Showing 87001 words to 90000 words out of 115393 words
bunne ki babu Wanda ya sa ni, kuma ba bu uban da zai tambaye ni".
Ji ka ke zuuuuuuu birrriii bur bu buttt bum bum bum. Marwanatu ta saki zawo ha'de da tusoshin tsoro.
To she hanci Musa bai tare da fa'din,
"Wallahi ki ka 'kara min tusa a ''daki SAI na illata ki. Za ki yi baya ni ko kuwa??".
"Zan yi, wallahi zan yi". Fa'din Marwa.
"Oya, ina jin ki". Musa ya fa'da tare da 'daura 'kafa 'daya a kan gado.
"Baba ne yai asiri ka dao na son Mufeeda ka koma so na. Shine da asirin ya ka ma ka, ka ce ka FASA auran Mufeeda, ni ka ke so".
"Za kuma ki ci uban ki yanzu ba". Fa'din Musa tare sa sauek 'kafar shi 'kasa, wani tu'ku'kin ba'kin ciki na taso NASA na raba shi dda annurin zuciyar shi da akai.
Duka yauwa Marwanatu kamar kayan wanki, ka na ya sake ta saki uku, tare kwace 'dan shi. Domin ya yi rantsuwa ko mutuwa 'dan zai yi bazai 'kara shan nono ba, balle ya tsotso tsiya.
Tun daga hanya Marwa zunduma ihu babu takalmi 'kafar ta, kan nan ba 'dan kwani. Fuska duk a kumbure saboda uban duka da Musa ya mata. Duk Wanda ya gan ta a hanya ya tambaye ta mai ya same ta, SAI ta ce mass mijin ta ne ya sake ta sakamakon aspirin da su ka mass ya aure ta ya karye. Aikuwa da yawan mutane Allah ya 'kara su ke mata tare da tsine mata.
Ko da ta isa gida, lokacin *MAI ZOGALE* ta dawo. Tun daga wake ta ke jin ihun Marwa. Da gudu tai 'kofa, kicibis su kai da Marwan. *MAI ZOGALE* ta ce,
"Lafiya Marwa? Ina habulkar(Abulkhair) 'din ya ke? Hatsari ki kai ne?".
"Ni dan Allah kin is he ni da tambaya, Musa ne ya sake ni saki uku, sakamakon asirin da muka masa ya karye. Ya ce shi bai san lokacin da ya aure ni ba, kuma ya kwace abulkhair ya ce wai bazan 'kara bashi nono ya sha ba, wai zai tsotso tsiya".
Kiiiiiiif timmmmm
*MAI ZOGALE* ta kife a 'kasa bakin ta na fidda kumfa.
~____________________~
*BAYAN BIKIN NASEER DA MASHKURA*
Abunda Mashkura tai tsammani a gidan Naseer ba shi ta taras ba, domin ta 'dauka gidan da Mufeeda ta zauna a nan gidan za ta zauna. Sannan ta yi tsammanin irin soyayyar da Naseer ya shayar da Mufeeda za ta sa mu ninkin hakan a wajan Naseer.
Sai dai sam Naseer ba ya da lokacin ta, gangan jikin sa kawai ta aura, ba ta ganin shi idan ba da daddare ba, da daddaran ma idan ta hana kan ta bacci, da sassafe kuma ya fice. Abun duniya duk ya bi ya ishi Mashkura.
~KATSINA. 'KAUYAN MAI RIGA~
Fatsima shekara goma sha shidda, amma kin kasa manta komai? Duk iri butulcin da ki ka mana, ba'kin cikin ki shi ya kashe mahaifiyar ki da mahaifin ki. Amma duk da haka muka tsamo mi daga halaka muka raba ki da 'dan boko, shine ki ka 'kullace mu har yanzu. Idan anyi magana sai ki ce 'yar ki. 'Yar ki 'din banza 'Yar ki 'din wofi. To wallahi ke da KADUNA har gaban abada. Idan ba ki sa ni ba ma yau ki sa ni. Tuni ke gawa ce a idanun 'yan Kaduna. Kuma shi kan shi Amadun da KI ke 'kulafuci akan sa, tuni an kashe sa saboda an gano bayan tsubbu har da shimmafin ya ke yi".
Wacce ake kira da Fatsima, ko 'daga kai ba ta yi balle ta kalli Yar ta hajjojo da ke magana.
"Idan kin ga kin fita daga 'kauyan mai riga, to gawarki ce ta fita" fa'din Hajjojo.
"Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un". Fa'din baba Idi da ke shigowa cikin gidan hankali ta she.
