Showing 36001 words to 39000 words out of 149166 words
Uncle Zaid ko kallona fa beyi ba, Hamma da kullum ya ganni burinshi ya takura min, ya nemi tsokana na, tunda na tafi Kd be kirani ba, idan na kirashi beya dauka, and yanzu kuma na dawo irin welcome din da zai min kenan? Ko kallo ban ishe shi ba? Ina mai magana ko tanka ni beyi ba? Uncle Zaid ko wani abu yace "na mishi?" da sauri Rafeeq ya rungume kanwarshi ya na kuka itama tana kuka ama ya kasa ce mata komai, sun ba Zaid tausayi, da sauri ya rabasu yace "fee'ah tashi ki shiga ciki" ba musu ta fita daga dakin tayi sama, Zaid ya kalli Rafeeq, yace "if you really dont want her to find out, then be yourself" yana kaiwa nan ya kabbara Sallah don ya san bazai samu amsa daga bakin shi ba. Yana idar da Sallah ya kalli Rafeeq yace "muje cikin Gida" Rafeeq ya dago ido ya kalleshi zaiyi Complain amma maganar ta mai nauyi, Zaid yace "ina jiranka" yayi gaba ya bar shi Zaune be da niyyar motsawa".
Aunty Yaushe Mami Zata dawo? Kafin Sauda tayi magana Zaid dake shigowa Parlorn yace "nace miki sai taji Sauki, Dr ya bata bed rest, soon zata dawo" ya karashe maganar yana me kallon Sauda yana mata inkiya da ta goyi bayanshi, sai a yanzu ta gane dalilin da yasa dazun Rafee'ah ba tace ima mamar ta ba, wato sun boye bata, aiko ba zai sabu ba, sai ta samu hanyar fallasa mata. Zaid yace "Aunty ina Yaya?" tace "yana nan Office in kusa da dakin shi" Zaid yace da Rafee'ah "ki shiga ciki ki kwanta ki huta" ta mik'e ta nufa daki. Sauda tayi Parlorn Alhaji Habib, Zaid ya rufa mata baya.
Yana zaune, Zaid ya gaishe shi, Alhaji Habib yace "Engineer har an iso? Ya hanya? Ina aka tsaya ne sai dai na ga shigowar yar gidanka? Zaid yace "Alhamdulilah, Ina Dakin Rafeeq ina Sallah" Alhaji yace "hmm lamarin Rafeeq sai gaba yake k'arayi, bansan me na mishi ba" Zaid yace "ba ka mishi komai ba, lokaci kawai yake buk'ata maganar shi ce ma nake so muyi" kamar an jefo shi ya shigo parlorn, yayi Sallama amma Zaid kadai ne ya fuskancin Sallama yayi, ya samu wuri ya zauna kusa da Zaid, Zaid ya tsura mai ido yana mai nuni da ya gaida Mahaifin shi da Auntyn su, fuska yayi yaki kallon side dinsu. Zaid dai ya san bazai tanka ba ya juya ga yayan shi yace "Rafeeq dama na kiraka ne nan gaban Ubanka mahaifi, shawara zamu baka, ba mu da gatan da zamu maka da ya wuce Addua da Shawara, kai Baligi ne kasan ciwom kanka, kasan abun da yake daidai kasan wanda ba daidai ba, kasan fari kasan bak'i, Rafeeq Abun da ya faru ina so Ka dauke shi a matsayin kuskure, Kaddara, ka rungume kaddararka, Kai musulmi ne, ba wai nace ka yafe ma mahaifiyar ka bane, so nake ka gano gaskia ka gane kurenka dukda ba laifinka bane, shisa kaga na daina takura maka da maganar ta. Alhaji Habib da matarshi dai ba su ce komai ba Zaid ya cigaba da cewa " Well this is not about your mom. Its about you, ina so ka maida hankali ka fara last semester din nan naka da kyau, yanda kowa ke Alfahari da kai kar ka bamu kunya, kamar yanda kake yi da, make us proud like always, ka fita da first class dinka that you truly deserve kajih?" Rafeeq kallon window kawai yakeyi, be tanka Zaid ba.
