Showing 84001 words to 87000 words out of 115393 words
religion.
Zafafa writers is a union to enlight women```]
*https://www.facebook.com/110224494006508/posts/110225604006397/?substory_index=1&sfnsn=mo*
*_Z• W• F•🏝_*
🌟NI DA SHI ABU DAYA NE🌟
('kiʀ'kiʀɑʀʀɑɳ ʆɑɓɑʀi)
ɓɑɳ yi ɗɑɳ wɑɳʝ kѳ wɑtɑ ɓɑ, iɗɑɳ yɑ yi รɦigɛ ɗɑ ʆɑɓɑʀiɳ ki/kɑ ɑkɑรi ɑkɑ รɑɱu.
laвarι ne мaι cιĸe da zazzaғan ѕoyayya, yaυdara, cιn aмana тare da 'dυмвιn nadaмa.
*Story and written by*
*Zulfa'u 'Saeed Ibrahim* ( _Maman Ummee_). @lso known @s
*MATAR SAYYADEE*
Dҽɖɩcatҽɖ tɷ mʏ 'kawaɭɭɩʏa ɾɷmaŋ ʝa'ɮa (ʍʏ ռaʍɛ saҡɛ )
*_PAGE 40_*
*FLASHBACK*
Lukman ne zaune akan wata kujera da aka yi sak royal, amma na siminti da aka 'kawata shi da penti. Akwai su guda bakwai a waje daban² a nan cikin garden 'din.
Waya ce a hannun shi ya na browsing yadda zai shawo kan kan budurwa.
Kaman ance ya 'daga idanun shi, aikuwa ya hangi baby ta na shan shishi tare da fesar da haya'kin cike da kwarewa, har wani o'o ta ke yi.
A matu'kar fusace ya mi'ke yai wajan..........
Nan muka tsaya a baya.
************
*CONTINUATION*
Wani irin razana tai tare da mi'ke wa ta bugi pot 'din shishan ya kife.
Wani haske ta gani ya gilma ta idanun ta, can ta ga tantabaru na tashi, sai kuma ta ga garin yai mata dun'din.
Lukman ne ya dunga kifa mata mari hagu da dama tare da fa'din,
"Shaye² ki ke yi? Da ma ke 'yar shaye² ce? Uban uban waye ya koya miki wannan harkan?". Da 'karfi ya mata wa'dannan tambayoyin muryan shi na echoing a garden 'din.
Jikin Baby na rawa hannun ta kuma dafe da both Chic's 'din ta, kan ta a 'kasa kamar tsohuwar munafika. (Ko da ya ke ai ita ce).
"Ba da ke nake magana ba?". Lukman ya 'kara fa'di da 'karfi sai da ta razana.
Bakin ta na rawa ta soma fa'din,
"Ya Luk.. Luk..man, ka yi ha'kuri wallahi bazan sake ba".
'Ko'karin kwance belt 'din jikin shi yake, Baby ta juya za ta shimfi'da da gudu. Aiko taku 'daya yai ya cafko ta tare da fa'din,
"Zaki ci uban ki yau". Ya fa'di hakan ne tare da 'karasa zare belt 'din jikin shi ya shiga shimfi'da mata ta ko ina a jikin ta.
Aikuwa ta shiga ihu ta na burgima a wajan.
Mufeeda da fitowar ta kenan daga side 'din Naseer ta hangi abunda ke faruwa. Da gudu ta 'karasa wajan tare da ri'ke belt 'din ta na fa'din,
"Don rahamar ubangiji yaa Lukman ka yi ha'kuri ka bar ta hakan. Ta tuba. Ko ma mai ta yi bazata 'kara ba".
Sakin mata belt 'din ya yi tare da fa'din,
"Mufeey ki bar yarinyar nan kawai. Ba ki san abunda ta ke aikatawa ba ne. Shaye² fa take yi. Dubi abunda ta ke shafa". Lukman ya fa'da tare da nu na mata shishi pot 'din.
Baby da tun da Mufeeda ta ri'ke belt 'din ta kwasa a guje tai part 'din haj Jummai.
"Ka yi ha'kuri yaa Lukman. Ba duka ba ne zai gyara 'barnan. Nasiha zaka mata tare da nusar da ita illar abun, musamman da ta ke 'diya mace".
Ajiyar zuciya Lukman ya saki tare da fa'din,
"Nagode da shawara, in sha Allah zan yi hakan".
Murmushi ta yi tare da fa'din,
"Nagode". Tare da juyawa za ta wuce.
"Ina zaki je kuma? Don muje caan mu zauna, dama akwai abunda na ke son tambayan ki".
