Showing 63001 words to 66000 words out of 115393 words
Dҽɖɩcatҽɖ tɷ mʏ 'kawaɭɭɩʏa ɾɷmaŋ ʝa'ɮa (ʍʏ ռaʍɛ saҡɛ )
*_PAGE 33_*
*Previous*
Wani irin jaa da baya ta yi tare da dafe 'kirji.
*Continuation*
Da sauri Mommah ta 'kara zuwa daf da Mufeeda ta cigaba da 'kare mata kalli from Head to toe.
"Dank'kari". Mommah ta furta ciki².
"Tabbas da ba din ba'a mutuwa a dawo ba da tabbas na ce wani abu". Mommah ta sa ke furtawa.
"Mommah me ki ka ce?". Naseer ya tambaya ya na me 'karewq mahaifiyar shi kallo, domin gaba 'daya ta rud'e.
"Babu komai, kawai yarinyar ce abun tausayi. Yanzu ka sanarwa iyayan ruk'on na ta? Ka da su zo su yi ta neman ta". Fa'din Mommah.
"A'a, ban sanar ma su ba. Sai dai yanzu tunda kin zo. Mommah ai da kin zo da Zaheeda ko Zaliha". Fad'in Naseer.
"Kai ni hankali na a tashe ya ke, kuma nasan ma sun yi bacci. Daddyn ka ma bai dawo gida ba. Sun kama wani mota da tabar wiwi shiyasa bai shigowa, su na can suna case, (kasancewar baban Naseer d'in custom ne.) Na dai kira shi a waya na shaida masa, ya ce zai shigo idan sun bar waje".
"To Allah ya dawo da shi lafiya, bara na je gidan na su na sanar". Fa'din Naseer.
"To sai ka dawo".
*11:00pm*
"Kallamu, ka ga 'yar iskan yarinyar nan tun takwas na 'daura mata tallah, amma har yanzu ba ta dawo ba, ta na can wajan 'yan iskan ta". *MAI ZOGALE* ta fa'da.
"Bar shegiya, za ta zo ta same ni, sai na karya 'kafafuwan ta akan yawon banza". Fa'din KALLAH ya na wani muzurai.
"Ah a, ni fa yawon ta na damuna yai ba, ta je tai ta yi. Ai idan ta kwaso ciwon zamani, kan ta zai 'kare. Ni yanzu tashi za ka yi, in sa'bi hijjabi na mubi hanya in kar'bo 'yan ku'da'de na, idan yaso ko komawa za tai ta kwana wajan 'yan iskan na ta bayan na 'karbi ku'dina, sai ta koma, ita ta sa ni". Fa'din *MAI ZOGALE*.
"To tashi mu tafi". Fa'din KALLAH tare da mi'kewa.
*MAI ZOGALE* ta 'dauko gyale ta yafa ta bi shi a baya ta na sababi ku biyar ne yai ciwon kai a cikin ku'da'dan ta SAI na, lahira ya fi Mufeeda jin da'di.
"Babbar bala'i". *MAI ZOGALE* ta fa'da da 'karfi bayan cin karo da ta yi da faranti ta haska. Aikuwa idanun ta su kai arba da gya'dar ta ya she a 'kasa, bokitin ri'di shi ma zu'be a gefe.
Idanuwan ta har wani 'kan'kancewa su kai saboda bala'i. Ta ce,
"Sittin ta ubangiji bazan yarda ba. Kalli ka ga ni. Kayan nawa ta watsar ta tafi iskancin ta. Qur'anin ubangiji ko watstsaya mata sai na ci kan babbar bura uban ta a garin Kaduna yau 'din nan. Wallahi duk in da za ta nai mo ku'di sai ta ne mo su ta biya ni kaya na da ta watsar ta tafi iskancin ta".
"Wannan dole ne dan uban ta". Fa'din KALLAH.
"Mu koma gida, duk in da ta je ai za ta dawo. Allah ya kai mu gobe. Za ta ci uban ta". KALLAH ya 'kara fa'di.