Don dai ya sa Rafeeq Farin ciki Zaid yace "kuma zan siya maka mota son ranka, ka fadi wanda kake so Gobe ka ganshi a gidan nan" nan ma be ce komai ba, Hakan yasa Alhaji Habib yace "toh nima Uncle din Yara baza a barni a baya ba, nima ina da kyautar da nakeso in ma Rafeeq" ya mik'e ya fita duk suka bishi da ido gaban Sauda ya fadi tana ta tunanin meye kyautar da Alhaji zai ma Rafeeq, Jim kadan sai gashi ya dawo da wasu files ya zauna, yace "Sauda da Zaid kuyi shaida, Kafin a samo Shaidu, Companyn Tie and Dye na Sokoto, da Hide and Skin na Keffi na Mallaka ma Rafeeq, ko na mutu ba su a cikin Gado, kuma da ka gama Service, komai na other Companies dina zasu dawo k'arkashin ku kai da Rafee'ah, Zaid ya washe Bakih yace kai MashaAllah, Angode Allah ya k'ara girma" Sauda kuwa Ba tasan duniyar bakin cikin da ta lula ba, kiris ya rage ta fashe don ta kumbura, ta kasa boye bakin cikinta da hassadar ta.
Amsa Rafeeq, Alhaji ya miko mishi Files din, Zaid ya mai Alama da ya amsa, kamar ba zai karba ba ya sa hannu ya amsa a hankali yace "nagode" Daddy yace tashi kaje ka adana. Kamar jira yake ace yatashi ya tafi ya mik'e da sauri, Files din ya mik'a ma Zaid, Zaid ya sa hannu ya amsa, yana bashi ya fita daga Parlorn. Zaid ko Farinciki yake tayi. Sauda kuwa ta na hada hanya don ta daina gani saboda bakin ciki ta fita.
Daki ta fada ta fashe da wani irin ihun takaici, ta daura hannu a kai, na shiga uku, Alhaji har ya fara rarraban kamfanonin ka? Be sakani cikin lissafi, wato daya gama Sabis zai maida komai karkashin sa shi da kanwar shi, ni kuma da tawa diyar oho, wallahi ba zai sabu ba, sai inga ta inda zai gama makarantar balle yaje service din har ya zama wani tsiya , ita kuma Rafee'ah sai ta tsani kanta, don boka na kan tudu zan sa ya Sa Rafeeq ya mata Fyade, ko kuma ta zama karuwar Yayanta, sai in ga ta inda zasu zama abun Alfahari ga mutane. Sai kowa ya tsanesu, shima Alhaji ya tsine musu ya koresu daga gidan shi, su shiga duniya, sai ya rage daga ni Sai diyata sai muci karenmu ba babbaka ta sa shewa kamar wata zararriya da sauri ta ciro wayarta ta latso number Boka na kan tudu ta labarta mishi plan dinta. Yace "Saude wannan magana ba ya waya bace ki zo Gobe kawai sai a duba" tace "to na kan tudu, ka tsumayi zuwa na gobe, da Asubar fari zan taho".
_Bibilicious Biebee_
👧🏽KE ALHERI CE
NA
BIEBEE ISA
® NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)
Pg2⃣8⃣
As promised, This page is for you Aunty Baraka❤❤❤
Washegari Alhaji Habib yace da Sauda zata raka shi Kano, haushi kamar ya kasheta don tayi niyyan zuwa gun boka na kan tudu yau, haka suka tafi Kano ba don taso ba.