"Hajjojo mai ki ka hwa'di? Dama duk abunda ku ka hwa'di min 'karya ku ke. To wallahi kahwa ta 'kahwar ku garin Kaduna nan da sati biyu. Yo ai wannan iskanci ne. Yo to in ba iskanci ba, ku rabo 'diya da gidan mijin ta akan batun banza. Duk sai kun ci tselar uwayan ku, idan har mu ka tai Kaduna na ji duk batun da ku ka hwa'di 'karya ne".
Jikin Hajjojo sai rawa ya ke yi, ba ta ta'ba zaton baba Idi zai shigo gida yanzu ba balle ya ji 'dumin da take wa Fatsima ba.
Harara baba Idi ya jefe ta da shi tare da fa'din,
"Makirar 'diya". Ka na ya shige 'dakin shi.
~KADUNA PRISON~
"Bawan Allah yau kwana sha biyu ina zirya anan kamin Allah ya sa in gan ka. Ba 'karamin binciken files akai ba kamin aka ga no na ka. Yau shekarun ka goma sha biyu a cikin prison 'din nan ba tare da na aikata komai ba".
Saurin 'dagowa bawan Allahn nan yai ya kalle sa tare da fa'din,
"Bawan Allah, ya akai kasan ban aikata komai ba?". Ya fa'di hakan ne idanun shi na fidda zafafan hawaye.
Ajiyar zuciya Daddy ya fidda tare da fa'din,
"Na da'de ina bincike akan ka, kamin nazo nai man ka nan cikin prisoñ, na san 'dan uwan ka ne ya shirya maka wannan tuggun, amma na yi maka al'kawarin fidda kai a cikin wannan gidan, amma da shara'di".
Saurin kallon shi AHMADU yai tare da fa'din,
"Fa'di shara'din ka, wallahi in dai bai sa'bawa Allah ba, zan yi maka shi. Wallahi ina so in FIFA daga gidan nan domin naga tilon 'ya ta".
"Ni ma a kan ta na ke son muyi magana".
Saurin sake kallon shi AHMADU ya yi ba tare da ya ce, ko mai ba.
Magana su kai Wanda ni kai na ban ji ba. Hawaye ne kawai ke zuba daga idanun Ahmadu.
Jinjina kan shi yai sannan ya ce.............
Ya na kai wa 'karshan maganar ya fashe da kuka mai sauti. Shi kan shi daddy share hawaye ya ke yi.
*MAMAN UMMEE*
*AKA*
*MATAR SAYYADEE*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
®🏝
*ZAFAFA WRITTERS FORUM* *...*📚✍🏻
[ ```Zafafa writers is a union for enlightening people to learn hottest things that relate marriage, love and religion.
Zafafa writers is a union to enlight women```]
*https://www.facebook.com/110224494006508/posts/110225604006397/?substory_index=1&sfnsn=mo*
*_Z• W• F•🏝_*
🌟NI DA SHI ABU DAYA NE🌟
('kiʀ'kiʀɑʀʀɑɳ ʆɑɓɑʀi)
ɓɑɳ yi ɗɑɳ wɑɳʝ kѳ wɑtɑ ɓɑ, iɗɑɳ yɑ yi รɦigɛ ɗɑ ʆɑɓɑʀiɳ ki/kɑ ɑkɑรi ɑkɑ รɑɱu.
laвarι ne мaι cιĸe da zazzaғan ѕoyayya, yaυdara, cιn aмana тare da 'dυмвιn nadaмa.
*Story and written by*
*Zulfa'u 'Saeed Ibrahim* ( _Maman Ummee_). @lso known @s
*MATAR SAYYADEE*
*_PAGE 42_*
Shuru wajan ya 'dauka har na tsawon mintuna goma. Can daddy ya nisa tare da fa'din,
"Mal Ahmadu, in sha Allah nan da sati ko karfin sati zaka fito daga prison 'din nan in sha Allah, sannan zan maka 'dan uwan ka kotu domin ta kwatan maka hakkin ka akan mummunar Sharrin da ya 'kulla maka, sannan dole ne yai wa kotu bayanin yadda akai ya samo bindigun da aka same ka da su a cikin gidan ka. Sannan ina son wannan envelope 'din da ka ce bawan Allah nan ya baka idan har za'a same su".
Goge hawaye mal Ahmadu yai tare da fa'din,
"In dai ba ha'ke gidan akai ba, ina da tabbacin za'a same su in sha Allah".
Hannu daddy ya mi'ka masa tare da fa'din,
"Nagode kwarai mal Ahmadu, sai na sake zuwa". Ya na gama fa'din haka ya wuce.
Har sai da ya fita, ka na mal Ahmadu ya bar kallon shi tare ajiyar zuciya.
~*********~
Tun da *MAI ZOGALE* ta fa'di 'kasa, komai na 'barin jikin ta na dama ya dai na aiki har da idon ta 'daya na 'barin dama.