Gaba kawai ta yi ba tare da ta ce masa komai ba. Ta na tafe ya na bi ye da ita a baya. A dai dai kofar gidan su ka ga mutum tsaye sai kwa'da sallama ya ke.
"Kai kai kai!! Lafiya haka da tsohon daran nan zaka ri'ka kwa'da sallama a gidan mutane? Ko kai 'din 'dan yankan kai ne?". Fad'in KALLAH.
Tambayan ma haushi ya bai wa Naseer, domin ya da'de da sanin halin iyayan ru'kon Mufeedan, azzalumai ne na bugawa a jarida. Danne fushin sa yai tare da fa'din,
"Kuyi ha'kuri, dama wani 'dan matsala ne ya sa nazo wajan ku".
"Matsala ta 'kare kan ka, mu bamu san ta ba". Fad'in *MAI ZOGALE*.
Kamar ya je ya sha'ke ta haka ya ke ji. Harara ya watsa mata 'kasa² tare da fa'din,
" 'Yar ku Mufeeda ce tsautsayi ya fa'da kan ta. Wani yai yun'kurin yi mata fya'de, amma Allah bai ba shi nasara ba, ganin tahowa ta SAI ya buga mata kai da bango sai da kan na ta ya fashe. Yanzu haka ta na asibiti ta farfa'do, sai dai an mata allurar bacci. Shine na ce bara nazo gida na shaida maku ka da kuji shuru hankalin ku ya tashi".
Wani dogon tsaki *MAI ZOGALE* ta ja tare da fa'din,
"Kallamu wai mu za'a rai na ma hankali. 'Dan iskan ta ne fa, sunje sun gama watsewar shine zai kawo mana wani 'kananan iskanci. Dama na da'de ina zargin Muheeda ciki ne da ita. Wato Ka 'dauke ta kunje zubda ciki ko?".
"Subhanallahi! Ni ba fasi'ki ba ne, asali na ma na tsani fasi'kin mutun ko fasi'ka. Abunda ku ke tunani ba haka ba ne ba Sam. Babu abunda ya ta'ba shiga tsakani na da ita saam". Fa'din Naseer.
"Dallah jaye can Ka bawa mutane waje. Kuma Ka sani wallahi kwandala cikin kud'ina ba za su yi ciwon kai ba. Ka fa'da mata ka da ta sake ta mutu, ta ri'ke numfashin ta tukun sai ta bi ya ni ku'di na bata asarar da tamun. Kuma asibiti babu wanda zai je a cikin mu. Ka je idan na gama jinyar cikin shegen da kuka ha'da ba ki kuka zubar sai ka dawo da ita". Ta na kai wa nan a maganganun ta, ta shige KALLAH ya bi ta a baya.
Sosai abun ya ba shi mamaki, girgiza kan sa yai tare da komawa wajan motar shi ya shige ya kunna ya bar layin domin komawa asibiti.
*11:40pm*
Tura 'kofar yai ya shiga 'daki. Har yanzu ba ta farka ba. Mommah zaune kusa da ita ta na ta kallon fuskan ta.
"Har ka dawo? In ce dai ka sanar da su?". Fa'din Mommah.
"Hmm wallahi ban ta'ba ganin 'yan iskan mutane ba irin mari'kan wannan yarinyar. Hmm kin mutanan nan ko a jikin su. Ce wa ma su kai babu wanda zai zo ya duba ta a cikin su, wai ciki ta zubar. Wai 'daukan ta nai na kai ta aka zubar mata da ciki". Naseer yq fa'da rai 'bace.
"Subhanallah! To Allah ya kyauta. Wannan abu bai yi ba wallahi. Kwata² a ce yanzu babu zumunci. Ranar lahira akwai kallo". Fa'din Mommah.
"Daddy yazo?". Naseer ya tambaya.
