Showing 39001 words to 42000 words out of 149166 words

Chapter 14 - Ke alkhairi ce COMPLETE HAUSA NOVEL

BIEBIE   

22 Oct 2024

25719

kasan ba zan taba yin wani abun da zai cutar da su ba, ina son su kamar ni na haife su, Rafee'ah ce ta titsitsiyeni da tamabayoyi.

Rafee'ah ta sake ihu dakata " Daddy, Uncle Zaid, Hamma, wai me ke faruwa? Bana fahimtar komai, tell me this is not true, ku fahintar dani, ku ce mun Sharri aka mami na" kuka takeyi sosai, kamar ranta zai fita, Rafeeq ya rikota, yace "kiyi hakuri Rafeeah, shiyasa tun farko ban so a sansr dake, coz nasan cewa u'll be broken" ta dan zabura kadan, ta ma rafeeq wani kallon da be taba ganin ta mai ba, tace "Me kake so kace? Ka yarda da sharrin da aka ma mami? Ashe wayon banza ne dakai?" Da sauri ya kalleta don be tabajin irin maganar nan daga bakinta ba, sam be ji haushin ta ba, yace "Rafee'ah, i saw Mami with my eyes" da sauri tace "you must be stupid Rafeeq, da ka manta who ur Mother really is, ka manta the type of woman she is, ka bari anger yayi controlling dinka, look at you now, you are miserable" Alhaji yace "Rafee'ah, ki kula da yanda kike ma Yayanki magana, beyi k'arya ba, tabbas abunda sauda ta fada miki gaskia ne, Zaid ne ya nemi Alfarman a boye miki saboda kina iya shiga wani hali a matsayin ki na mace, amma tabbas Mamin ku Kwarto ta kawo dakin aurenta, Mamin ku ta dade tana cin amana ta" tsananin bacin rai Rafee'ah ta shiga, tace "whoever believe this is a stupid idiot, wallahi sharria aka mata, makiri ba ta inda be yin makircin shi, ta daga hannayen ta sama ta cigaba *amma Wallahi Tallahi Billahi*, _da yardan Allah da izinin Allah_, _Whoever did this to my mum is going to pay for it_, _ba zan taba hutawa ba har sai na bi mata hakkinta_ *Ya Allah ko yau na fadi na mutu Allah ka bani hanyar saka wa Uwata*, *Ya Allah ka amshi addua ta ka bani iko Ameen*
Wani irin dumm Sukaji a jikin su gaba ki daya, gaba ki dayan su suka ji a jikin su wanna addua ta Rafee'ah karb'abba ce, Sauda hankalin ta ya tashi matuk'a, Zaid da Alhaji Habib bakin su ya mutu murus, Rafee'ah ta juya da gudu ta haye sama tana kuka, Rafeeq kuwa hankalin shi ya gama tashi, abun da yake gudu ne ya faru. Zaid yayi saurin bin bayan Rafee'ah.

Sauda ta dafe kanta takaici goma da ashirin, Yaran Mijinta sun mammareta a gaban mijinta amma ya kasa cewa komai? Nan gaba k'ila belt zasu sa mata su mata mugun bugu, wai har Rafeeah ta daga hannu ta mareta, Rafeeq ma haka. Tabdijam aiko sun tsokalo wa kansu tsuliyar dodo, ita kadai tasan abun da zata musu, ba shegen bokan da zai ci kudinta wanna karon da kanta zatayi maganin su once and for all, ita kadai ke ta maganar ta.

A.Habib ya shigo dakin matar shi, tana ganin shi ta fara murmushi, Alhaji ka shigo, yace eh "Saude, hakuri nazo baki kan abunda yaran su ka miki, basu kyauta ba" sauda a ranta tace "jar uba, wato ba zai ban hakuri a gabansu ba don kar suce ya musu ba daidai ba shine ya biyota daki ko? A fili kuwa tace "haba Alhaji, ni ko daya ban rik'e su a rai na ba, ai da na kowa ne, na mata uzuri, tana cikin tsoro da rudani, amma wlh Alhaji bakomai" Alhaji har ranshi yaji dadi, yace "shiyasa nake son ki, nagode Saude."

