ashe ku ƴan biyu ne?"

Shi kansa CEO Mubeen bin ƴar tashi yake da kallo yana jiran yaji ko daga ina ta samo wannan bahagon labarin nata maras makama.
"Waye ya faɗa Miki Nihla?" Ammiey ta tambaya har lokacin fuskarta ɗauke da mamaki.
Amsa ta ba su da faɗin "Ɗazu na ga ɗayar ai, mai kama da Ammiey Ra'isa."
Gaban CEO Mubeen ne ya buga don kuwa lokaci guda ya gano wa take nufi, tabbas shima da a ce Ra'isa ce gaba da shi da zai iya faɗin kwatankwacin abinda Nihla ta faɗa sai dai shi aka fara haifa ya kuma san adadin ƴaƴan da Ammiey ta haifa har zuwa rasuwar Daddysa. Shiru ya yi yana jujjuya abun cikin ransa tare da dakon amsar da Ammiey za ta bayar. Jin Ammiey ta yi shiru yasa Ra'isa kiran Nihla ta dawo kusa da ita tare da kunna mata cartoon a system ɗinta, wannan ne dalilin shashantar da zancen saboda can dama ba shi da wata mahanga ko direction.

*Washe gari*

Bayan Hamra ta yi sallar asubahi ta yi maza ta yi azkar da ƴan addu'o'inta tare da neman sa'ar ubangiji wurin samun wannan aiki da take nema. Bayan gari ya waye kuma ta nufi cikin ma'aikatar sai dai ba ta samu dama ba saboda an sanar da ita cewa committee na masu ɗaukar aiki suna gab da fitowa da sanarwa ta ɗan jira.

Tun daga wannan rana ta mayar da masallacin kamar ɗakinta, a nan take bacci amma kuma sosai ta samu damar samar da kusanci tsakaninta da mahaliccinta, sayan abinci ne kawai ke fitar da ita daga masallacin. Tsawon kwanaki huɗu tana zaune a El-Mubeen Luxuries ba ta ƙara haɗuwa da CEO Mubeen ba, haka zalika Nihla, yarinyar da taji tana ƙauna lokaci guda har take jinta tamkar jininta. A rana ta biyar Nihla ta biyo ta ma'aikatar bayan ta sa driver ya kawo ta direct daga school wai ita a motar Abie ɗinta za ta koma gida. Tunda suka haɗu suke surutu sai dai yau cikin Sa'a ta hango CEO Mubeen tahowa, tana ganin haka ta yi wa Nihla sallama ta koma masauƙinta. Bayan su Nihla sun tafi, tun a mota ta fara damun Abie ɗinta akan ya ɗauko musu Ammiey Hamra ta dawo gidansu da zama, sai dai banza ya mata ba tare da ya ce komai ba.

Alhamdulillah, cikin Sa'a da ikon mai duka, Hamra ta fito sallar azahar ta ga takarda nanne jikin wani notice board da ke kusa da masallaci na cewar Ranar Litinin za a yi tantancewa don ɗibar sabbin ma'aikata, a wurin ta yi sujjada ta godewa Allah, dama fargabarta ba ta wuce rashin kuɗi ba, gaba ɗaya kuɗaɗen da ke wurinta sun ƙare ta ma rasa yadda za ta yi ta dai miƙa komai ga Ubangiji,ga shi kuwa ya isar mata. Ranar Litinin kuwa ta fitar da WAEC result ɗinta ta shirya, ƙarfe bakwai ta fita tare da tambaye wasu mutane venue ɗin da za a yi interview ɗin wanda ta riga ta haddace a jikin takardar sanarwa. Tabbas ta sha mamaki kam, ashe sashen da take admin block ne, ba komai ba ne daga EL-MUBEEN'S LUXURIES... Don kuwa wurin da aka kaita har sai da ta ji tsoron neman aiki a wannan wuri don gani take kamar ya fi ƙarfinta. Tabbas El-Mubeen Luxuries ba ƙaramin Company ba ne da ya yi fice a fannoni da dama da suka shafi ci gaban zamani sai dai sun fi fice a ɓangaren samar da kayayyakin more rayuwa da zamani ya zo da su, motoci da sauran machines da ke sauƙaƙawa mutane aiki. Akwai sashe na musamman da suke zane, zanen motoci waɗanda ba a taɓa ƙera irinsu ba, waɗannan zane da suke yi kuma ba kara zube ake yi ba, sai an tsara yadda wannan mota za ta kasance tun daga kan injinta da kuma wata siffa ta musamman da wasu motocin ba su da su. A cikin El-Mubeen Luxuries akwai sashen da suke yin takalma na ƙasaita da kuma gama gari, akwai sashen da ake kaya...in nace kaya ina nufin English wears. Daga haka ya isa ku yarda cewa El-Mubeen is luxurious industry.

Bayan kowa ya bayar da takardunsa, sakamakon wadatattun ma'aikata a take aka dudduba, aka kuma zaɓi kowa a ɓangaren da ya cancanta, alhamdulillah, Hamra ma ta samu a ɓangaren share-share da goge goge amma a sashen admin block. Bayan orientation da aka musu ne ma ta fahimci cewa aikin ba wani yawa ne da shi ba amma kuma akwai kyakkyawan payment. Murna sosai Hamra ta yi tare da yi wa Ubangiji godiya, addu'o'i masu kyau kam Yaya Hamid da Ummie sun sha ta, daga nan kuma ta koma masallaci kamar yadda ya zama masauƙinta. Washe gari Hamra ta fara aiki, tsawon sati gana aiki amma kuma ba ta taɓa haɗuwaa da CEO Mubeen ba, hasali ma takan share shashensa ne wanda yake da ɗan girma kaɗan kafin zuwansa ta kuma jera komai tsaf-tsaf.

Haka rayuwar ta ci gaba da tafiya mata har tsawon wata guda har ranar kuma ba ta ƙara ganin Nihla ba, hakan kuma ya sa ta ji babu daɗi don kuwa yarinyar ta mugun shiga ranta ne fiye da tunaninta. A yau bayan ta kammala ayyukan ta tana shirin komawa masallacin ta jiyo Muryar Nihla na ƙwala mata ƙira, da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login