Rafee'ah ta rada ta inda zata bullo ma Rafeeq, don har yanzu bata san damuwar shi ba, da ta matsa ma Zaid sai ya gaya mata, sai yace mata "zaifi kyau ki taya shi da addua, Shi kadai yake bukata, kar ki tsananta Bincike you might end up hurting yourself" haka Rafee'ah ta cigaba da shishige ma Yayan ta ko zata samu ya dawo yanda yake a da, amma shiru ba cigaba, haka zata karashe surutun ta ta barshi, duk yanda yake so ya dan dinga kula Kanwar tasa hakan ya faskara, abun ya zame mishi jiki, Yanzu magana ya zame mishi wani gagarumin Aiki, da Zaid kadai zakaji yana magana, shima be wuce ya bishi da kalma biyu ko uku ba, abun Rafeeq ya wuce Miskilanci, don abun yayi k'amari har ace be iya shiga cikin Gidansu ya ci Abincin da Matar Uban shi ta dafa, kai ko daki aka biyo shi dashi be ci haka zai bar musu shi inda suka aje mishi shi, Be cin abincin Gidan su kwata kwata, sai dai yaje gun me indomie ya sha shayi, da Zaid ya lura da hakan sai ya siyo mishi Cupcakes,Biscuits Shortbread da Drinks kalakala ya ajiye mai a daki tunda yana ganin asaran cin Abincin Gidan su..
Da kyar Maalesh ya sa shi shirin Makaranta, ba don yaso ba, sai dai kawai baya so su tsaya gardama da Maalesh, ya shirya suka wuce School, tunda suka isa Sciences aka zagaye motar Maalesh, Maza da Mata kasancewar R-Lema na kowa ne, Maalesh yace "Guy, dole ka fa sake fuska, mutanen ka na jiran fitowar ka" be kula Maalesh ba sai ma dauko wani Bakin Gilashi irin no respect din nan ya k'wama a fuskar shi, ya bude Kofa ya fita, ji kake ana R-Lema, ko kallo basu ishe shi ba, tafian shi kawai yakeyi, burin shi ya ganshi a Class, duk suka bishi da kallo suna mamakin wanna Shariya na R-Lema, sai duk suka maida kallo ga Maalesh, Maalesh ya shiga raba idanu kamar yayi K'arya, da k'yar yace "kuyi hakuri, R-Lema na da dan damuwa ne, ky tayashi da Addua". Mutanen kam suka jinjina kai, da alamu kam, don ba haka suka saba ganin shi ba, shi mutum ne mai son jamaa, da da ne, da ya fito zai dinga ba mutanen nan hannu suna gaisawa, ya dinga jan tsokanan yan matan nan, ana wasa ana daria, lallai dole suke tayashi da addua Allah ya yaye mishi damuwar shi.
Ai ba Daliban ba, harta Mallamai sun san da Chanjawan R-Lema, yanda kasan hoto haka yake zaune a aji, ba motsi, ba kamar da ba, kafin Lecturer ya gama tambaya har ya bada amsa, amma yanzu ko sun tambaye shi shiru zakaji yayi, bawai be gane abun da ake koyar dashi bane, tsaf yake fahimta kamar kullum, abunda yake ganin asara shine ya bude baki yayi magana ko ya bada amsa, yana jin kuiwar magana, kwanaki da ya ba wani Lecturer haushi koran shi yayi a aji, don ya dinga mishi magana jo tak Rafeeq be ce mar ba, abun ya ba mutumin haushi ya kore shi, sai da Maalesh ya je ya sanar da Level Coordinator dinsu, kasancewar Coordinator abokin Zaid ne, Yazo ya bada hakuri, yace yayi hakuri Rafeeq is Mentally Sick, yayi considering dinshi tunda kowa yasan ba haka yake a da ba. Da haka aka rufe bakin lecturers, ko sunzo ba sa tambayan Rafeeq don sun san ba tanka su zaiyi ba.
Duk nacin da Yanmatan Rafeeq keyi don ya kulasu haka suka gaji suka hakura, don ko sun fi k'uda k'wak'wa iskar da ya debo su Rafeeq be kallo, Cafteria da da ya maida shi Gidan Uba, a rana sai yaje so nawa, yaje ya siya ma yanmata abinci, yanzu kuwa ko kallon hanyan beyi, in ka ganshi cikin Makaranta yana aji, da sun gama lectures be kara ko minti zai bar ajin don be son surutu, Chan bayan Labs inda ba ka ganin kowa yake zuwa ya zauna shi kadai. Haka Rayuwar shi ta cigaba da tafia..