Bayan Maghrib Uncle Zaid ya shiga dakin Rafee'ah da Sallama, ciki ciki ta amsa don tana ji haushin kowa a gidan, Kan side drawer ya zauna yayi yace "Rafee'ah" ta dan yi shiru kafin tace "kaima ka yarda da k'azafin da akayi ma Mamin mu?" Zaid yace "ban tab'a yarda ba Rafee'ah, Mami ba haka take ba" farinciki ya lullube ta, da sauri ta juyo inda Uncle Zaid yake zaune, ta riko hannuwan shi biyu tace "Uncle Zaid, ka taimake ni mu gano inda Mami take, Uncle Zaid so nake a wanke ta daga zargin da suke mata duka, har Daddy ya maidota dakin ta, Uncle Zaid so nake duk wanda yake bayan wannan manakisar ya wahala, ya wulakanta, Uncle Zaid ka taimake ni" Zaid ya sauke gwaron numfashi yace" Rafee'ah its not easy as u think, Wallahi ba inda ban neme Mamin ku ba, a wani zuciyata ta bani she's safe, only if i know where i can find her, zan fi kowa jin dadi" Rafee'ah tace "Uncle Zaid, dole mu nemo Mami, Zaid yace "toh Rafee'ah ta yaya?" tace muje mu ga Baba Alhaji (Baba Tj) na fi zaton yasan inda take" Zaid yace "wallahi nafi sawu nawa yace shima nemanta yake" Rafee'ah ta mik'e ta zura Hijab dinta tace "Uncle Zaid, i dont believe baba Alhaji, i have a feeling he's hiding something". Zaid yace "lets go findout" a tare suka bar Dakin don zuwa gidan Kakan su Rafeeq.

Rafee'ah ta durkusa gaban Kakanta, tana kuka kamar ranta zai fita, tace "Baba Alhaji, mesa ba zaka gaya mana inda Mamin mu take ba? Haka kake so mu cigaba da rayuwar mu ba Uwa? Kua da ranta? Baka ga yanda Rayuwar Rafeeq ya koma ba? Hankalin Baba Tj ya tashi, cikin in ina yace " wai waya gaya muku na san inda take?" Rafee'ah tace kaji tausayin mu ka gaya mana, watanni 4 kenan rabon mu da mahaifiya, please ka fada mana" Baba Alhaji yayi shiru, yace "nifa ba zan maida ma Habib Aisha ba, har sai gaskia ta baiyana da kanshi, sai Habib ya bambance. Sai a sannan Zaid yayi magana yace " Baba ba mu na nemanta bane don ta koma gidan Yaya ba, ina so na tafi da ita gida na ne, na san duk inda take kadaici ya ishe ta, amma idan ta zauna gidana time to time zata dinga ganin su Rafee'ah" Baba Tj yace Aa Zaid, zan dai gaya muku inda take amma bazai yiwu ka kaita gidan ka ta zauna ba, ai akwai matsi da takura ga ka da iyali" Zaid yayi saurin cewa "Haba Baba,kar fa ka manta ko bata auri Yaya Habib na ni me kula da ita ne, ma tsare mutuncin ta, donAllah baba kar ka hanani" Mama tace "gaskia ne Alhaji, ni na amince ma Zaid, ka fada musu" Baba Tj yace "Hakane, Aisha na gidan Goggon ta dake Malumfashi tsawon watannin nan, kuma har ta gama Iddanta" Rafee'ah tayi saurin rugume kakan ta don murna yace "tafi chan kar ki karya ni".

*KUYI HAKURI, ABUNDA YA SAMU KENAN YAU, BA KUMA NAN NA SO TSAYAWA BA,WANNAN YA FARU NE SABDA WASU DALILAI. INSHAALLAH GOBE DA SAFE ZAKU GA CIGABAN 29 ATTACHED TO THIS PAGE, DA NA SO BARI SAI DA SAFE, AMMA DA YAKE NAYI ALKAWARI SHISA, PLEA[truncated by WhatsApp]