Gaban Mufeeda ya fa'di, amma sai ta 'kir'kiro murmushi tare da fa'din,
"Ya Lukman idan ba za ka da mu ba, anjima mu yi maganar, yanzu Ummie jira na ta ke yi".
"OK ba damuwa, muje in raka ki".
Ba don Mufeeda ta so ba, tai gaba ya na biye da ita a baya. Daga baya ya dawo gyefan ta suka jera ya na 'dan jan ta da hira.
Naina ce ta fito daga side 'din haj Jummai, hannun ta ri'ke da keyn mota ga dukkan alamu fita za ta yi. Kallon su ta yi tare da ta'be baki ka na ta juyar da kan ta kamar ba ta gan su ba.
"Aunty ina za ki je? Ke da ba wani sanin kan garin ki kai ba". Fa'din Lukman.
Kallon shi ta yi ta 'dan saki fuska tare da fa'din,
"Abincin Ahmad ne ya 'kare, shii ne na ke son naje supermarket na sayo masa. Kasan har yanzu ya kasa sabawa da abincin Nigeria, sai da custard, oat da kuma cornflakes. To duk sun 'kare, shine na ke son sayo masa".
"OK. In dai wannan ne, ki koma kawai, zan je in sayo masa yanzu". Fa'din Lukman.
"Aaa'a ka bar shi kawai, ni ma ina son in 'dan ga garin". Fa'din Naina.
"OK ba matsala, sai kin dawo". Fa'din Lukman.
"Sai kin dawo, Allah ya tsare". Mufeeda ta fa'da.
Wani kallon banza Naina ta jefe ta da shi, ba tare da ta amsa ba tai wucewar ta".
Har part 'din haj Zulfah, Lukman ya raka Mufeeda, ka na ya wuce part 'din mahaifiyar sa.
Matan yaya Abubakar ne a kitchen ta na ha'da abinci, ga 'ya'ya da jiko ki nan turum a parlour su na wasan su.
Wurga idanu Lukman ya shiga yi ya na nai man in da zai ga Baby.
"Ke Husna ina Baby?". Lukman ya tambaye babbar 'yar yaya Abubakar.
"Uncle, 'dazu ta shigo da gudu tai sama". Husna ta ba shi amsa.
Ba tare da ya ce ko mai ba, ya nufi hanyar saman.
'Dakin mummy ya fara nufa tare da kwankwasawa ka na ya tura 'kofar. Mummy na zaune ta saka baby a gaba da ke ta faman kuka kamar wacce alokacin ne uwar ta ta rasu. Ta na ganin jawad, tai tsalle ta fa'da gado tsan lungu.
Wani mugun kallo ya watsa mata tare da fa'din,
"Ba'kar munafuka, ai dole ki 'boye tunda kin san kin aikata tsiya".
Mummy ta katse shi rai 'ba ce,
"Look, Lukman akan Baby zamu samu matsala da kai, ta fa'da min ko mai ai. Meyasa za ka mata irin dukan nan haka kamar ka kama ta ta na shan wiwi ko cocaine? To gaskiya ban son haka. Ta ce min ba abun maye ba ne, flavour ne a ciki mai saka 'kamshin baki. Na kuma yi mata fa'da, shi ma shishan ba za ta 'kara sha ba. Kuma ta min al'kawari. Ko ba haka ba Baby?". Ta 'karashe maganar tare da kallon Baby.
Saurin gya'da kai babyn ta yi, ta na 'kara ma'kurewa jikin bango.
"To ka dai jiko? Ba za ta 'kara ba. Ai shikenan".
Saboda tsabar haushi, Lukman bai iya cewa komai ba, ya juya ya fita. Domin idan ran shi ya kai 'kololuwar 'baci, bai iya cewa komai. Sai dai ya tashi ya bar wajan.
*~NAINA~*
"Wallahi I'm tired of you changes because of that bullshit. We are going back either you like it or not. And wallahi I'm not going to leave you here. We're going back together". Naina da ke kan Jawad ta ke fa'din haka kamar za ta fasa masa dodan kunne.
Abunda zai ba ku mamaki, shi uban gayyar yi yai kamar bai san da mutum a kan shi ba. Danne² shi kawai ya ke a laptop.
"I'm talking to you". Naina ta 'kara fa'da da tsawa.
Sai alokacin ya 'dago da manyan idanun sa ya sauke a kan ta tare da fa'din,
"I'm back to my country, or lemme just say we are back".
"What!". Naina ta fa'da a matu'kar razane.
"Yesss". Fa'din Jawad tare mi'kewa ya aje laptop 'din akan kujera ka na yai hanyar bedroom.