Duk Yanda taso ta kebe ya je gun bokan ta Alhaji Habib ya toshe, be bata damar zuwa ko nan da chan ba, ko ina zaije da ita yake zuwa, be barin ta ita kadai, ta rasa yanda zatayi, haka dai ta hakura har suka karaci kwanakin su a garin Kano.
Bayan Sati Uku
Sauda ta kalli Boka cikin kunan rai tace "ya zaka ce min hakan ba zaiyiwu ba? Meye ba zaiyiwu ba? Kaine fa kake share min hawaye na, kai ke biya min buk'atu na"(Waiyazubillah, ya mu Mata, mu kula, mu lura, aikin Boka na tasiri ne da Yardar Ubangiji, Boka be Isa Ya biya mana Bukattun mu ba. Allah sa mu dace). Ta yaya zan ce maka ga abun da nake so kace min ba zaiyuwu ba? Kasan taya na bar Katsina na zo nan? Ni yanda nake so haka zaayi, Kawai Rafeeq nake so ya fyade kanwarsa". Boka yace "Saude kar fa ki manta, duk aikin da kike samu muna miki shi yanda kika buk'ace shi, tunda kikaji nace wannan bazaiyuwu ba toh ki hakura da wannan, amma na riga na biya miki dayan bukatar hana Yaron Gama Makaranta" Sauda ta katse shi ta hanyar cewa "yo ni raba ni da wata makaranta, yo ya gama ina ruwana, ni buk'ata ta shine Alhaji ya tsine musu duka, kai ni ban k'i su mutu ba" Boka yace "Ke Saude saurareni kiji, jijsan aiki na kamar yankan wuk'a yake, ba wanda ya kaini aiki me kyau, na hango miki gaba ne, duk wanda zai ce miki ki bashi kudi ya miki Aiki kan Mijinki akan 'ya'yansa, to nayi imani kudinki kawai zasu ci, ba wani mugu a doren k'asar nan da zai iya hada Mijinki da Yaransa ba, wai shin baki san so da ke tsakanin d'a da mahaifi ba? Kar ki ga kinci nasara kan Matar shi, kice suma zaki ci nasara, Saude shawara zan baki, idan kika matsa kan hakan, to Asirin ki na Gaf da tonuwa..
Sauda ta k'ule matuka, ta mik'e cike da Masifa, tace" kai na kan tudu, kar ka cika ni da wannan soki burutsun, ai baka gaya min Imani ya fara shigan ka ba, idan ka tsufa baka iya biya min buk'ata ta sai ka sanar dani, bawai ka dinga ce min hakan bazaiyiu ba? Ba ka k'ara gani na nan, zanje in samo wanda zai iya min abun da nake so" ba ta jira amsar shi ba ta fice daga Bukkar.
Cikin Kwanaki 20 Saude ta zabure sosai, duk inda ta san zata samu bokaye ta bi, burinta Rafeeq ya lalata ma Rafee'ah Rayuwa, sun san aikin da ta ke so a mata ba me yiwuwa bane amma sunk'i gaya mata sai dai su ce mata taje Gida zata ga aiki da cikawa, haka zata dawo gida tayi ta jiran tsammani, shiru takeji, sai ma wani Gatan da Alhaji yake k'ara ma yaran sa, haka zata chanxa wani boka, Bokaye kuwa sai cin kudinta suke yi, da ta gano su dai tayi watsi da dukkan su ta zauna gaban Madubi ta na kallon kanta tace "Haba Saude, sai kace ba mace ba, idan Plan A yak'i ci, sai a gwada Plan B, Wato K'issa" ba Bokan da zai k'ara cin kudina, cikin ruwan Sanyi zanyi maganin ku Rafeeq da Rafee'ah..
Bayan Wata Daya
Karatu suke kain da nain, Rafeeq ya dage da Project dinshi, be kula kowa yake abubuwan shi, kwanaki kadan ya rage su fara Final Exams, Rafee'ah har ta saba da Shariyar Rafeeq, itama tana ta karatun ta cikin kwanciyar Hankali, Babban Tashin hankalin ta Mamin ta, ta fara gano akwai wata makarkashiya, duk wanda ta tara da maganar mahaifiyar ta sai yayi shiru, har takanas taje gidan Kakanin ta don tambayo idan Mahaifiyar ta take, amma bata samu amsa daya k'wak'wara ba, sai hanya hanya suke mata.