👧🏽KE ALHERI CE 🙇🏼‍♀

NA

BIEBEE ISA

® NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Pg3⃣0⃣

Saude ce ta nufa gun Rafeew ta na kururuwa, tana fadin yau mun bonu "Shima ya mutu" Zaid dake tsaye tun dazun ya kasa motsi sai hawayen da ke bin kumatunshi, ya tuna inda Rafee'ah ke rok'on shi ya barta ta bishi Malumfashi, da ya hanata binshi da duk sai yaji ya tsani kanshi, ya share hawayen shi, ya taka har toilet din Rafee'ah ya dibo ruwa a cup, yazo ya yayyafa mai, Zumbur Rafeeq ya tashi, Saude mamaki ya lullubeta, ya akayi Rafeeq ya tashi? Daman be mutu ba?, Rafeeq ya fashe da kuka, tare da Rungume Zaid, "Uncle Zaid, Rafee'ah ta tafi ta barni, Rafee'ah ta mutu, she was in my room yesterday, telling me she loves me, Uncle Zaid why didnt i tell her i love her back? Ina sonta wlh Sosai, ta dawo, i so much hate myself right now" duka dakin suka fashe da wani irin kuka mai tsumma Rai. Hafiz ne yayi karfin halin cewa sai ayi Gaggawar kaita makwancin ta, barin je in sanar a gidan Radio, karfe Goma Za'ayi jana'iza, Alhaji Habib kamar mace kai kadai ya daga. Zaid yace da Hafiz "donAllah ayi prolonging dinshi zuwa Azahar" Hafiz yace saboda me? "Ai gwara a kaita gidanta na gaskia" Zaid yace "ina zuwa" ya fita da Sauri, be tsaya ko ina ba sai gidan Baba Tj, nan ya shaida musu Mutuwar, yace "Allahu Akbar" Zaid yace "Baba, so nake ka kira Mami ka gaya mata, Iliyasu ya dauko ta ita da Safiyya, ba zaa kai Rafee'ah ba sai Mami tazo ta mata addu'a, Ba musu ya lallubo ta a waya, ta dauka da Sallama, Baba "ina kwana?" ya amsa, yanda taji muryan shi ta tabbatar ba lafia, gaban ta ya tsanan ta faduwa don tun ran da Rafee'ah ta tafi taji jikinta yayi sanyi kalau. Yace "ki shirya ke da Matar Zaid direbanshi zai dauko ku ya kawo ku Katsina" cikin daburcewa tace Lafiya Baba? Waye be lafia? Mama ce?" yace aa Mamarki na chan daki kalau take" to baba Gaya min na san tabbas ba lafia" Yan nasihohi Baba ya fara mata kan daukar K'addara, nan ta dago mutuwa akayi, cikin rawar murya tace "Baba, Rafeeq ya rasu ko?" yace "aa, ba Rafeeq bane, Yaruwar sa ce" wasu zafaffen hawaye na tashin hankali suka soma kwaronyowa daga idaniyarta, a hankali tace "Rafee'ah" Baba yace "itace, Aishatu" _Inalillahi wa ina ilaihirrajiun, Allahumma Ajirni fi Musibati wa akhlifni khairin minha_ jikinta ya fara rawa. Ta zube kan kujera, "hakuri zakiyi Aishatu, yau da safe ta tashi da Amai" da kyar tace "Baba yanzu Safiyya zata taho, ni ba zan zo ba, ayi gaggawar kai ta makwancinta, _Ubangiji Allah ya yafe ma Rafee'ah, Allah ya gafarta mata, Allah ya sa chan ya fiye mata nan, Allah ya sa Aljanna firdaus ce Makomarta_ *Ameen* dif ta datse wayar.
Zaid yace " Baba, ya tace? Tace a kai Rafee'ah a rufe ta, ba za tazo ba" Zaid yace "aa Baba, ta zo donAllah, barin sake kiranta" Baba ya dakatar da shi "Aa Zaid, ka barta, chan din zai fiye mata kwanciyar Hankali a bata Space, shes a mother". Ba dan Zaid ya so ba ya rabu da ita. Suka tashi suka tafi Gidan Lema.

Mami ta iske Safiyya a Daki, tace "Safiyya sai ki shirya ko? Tafiya ta kama ki katsina" yanda Matar Zaid ta ga Mami ta san ba lafiya duk da ba kuka take yi ba" tace "Mami Lafiya?" tace "Rafee'ah ce ta Rasu" Inalillahi wa ina ilaohir rajiun tace ta pashe da kuka" Mami tayi saurin fita daga dakin. Sai da ta ci kukanta ta gode Allah kafin ta kira Mijinta Zaid, ya tabbatar mata da Mutuwar yace yanzu ma Wanka zaa mata, karfe Goma zaa yi Janaizar ta. Ya tambaya "ya Mami?" tace "gata nan dai, Allah ya dora mata Tauhidi, tayi tawakkali" yace "Allah sarki Mami, to ke ki lallaba ki shirya, Iliyasu ya kawo ki Allah ya kiyaye hanya tace "Amin".