Ba 'karamin tashin hankali ta shiga ba. Marwanatu kuwa saka ta take a gaba tai ta kuka ta na fa'din *MAI ZOGALE* ta cuce ta. A nan wajan take bayan gidan, Marwanatu kuwa ko kula da ita bata yi. Shikuwa KALLAH ya na can yawon maulan da ya saba ko bi takan sakin da a kai wa 'yar shi bai ba, domin daman ya riga ya san duk daran da'dewa asirin zai warware.
*_________*
*NASEER & MASHKURA*
*_________*
"Wallahi na gaji, nagaji! Ka kawo ni nan gidan ka aje ni, ban ce komai ba, ba ka bani kulawa da kuma ha'kki na a matsayi na na matar ka, na kauda da kai, kullum shinkafa da mai da yaji na ke ci cikin gidan nan, ban yi 'korafi ba, yanzu kuma sai ka kawo min gyero da kuma masara a matsayin abincin da zan ri'ka ci? Ba zai yu ba. Wannan sabon salon wuka'kanci ne kawai don ka ga ina son ka, ai baka isa ka ce min ba ka da 'kudi ba. Nasan irin rayuwar da ku ka yi kai da Mufeeda, abinci ku ke ci mai rai da lafiya, har mota mai tsada ka sai mata. Ka ma bari in yi amfani da motar ka'ki, ba ka ta'ba kwanciya da ni a matsayi na na matar ka ba. Mai ka ke nufi ne wai?".
Wani irin kallo Naseer 'din ya watsa mata tare da fa'din,
"Ya kike so in yi ne? Wai ance maki son ki na ke yi na aure ki? Na aure ki ne kawai don in 'kuntatawa 'kawar ki, ku ma da waje wa mu kai dake. Kuma cima da ki ka ga ya canza a gidan nan, ba laifi na ba ne, an kore ni wajan aiki na, sannan anti blocking account 'dina, wannan gidan ma mu na daf da barin shi, domin ida shekara ya 'kare, ban da #200 thousand 'din da zan biya ku'din haya. Sannan ko a mafarki, ka da KI ta'ba tunanin zan iya kwatanta irin son da na wa Mufeeda a gare ki, ko Kusa ba za ki ta'ba samun haka ba. Bayan ita ba na tunain akwai wata 'diyar da zan iya gwadawa soyayyar nan. Ku mata munafukai ne, wajan ku fari, cikin ku yafi dafin maciji. Idan kin ga zaki iya zama dani haka, fine. Idan kuma ba zaki iya ba, 'kofa a bu'de ta ke, ban 'daura miki idda ba". Naseer ya gama fa'din haka ne tare nunawa Mashkura 'kofa.
Da gudu ta shiga 'daki ta rufo 'kofa.
Shikuwa Naseer, tsaki ya buga tare da ficewa daga gidan.
Mashkura na jin alamar fitar sa, ta lalubi wayar ta tare da danna wasu numbobi. Gudu biyu aka 'daga.
"Fairuza na shiga uku na lalace". Fa'din Mashkura tare da rushewa da kuka.
Daga 'dayan 'bangaran Fairuza ta ce,
"Mashkura mai ya faru, yi min bayani. Aikin mu ya lalace ne?".
"Aikin mu kwata² bai yi ba, nasan akan plan 'din shi ya aure ni. Ai na fa'da miki ya ce min zai aure ni ne kawai domin ya 'kuntatawa Mufeeda, amma ki ka ce min boka ya ce komai zai yi dai² bayan aure, kin ce boka ya ce zan juya shi son rai na. To gashi ban samu nasarar juya shi ba, ni duniyar na son juya min baya". Mashkura ta na maganar ne kamar za ta shi'de don kuka.
"Calm down please. Ki nutsu ki min bayani in details domin in san ta yadda zan shawo kan matsalar".
Mashkura ta 'dan sassauta kukan ta tare da fa'din,
"Har yanzu bai ta'ba ha'da shimfi'da da ni ba, sannan bai kai ni gidan da suka zauna da Mufeeda ba, haya ya kama min ke kin sani, sannan na fi sati abincin 'kari har na dare shinkafa da mai da yaji ne. Yau kuma sai ga gyero da masara, wai kunu da tuwun masara zan koma ci saboda an kore shi wajan aiki sannan kuma wai tashi zamu yi a gidan domin bai da ku'din sake biyan gidan idan shekara ta zagayo, wai anti blocking account 'din sa duka".
Wani iska mai huci Fairuza ta fesar tare da fa'din,
"Allah dai ya tsine wa mahaifin nan nashi, wallahi duk aikin shi ne".
"Wallahi shi ne. Shine Fairuza. Kin san dama fa bai son aure ba da shi. Ya kwace komai na shi dake wajan Naseer. Kuma duk sanadin la'ananniyar Mufeeda nan ne wallahi". Fa'din Mashkura.