Yau tace InshaAllah dole sai ta gano gaskiar inda Mahaifiyar ta take, Bayan ta dawo School ta nufa dakin Aunty Saude, ta tura kofar da Sallama, Sauda daga ciki tana waya da Meema da Aneesa tayi saurin latse wayar tana addua Allah ya sa Rafee'ah bata ji me take fada ba. Ta amsa mata sallamarta, "Rafee'ah sannu da zuwa kin dawo?" "eh Aunty ya Gida?, kina da lokaci? Akwai maganan da nake so muyi" Sauda tace ohh Rafee'ah, barin yi Sallah sai inzo muyi magana ko? Rafee'ah tace toh, nima barin shiga in watsa ruwa".
Sai da tayi wanka tayi Sallah ta fita parlorn k'asa, Saude ta sauko itama, tace "Rafee'ah, har kin fito? Tace "eh Aunty i'm just eager to talk to you", Saude tace "tohfa, what's it about?" Rafee'ah ta rik'o hannayen Saude guda biyu ta zaunar da ita, tace "Aunty, donAllah ina so ki gaya min gaskia, duk wanda na tambaya baya bani gamsashiyar Amsa, ki taimaka ki gaya min, ina Mami na take? Na kusa wata 3 daga dawowa na da kaduna, ba labarinta, kar kuna 6oye mun wani abu, please ki gaya min".
Cike da makirci Sauda ta fashe da kuka, nan da nan Rafee'ah ta rikice "Aunty me ya sameki? Ko dai Mami na mutuwa tayi?" Saude cikin kukan munafurci tace" ko daya Rafee'ah, zan gaya miki abunda na sani game da Mamin ku, amma kar ki ce ma kowa ni na gaya miki don ba sa so ki sani" Rafee'ah ta gyara zama tace "InshaAllah" Sauda ta kara sautin kukan ta, tace "Rafee'ah, ashe maminku yar iska ce? Ashe Magajiya ce uwar karuwai? Kwarto ta kawo cikin dakin auren ta, Kwartu--" bata k'arashe zancenta ba taji an sauke mata wasu kyakyawan mari biyu, a zabure ta dafe kuncinta, ta daga idanuwan ta taga Rafee'ah tsaye tana huci kamar Zakanya, Sauda ta dago a fusace, tace "Rafee'ah, ni zaki mara? Don na gaya miki gaskia? Don ma ban gaya miki gaskian lamarin ba? To kwance a ka ganta haihuwar uwarta da gardi" Wasu Mari ta sake ji an sake mata wasu na bin wasu, Mamaki ya rufe ta, tabbas ba Rafee'ah ce tayi marin nan ba, kafin ta ankara taji muryan mijinta Alhaji Habib cikin daga murya yana cewa "Rafeeq, dont, kar ka sake taba ta" Rafeeq beji ba illa ma dunk'ule hannun da yayi zai kai mata nushi, da murya karkausa Uncle Zaid ya kira sunan shi "Rafeeeeq".
_Bibilicious biebee_
👧🏽KE ALHERI CE 🙇🏼♀
NA
BIEBEE ISA
® NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)
Pg2⃣9⃣
Fasa nushin ta Rafeeq yayi, ya sauar da hannu yana ajiyar zuciya, Zaid ranshi a bace, be ji dadin abun da Sauda tace game da Mami ba, k'ila da shi ke kusa da ita da ya karairayata, Alhaji ne yace cikin fada"ke ma dai me yasa kika gaya mata? Tun farko Zaid ya nema Alfarma gun mu yace kar a gaya mata, do u want to break her? Bakiga yanda abun yayi affecting Rafeeq ba? kinsan zai yi affecting dinta, maybe worse than Rafeeq, u shouldnt have told her" Sauda ran ta ya gama baci, amma ganin Mijinta da Zaid tsaye ya sa ta fara kukan munafurci, tace "Haba Alhaji