Bayan tafiyar Matar Zaid Mami ta fito Parlor, ta zauna ta shiga tunani, Allahu Akbar daidai nan Suka rabu Shekaran Jiya, ta tuna Yanda Rafee'ah ke ta nannukarta tun zuwan su Kaduna, yanda bata yarda tayi nesa da jikinta, ta rungume ta ta kwanta kan cinyarta, ko toilet zata shiga sai ta rike hannun Mami ta jata har bakin toilet din ashe duk na bankwana ne? Ta tuna lokacin tafiar ta har ta fita ta dawo da gudu tace Mami kice Allah ya min Albarka, " tayi daria tace Allah miki Albarka Rafeeah, Allah baki miji Nagari, wanda zai kula min dake" tayi daria tace "Ina sonki Sosai Mamina" "nima ina sonki Sosai Rafeeah ta" muje in rakaki Uncle Zaid dinku na waje yana jira. Nan mami ta fashe da kuka mai tsumma zuciya. Allah ya gafarta miki Rafee'ah, na yafe miki duniya wa lahira, Allah ya hada fuskokin mu a Aljannah firdaus..

11:00am.

Rafeeq kwance kan Gadon Asibiti, don a Mak'abarta ya sume yayin da aka Birne Rafee'ah, daga Gidansu zuwa Makabarta yayi suma kusan kala 5, da ance a maida shi gida sai yace shi be yarda ba dashi zaayi Janaizar Kanwar shi, kafin a rufeta ya suma, bayan an rufeta ma haka, Maalesh ne yace da Hafiz, Uncle Hafiz barin kaishi asibiti, ya samu hutu a chan, Hafix yace "kayi dabara Mahmud".
Haka Rafeeq yayi ta zaman Asibiti har sai da aka gana Zaman makoki, da ya tashi ya fara sambatu zaa mishi Alluran bacci.

Bayan Kwana 3 Rafeeq zaune cikin dakin shi, Maalesh na gefen shi, dawowan su kenan daga Asibiti, Maalesh ya k'ura wa Rafeeq ido, kallo daya zaka mai kaji ya baka tausayi, Mutuwar Rafeeah ya mugun girgiza shi, idan an lek'o yi mishi gaisuwa har mutum ya zauna ya gama maganar shi Kallo be ishi Rafeeq ba, Maalesh ne ma dai ke amsa gaisuwar, Bayan an watse Maalesh ke cewa "kai Rafeeq abun ka fa k'ara gaba yakeyi, muma fa duk mun girgiza da mutuwar Fee'ah, barin ma gaya maka abunda baka tab'a sani ba, Ina mutuwar Son Rafee'ah, na sota kamar raina jira nayi lokaci yayi in baiyanar mata da son da nake mata, nayi dakkon sonta da dadewa, amma ta tafi ta barmu, nayi Alhinin mutuwart amma Sai naga ba abunda ta fi buk'ata da ya wucei Addua, sai na dau k'addara ya kasance ko da yaushe ina mata addua, toh idan addua take buk'ata, har mutane suzo don taya ka Addua ka gaza ce musu Amin? Haka akeyi?" kamar Rafeeq zai yi magana sai kuma ya fasa, ya mik'e don fita daga dakin, ganin haka Maalesh yayi saurin mik'ewa yace ba sai ka bar min dakin ba, dakin ka ne, nine zan fita" ya fice ya bar Rafeeq tsaye, yana so yace mai ya dawo amma ya kasa.