"Yanzu nan ya wuce ma, ya je ya kwanta ya huta. Kai ma Ka tafi gida ka kwanta, ni zan kwana da ita". Fa'din Mommah.
"A'ah Mom, ni ma zan kwanan anan".
"Hauka ake da zaka kwanan nan? Kai fa na lura da kai ba ka da ta ido". Fa'din Mommah.
Sosa kyeya ya soma yi da key 'din motar shi ya na dariya.
"Maza wuce gida gari na da'da yin duhu". Mommah ta sa ke fa'da.
"To mom, sai da safe". Naseer ya fa'da tare da yin hanyar 'kofa. Har ya fita, ya kuma bu'de 'kofar, zai yi magana Mommah ta nuna masa hanya da hannu alamar ya wuce ba ta San jin komai.
Dariya yai tare da rufo 'kofar ya wuce.
*WASHA GARI*
Ba ita ta farka ba sai da asubha. Lokacin Mommah na zaune kan 'dan kwalin ta tana lazumi, idar da sallar ta Ke nan tq jiyo salatin Mufeedan 'kasa².
Saurin tashi ta yi ta 'karisa wajan ta tare da ri'ke mata hannun da ba 'karin ruwa.
A hankali Mufeedan ta bu'de idanun ta da su kai jazur ta na kallon Mommah. Can kuma tai wani irin zabura ta tashi zaune ta na zazzare idanu.
Saurin dafa ta Mommah ta yi tare da fa'din,
"Kwantar da hankalin ki 'ya ta, babu abunda ya same ki, kan ki ne ya bugu. Ki ba asibiti ne yanzu haka ki na samun kulawar likita".
"Gya'da na, ri'di na. Na Shiga uku na. Ina farantin gya'da na, ina robar ri'di na?". Mufeeda ta fa'da hankali ta she.
"Ki kwantar da hankalin ki, gya'dar ki da rid'in ki su na nan". Mommah ta fa'da tausayi faal ran ta.
Wani ajiyar zuciya ta saki da ta ji gya'da da ri'din na nan.
"D'iya ta ya jikin na ki? Yanzu ina ya ke maki ciwo?". Fa'din Mommah.
"Kai na ne kawai ke min ciwo. Amma ni ban san ki ba. Inna ta ta na can ta na nai ma na".
"To kwantar da hankalin ki, Innar ki tasan ki na nan a asibiti, ni mahaifiyar Naseer ce, shi ya kawo ki asibiti kuma ya je ya nasar da iyayan ki har gida".
Tun da Mommah ta ce ita ce Mahaifiyar Naseer wani uban kunya ya lullu'be Mufeeda har sai da Mommah ta fahinta. Murmushi Mommah ta yi tare da fa'din,
"Ki kwantar da hankalin, ki 'dauke ni tamkar mahaifiyar ki".
Sunkuyar da kai Mufeeda tai ta na wasa da yatsun hannun ta.
Nan Mommah tai ta Jan ta da hira har ta 'dan saki jikin ta don har ta na amsa tambayoyin da Mommah ta ke yi ma ta cikin hikima.
Misalin karfe bakwai, sai ga Naseer, Zaheeda da Zaliha ('kannan Naseer, tagwaye ne identical) har da daddy sanye da uniform 'din custom a cikin shi. Hannun su flask ne da many a kula guda biyu.
Tunda suka shigo Naseer ya zubawa Mufeeda idanu. Zaheeda da Zaliha kuwa ha'da baki su kai wajan fa'din,
"What a beautiful creature. Mommah ina kika samo 'yar India haka".
"A wajan koyo gaisuwa". Mommah ta ba su amsa tare da jifan su da harara.
"Ina kwana sir?". Mommah ta kalli daddy tare da gaishe shi.
"Lafiya 'kalau matar kirki, ya mai jikin?". Daddy ya amsa tare da tambayan ta.
"To alhamdulillah ga ta nan". Mommah ta fa'da tare da nuna Mufeeda.