Da gudu ta bishi tare da shan gaban shi, zufa har ya soma wanke mata jiki. Ta ce,
"Are you out of ur sense? What are you talking about? Aren't you a shame of your self? It's because of that foolish girl? Lemma tell sometimes you didn't know, she's a widower with five children. I mean she gave birth to quintuplets. I known that you're in soon much love with her, but lemme remained you, I can't share you With any woman in this world. And I will never let that happen. I calling small daddy right now". Ta na kawo wa nan ta bangaje shi tare da shigewa 'daki ta kullo 'kofa.
'Daga kafa'dun shi ya yi , irin I don't care 'din nan.
Mu ha'de gobe.
*MAMAN UMMEE*
*AKA*
*MATAR SAYYADEE*
[10/3, 12:54 PM] Meenal: *بسم الله الرحمن الرحيم*
®🏝
*ZAFAFA WRITTERS FORUM* *...*📚✍🏻
[ ```Zafafa writers is a union for enlightening people to learn hottest things that relate marriage, love and religion.
Zafafa writers is a union to enlight women```]
*https://www.facebook.com/110224494006508/posts/110225604006397/?substory_index=1&sfnsn=mo*
*_Z• W• F•🏝_*
🌟NI DA SHI ABU DAYA NE🌟
('kiʀ'kiʀɑʀʀɑɳ ʆɑɓɑʀi)
ɓɑɳ yi ɗɑɳ wɑɳʝ kѳ wɑtɑ ɓɑ, iɗɑɳ yɑ yi รɦigɛ ɗɑ ʆɑɓɑʀiɳ ki/kɑ ɑkɑรi ɑkɑ รɑɱu.
laвarι ne мaι cιĸe da zazzaғan ѕoyayya, yaυdara, cιn aмana тare da 'dυмвιn nadaмa.
*Story and written by*
*Zulfa'u 'Saeed Ibrahim* ( _Maman Ummee_). @lso known @s
*MATAR SAYYADEE*
Dҽɖɩcatҽɖ tɷ mʏ 'kawaɭɭɩʏa ɾɷmaŋ ʝa'ɮa (ʍʏ ռaʍɛ saҡɛ )
*_PAGE 41_*
Kwance ta ke akan makeken gado ta na ta juyi. Ayaan da ke gyefan ta sai tsala kuka ya ke yi, amma ba ta saurare shi ba.
"Mai na ke son jawo wa kai ne ne? Sam yaa Naseer ba tsaran aure na ba ne. Mai zai yi da bazawara ma 'ya'ya biyar. Dole ma na yakice shi a cikin zuciya ta". Mufeeda da ke kwance sai juyi ta ke yi akan gado ta ke wannan zan can zuciyar.
Baaba Habiba ce ta bu'de 'kofar ta shigo tare da 'daukar Ayaan da ke kuka ka na ta 'daka mata duka a gadon bayan ta ta ce,
"Hauka ki ke yi ne Mufeeda? Ki na ji Ayaan na kuka amma kin yi biris. Mai ke da mun ki ne?".
Mi'ke daga kwancan ta yi ta zauna tare da fa'din,
"Baaba wallahi rigimar Ayaan ce tai yawa. Babu abunda ya sa ni sai rigima. Ciki muka kawo duniya".
"Ungo nan". Fa'din baaba Habiba ta re da mata da'kuwa.
"Amshe shi ki ba shi ya sha ko in miki duka a 'dakin nan". Baaba Habiba ta sa ke fa'da.
Amsar shi Mufeeda ta yi ta na turo baki.
Kwafa baaba Habiba ta yi tare da ficewa daga 'dakin.
~*KADUNA*~
"Wallahi kin san Allah, Naseer sai ya mai do min duk wani abu da yake hannun sa in dai mallaki na. Ban hana shi aure ba, ya je yai aure. Amma kamar yadda na fa'da, komai nawa SAI ya dawo hannu na. Har nawa ya ke da zamu gindaya masa abu ya tsallake? Ba dai ya saki 'yar mutane ba tare da wani dalili ba, ni kuma SAI na shayar da shi ruwan mamaki. Ki ce masa ya same ni a 'daki na, right now". Daddy ya saka Mommah a gaba kamar ita ta saka shi yin saki ya na ta bala'i. Fuuuu ya wuce sama, har ya kai karshe step 'din, ya juyo ya kalli Mommah ta re da fa'din,
"Right now".
Ajiyar zuciya Mommah ta saki tare da 'daukar wayar ta ta dannawa Naseer kira. Bugu biyu ya 'dauka. Mommah ba ta bashi damar magana ba ta ce,
"Ka zo mahaifin ka na san ganin ka yanzun nan". Ta na gama fa'din haka ta katse wayar.
Cikin abunda bai fi minti goma ba, ta SAI ga shi ya shigo gidan. Babu kowa a parlour. Kai tsaye ya haura saman.