Fairuza ta nisa tare da fa'din,
"Kuma babbar matsalar shine, asirin na da wuyan kama jikin su, ki duba Naseer, kamin mu cusa tsana da 'kiyayyar Mufeeda cikin zuciyar sa, boka ce mana yai dole sai mun saka masa wani gagarumin tashin hankali da zargin ta a zuciyar shi, domin sai yaji bacin rai akan ta irin 'kololuwar nan kamin asiri ya kama shi".
"To ya kike ganin za'ayi? Ni fa wallahi ko ba abincin, idan har za'a saka masa magigicin 'kauna ta a zuciyar sa, ya kuma soni fiye da mahaifiyar sa, zan iya zama da shi a cikin ko wani irin hali wallahi". Fa'din Mashkura.
"Ki kwantar da hankalin ki, kawai ki san yadda zaki yi ki turo min da 200k, ni kuma gobe zan koma wajan shi, ko ma menene zan ce mass yai kawai in dai Naseer zai 'kaunace ki". Fa'din Fairuza ta na wani hararar wayar.
"Yanzun nan zan turo miki, zan miki transfer yanzu, wallahi dama abunda ya rage min kenan a cikin account. Don girman Allah ki taxi yanzu".
"Ba Matsala, turo kawai, sai in tafi yanzu 'din". Fa'din Fairuza.
Cikin mintuna uku kacal sai ga alert a wayan Fairuza.
Fairuza ta duba taga ku'din. Dariya tai tare da fa'din,
"Wawuya sha³ kawai, wallahi ba wani wajan bokan da zan je. Wannan ku'din da ki ka turo kuma, na yagi rabo na".
~*KANO*~
Wayar ta da Naseer ya sayan mata da ke 'kara ya dawo da ita daga dogon tunanin da ta tafi. Kallon wayar ta yi, ta ga *GARKUWA* a jikin screen 'din. Haka kawai murmushi ta ji ya su'buce mata. Wayar na daf da tsinkewa, ta 'daga tare da fa'din,
"Amincin Allah ya tabbata a gare ka yaaya na".
Ajiyar zuciya Naseer ya saki tare da fa'din,
"Ke ma haka 'yar shalelan 'kan wata. Ina 'ya'ya na suke?".
"Su na can baaba da ummie na fama da rigimar su". Fa'din Mufeeda.
"Ki same ni a garden yanzu". Ya na fa'din hakan ya katse wayar shi.
Shuru tai ta na jujjuya wayar dake hannun ta. Can kuma ta mi'ke tare da warware gyelan abayan dake kan ta ta yafa shi a jikin ta. Zaka rantse da ubangiji Mufeeda budurwa ce, domin ba ta yi kama da wacce ta ta'ba aure ba, balle har akai ga zancan 'ya'ya har biyar.
Fitowa tai hannun ta rike da wayar ta tana tafiya ta na wasa da wayar.
Finciko ta ta ji anyi ta baya, saurin juyowa tai su ka ha'da idanu da *NAINA*. Tsayawa Mufeeda tai ta na kallon ta cike da mamaki.
Nuna ta naina ta yi da hannu tare da fa'din,
"Ki kalle ni da kyau, kin san idan kyawu ne na jiki da fuska, ni ma ba baya ba ce, idan gashi ki ke ta'kama da shi, (Naina ta cire talan da ta rufe kan ta, ta wani girgiza kan ta, gashin ta ya zubo har baya. Ta cigaba da fa'din,) kalla da kyau, shi ma ina da shi. Ina son ki fa'da min da wani irin charm ki kai amfani da shi miji na, I mean the love of my life, ya so ma son ki? Imaging, divorcee with five children, how comes?".
Mufeeda kallon ta ta shiga yi from hair to toes, irin kallon lafiyar ki 'kalau kuwa, can ta nisa tare da fa'din,
"Waye mijin na ki".
Waro idanu Naina ta yi tare da fa'din,
"Are you asking me?".
"I have to". Mufeeda tai saurin ba ta amsa.
"To ina nufin Jawad, masoyi na, kuma miji na ni ka'dai".
Wani irin dariyar rainin wayau Mufeeda ta yi ta re da fa'din,
"You need to see a doctor". Ta na gama fa'din haka tai hanyar garden ba tare da ko waiwaye ba.
Naina kuma ji ta yi kamar ta fashe tsabar ba'kin ciki, ba bu abunda ya soke ta matu'kar kamar *you need to see a doctor* da ta fa'da.
Zaune ya ke akan 'daya daga cikin royal chair 'din da ke zagaye da garden 'din, hannun shi rike da wani 'dan madaidaicin cup ya na seeping Chapman 'din da ke ciki da straw.
San'da ta soma yi don tai surprising 'din shi. Sai da ta zo gam taji saukar muryan shi ya na fa'din,
"I smell the scent of ur perfume".