Kai a 'kasa cike da kunya Mufeedan ta ce,
"Ina kwana daddy?". Cikin sanyin muryan da ke nuna tsantsan kunyar sa da take ji.
"Lafiya lau daughter, ya 'karfin jikin na ki kuma?".
"Alhamdulillah daddy". Fa'din Mufeeda.
"Masha Allah". Daddy ya fa'da.
Twince su ka 'kara kusa da gadon tare da fa'din,
"Ina kwana beauty?, ja jikin ki?".
D'ago kai tai ta kalle su, Ba 'karamin burge ta su kai ba, za su iya zama sa'annin juna. Kan su 'daya, komai na su iri daya, da kyar ka iya banbanta su.
Murmushi ta sakar masu tare da fa'din,
"Lafiya kalau, naji sau'ki".
"Ki na da kyau". Zaheeda ta fa'da.
Still Murmushi ta 'kara yi.
"Ku wasu irin sakarkaru ne wai, kun kawo abinci, mai makon ku aje ku zubawa petient kun tsaya kuna lugudan le'be".
Saurin aje kulan Zaheeda ta yi tare da fiddo plate ta zuba Irish da kwai da miyan hanta, ka na ta 'dauko up ta ha'da tea mai 'dan jaran kauri ta mi'kawa Mufeeda. A kunya ce ta kar'bi plate 'din, Mommah kuma ta kar'bi cup 'din.
Tun 'dazu Mufeeda ta ke son ta gaida Naseer amma kunyan idanun Mommah da daddy ya hana ta, sau uku ta nq 'dago idanuwan ta suna ha'da ido.
"Mata na ya jikin ki?".
Ta kai cup ke nan bakin ta ta ji saukar muryan shi a kunnan ta, ba ta San sadda ta furzo tea 'din waje Ba ta nq zazzare idanuwa, gaba 'daya kunya ya kama ta.
Daga Twince, Mommah har daddy dariya su ka saka.
Mommah ce ta sha mur tare da fa'din,
"Fita ka wuce wajan aikin ka, ban san shashanci. Da yanzu ta kware fa? Idan kai ba ka da kunya, ita ta na da shi". Sai ta mai da kallon ta izuwa Mufeeda tare da fa'din,
"Y'ata rabu da shi ki ci abincin ki kin ji".
Gaba 'daya kunya ta gama rufe Mufeeda, da kyar ta iya cako Irish guda 'daya da fork ta saka a bakin ta.
"Khairat ta shi za ki yi in sauke ki gida sannan in wuce wajan aiki. Ke ma ki sa mu ki wanka ki huta". Fa'din daddy ya na kallon Mommah.
Twins su ka kalli juna suka kwashe da dariya. Zaliha ta ce,
"To daddy ai a wajan ka ya Nas ya ko yi soyayya, dubi fa har wani canzawa mom suna kai, wai Khairat".
Da'kuwa Daddy yai wa Zaliha tare da fa'din,
"Ja'ira, ni abokin wasan ki ne?".
Dukkan su dariya su ka sa, har Mufeeda sai da ta murmusa.
Familyn sun burge ta, akwai fahimta da soyayyar juna a tsakanin su. Abun burgewa.
Ji tai hawaye sun taru a idanun ta, ita ma da iyayan ta na da rai, da yanzu ta na cikin su cikin walwala da jin da'di.
Mommah ce ta mi'ke tare da fa'din,
"To 'ya ta, ni zan je gida sai nadawo anjima".
"To mom, nagode Allah ya saka da alkhairi ya 'kara girma".
"Ameen nagode, amma ba godiya a tsakanin mu, in sha Allah wata rana ke 'din matar Naseer ce".
Wani irin 'kudunnune fuskan ta tai da zanin gado. Dariya ta bai wa duka 'dakin.
Daddy ya ce,
"To Allah ya 'kara sauki, ni dai sai dare zaki gannin".
Ai bata iya 'dagowa ta ba shi amsa ba saboda kunyar da Mommah ta ba ta.