Meema da Aneesa kanwar Sauda zaune cikin Parlor, tun randa akayi rasuwar sukazo, Zaid ya shigo ciki, Aneesa ta mik'e da sauri, tace "Uncle Xaid ina wuni?" ya amsa da murmushi lafia lao Aneesa, kinsha hutu ya kano?" tace Alhamdulilah, ya k'arin hakuri? Allah ya jikanta, ya Amsa da "Amin" Aneesa sai zungurin Auntyn ta Meema take tayi, tun shigowar Zaid parlo ta sandare daga zaune, don farat daya taji Son Zaid ya mamaye mata Zuciya, Sai da Aneesa ta takata da karfi kafin ta dawo hayyacin ta, da sauri ta gaida Zaid tare da mai gaisuwa, ya amsa ta tare da cewa "barin hau sama gun Yaya". Ya haye Sama. Meema ta kalli Niece dinta tace "Omg, Wallahi naga mijin aure, ina sonshi, kuma sai na same shi ta halin k'ak'a waye shi? Aneesa tayi daria tace " Kanin Daddyn su Rafee'ah ne, kuma yana da mata" tace "ba mata ba ko Matan sa hudu sai ya aureni". Aneesa tace "muje dai ki gaya ma mommy".

Sama Suka hau dakin Sauda, Meema tace da yayarta "Sis, nayi new catch cikin gidan nan, kuma ance K'anin Mijinki ne, nidai na samu mijin Aure" Sauda ta zaro ido a ranta tana Allah ya sa ba Hafiz bane, karaf Aneesa tace "Uncle Zaid ne" Sauda ta sake Ajiyar zuciya tace "Ke wannan ya miki nisa, yana da mata" Meema tace nidai na samu miji, sai ki min hanyar samun shi" Saude tace "sai ki ja hankalin shi ta hanyar Kissa" tace "Ahap sis har sai kince, kar fa ki manta wacece ni" sukayi shewa tare da chafe wa, Aneesa tace Kinga ni in auri Rafeeq, ke ki auri Uncle Zaid, mummy na auren Daddy, kinga shikenan duniya zata sanmu as Rightful Heirs to the Lema's property. Duk sukayi daria, Meema tace "shi kuma Rafeeq din wayei? Aneesa tace "haba Aunty Meema, so nawa zan gaya miki Rafeeq dan Mijin mommy ne, kuma love of my life, don shi zan aura " Saude ta kalli Diyarta Aneesa, ta san yanda take son Rafeeq, kuma ba za taso yin magana gaban ta ba tace "Aneesa je ki duba yanda Rafeeq yake, m sure he needs someone to talk to" tace "eh wallahi bari inje" ta fita da sauri..

Fitowar Hafiz kenan daga Parlorn Alhaji Habib lema, ganin Zaid ya sa shi fitowa, ya dan basu guri ne don su tamu tataunawa da Zaid, yazo wuce wa, daidai kofar dakin Sauda yaji tana cewa;
Saude ta kalli kanwarta tace "Meema, shi wannan Rafeeq din da kikaji Aneesa na magana dan Alhaji ne fa, wani irin banza yaro ne me baudaden zuciya, wai shi Aneesa ke so, kinsan kuwa yaron nan har Marina suka tabayi shi da wanda ta mutu?" Meema ta zaro ido tace "ke haba?, to ke me kika musu,kar kice min baki masu komi ba? Tace "trust me, ban musu komai ba time din, illa kara jan su jiki da nayi, sai Mak'ale ya kawo mun poison, na zuba musu Abinci, poison din ba me kashewa nan take bane, slowly ya ke cin yan hanji, a karshe sai mutum ya mutu don gudun zargi, to too bad Rafee'ah din ce kadai ta mutu da alamu shi be ci abincin ba, amma bakomai shima ba dadewa Zai bi yaruwar sa". Sowa Meema ta sake tace " shisa nake sonki, nobody dare mess with us" tashin hankali ya rufe Hafiz, Ya bugo kofar dakin da karfi. Sauda da Meema suka tashi a firgice.

Suna rok'on Allah yasa Hafiz be ji su ba, wani irin kallon tsana ya bi Saude da Meema, Yau duk me zai faru sai dai ya faru wallahi, don he wont let this pass, dole ya tona asirin Sauda, Meema tayi saurin cewa "Uncle Hafiz ina wuni kwana da yawa" wani irin mugun kallo ya wurgeta dashi, cikin dacin murya ya fara magana "Sauda ashe rashin imanin ki yakai haka? Wani irin zuciya ne dake? Shin baki tsoron Allah? Ba kiji komai ba kika kashe innocent soul kamar Rafee'ah? Kisa fa Sauda? Toh wallahi asirinki ya gama tonuwa,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login