"Hey ka fito fa ka wuce wajan aiki da wuri, ni na san ka mata yai by now ka na banki. Za ka amsa query idan Ka je". Mommah ta fa'di hakan ta re da ficewa.
"Khairat". Daddy ya kira sunan ta amma fuskan shi na ga titi.
"Na'am sir". Mommah ta amsa.
"Kin ga abunda na ga ni a fuskan yarinyar nan kuwa?". Fa'din daddy.
"Wallahi sir, ni kusan suman tsaye nai saboda mamaki. Da badan ba'a mutuwa a dawo ba, babu abunda zai ha ni cewa wannan 'ya ta ce". Fa'din Mommah.
"Zan yi bincike akan yarinyar nan". Fa'din daddy.
"Hakan na da kyau sir".
Bai kuma cewa komai ba, ya cigaba da tu'kin sa. Sai da ya sauke ta har harabar tan'kameman cikin gidan sannan ya juya kan motar sa ya wuce wajan aiki.
Matsawa yai jikin gadon tare da har'de hannayan shi ya na kallon ta.
Zaheeda ta kalli Zaliha, ta furta,
"Perfect match" a hankali.
Ita kuma Zahila tai mata haka 👌🏼da hannu.
"Wato baza ki kalle ni ba? Ya ma ki kyau".
Kamar ba za ta 'dago ba, sai kuma ta 'dago ta kalle shi 'din.
Ba 'karamin kyawu yai ma ta ba, sanye ya ke cikin suite ba'ka'ke. Ta cikin ta kasance ja, necktie 'din ma ja, takalmin shi sau ciki shi ma ja, rigar ta sama ba'ka rike hannun shi. Kan nan wai she'ki ya ke yi. Ba 'karamin kyawu yai mata ba. Fari ne sosai, ajikin shi abu biyu ne ba'ki, gashin kanshi da had santsi ya ke, da kuma wani 'dan 'digo a kumatun shi da ya 'kara masa kyawu ainun.
"Kallon fa? Na miki kyau ne?". Naseer ya fa'da tare da d'age girar sa 'daya.
Wani sanyayyiyar murmushi ta sa ki tare da sunkuyar da kan ta.
Zaheeda da Zaliha kuwa sai murmushi su ke su na gulma 'kasa².
"Tun da ba za ki min magana ba, ni zan wuce Ka da nai latti. Mai ki ke so na taho miki da shi anjima?".
"Babu komai". Mufeeda ta fa'da a hankali.
Sai ya nai mi waje ya zauna tare da fa'din,
"Nasan dai kin ji sanda Mommah ke min fa'dan wucewa wajan aiki ko, to in har ba ki fa'di mai zan taho miki da shi ba, yau ba in da zani".
'Dagowa ta yi ta kalle shi ta ga fa tabbas da gaske ya ke, ta kuma rasa mai za ta ce masa.
Murmushi ne ya su'buce mata lokacin da ta tuna yanzu ba lokacin agwaluma ba ne, sai ta 'dago ta ce masa,
"Agwaluma na ke so".
"Agwa mene? Ai yanzu ba yayin ta ake ba". Fa'din Zaheeda.
Kunya duk sai ta kama Mufeeda, don ta ma manta 'kannan shi na 'dakin.
Harara Naseer ya watsa masu tare da fa'din,
"Da ku ake? Yanzu za ku koma gida idan ku kai wasa".
Kowa yai guum su na shanye dariyar su.
Kallon Mufeedan yai tare da zuwa saitin kunnan ta ya ce,
"Ki ba ri sai na yi ajiya tukunna a faramin wannan horan".
Juya masa baya tai da sauri tare da rufe idanun ta da tafukan hannun ta.
Shikuma dariya yai tare da kallon 'kannan shi ya ce,
"Ku kula min da ita sosai".
"OK bro, mu ma Ka two mana da recharge card, sub 'din mu ya 'kare".
"Ok". Shine abunda ya fa'da tare da