Sallama yai a 'kofar 'dakin. A da'kile daddy ya amsa masa sallamar ciki².
Kamar munafuki ya shigo ya raku'be a jikin kujera tare da fa'din,
"Daddy, Mommah ina wuni?".
Babu wanda ya amsa mashi gaisuwar sa, SAI ma wata uwar harara da Mommah ta jefe shi da ita.
Ba yabo ba fallasa daddy ya kalle sa tare da fa'din,
"Alhamdulillah! Yau auran ka saura sati 'daya ko? Mu ba ka 'dauke mu matsayin mahaifan ka ba ko? Da kyau. Da mu ka hanaka auran, shine ka je ka ha'do ni da tawa mahaifiyar ko? To bari ka ji, ni baka isa ka rabamu da mahaifiyar mu ba, zamu rabu da Dada lafiya. Kaje kai auran ka, amma Wallahi tallahi, komai fake wajan ka nawa, a yanzu SAI ka aje min shi kamin ka bar gidan nan. Makullin mota na, makullin gida na, ku'da'dan da ke account 'din ka Wanda kasan ni ke turawa, duka a yanzu na ke bu'katar su".
A matu'kar firgice Naseer ya 'dago ya kalli mahaifin na shi idanuwan shi sun cicciko da hawaye. Ya bu'de ba ki zai yi magana. Daddy ya dakatar da shi tare da fa'din,
"Not a word, ba ba San jin ko 'kalma 'daya daga gare ka. Properties 'dina na ke so yanzun nan".
Wani irin miyau mai wuyar ha'diya Naseer ya ha'diye, Adam's apple 'din shi SAI da yai sama tare da yin 'kasa. Da 'kyar ya iya ciro hannun shi a aljihu, ya fiddo makullin gida da na motar ya aje Kusa da 'kafar daddy, kana ya fiddo wayar shi tare da yin transfer ku'din da ke account din shi, Wanda dama ya bu'de shi ne domin ku'din da daddy ke turawa.
Daddy na ganin alert ya kalle shi tare da nuna masa 'kofa ya ce,
"I don't want to see your face ever again. Get out before I lose my temper". Daddy ya 'karisa da 'karfi.
Jiki a sake Naseer ya fito daga 'dakin, Jan 'kafa kawai ya ke yi, amma bai san in da 'kafar ta shi ke sauka ba.
Twins na parlour su na kallo, kallo 'daya su kai wa yayan na su suka 'dauke kai tare da barin falon immediately.
Baki bu'de ya bisu da idanuwa, bai san Sadda wasu zafafan hawaye su ka zubo masa ba.
Ya kusan 5min ya na tsaye wajan ka na ya na san dan 'kafafuwan sa ya fice daga gidan 'kafar shi ko takalmi ba bu.
~MARWANATU~
"Gaskiya *MAI ZOGALE* na gaji, ki mai da ni gidan miji na. Ki na ga ni fa yai wata uku kenan Musa bai waiwaye mu ba. Ko fa kiran sa nai a waya ba ya 'dagawa. Daga baya ma saka number ta yai a blacklist. Ni dai ina zaman zama na ki ka wani ce SAI nazo gida Wanka. To gashi nan garin son ku'din ki, zaki karshe min aure". Marwanatu ke fa'da cikin fa'da².
*MAI ZOGALE* ta daga ta tare da fa'din,
"Kwantar da hankalin ki, yau 'din nan zaki koma gidan ki, ko Musa yazo ko bai zo ba. Akwai ni Babban shiri da ba ke yi a kan shi. Shi da kan shi SAI ya zo ya dur'kusa a gaban ki ya na nai man gafarar ki".
Turo baki Marwa ta yi tare da fa'din,
"Ummm, ai kin da'de ki na fa'din haka, ban ga ko mai ba, SAI ma kin 'daukar waya ta da yake yi".
"Ke dai kwantar da hankalin ki". Fa'din *MAI ZOGALE*
Rana na yin sanyi, Marwanatu ta goye 'dan ta tare da harha'da kayan ta ta gudu gidan mijin ta. Lokacin *MAI ZOGALE* ta tafi yawon bin bokayan ta da babu abunda ake yi SAI damfarar ta da cin ku'din ta.
*______*
"Musa ba ka ganni ba ne? Ba ka ga ba dawo ba? Ko ba kai kewa ta ba ne?". Fa'din Marwanatu ta re da tsurawa Musa idanu.
A wani irin fusace ya juyo ya kalle ta tare da fa'din,
"Uwar wacece ke? Mai na ha'da da ke? Ya akai na aure ki? Wallahi ki min bayani ko kuma numfashin ki ya 'kare a gidan nan".
Wani irin waro idanu Marwanatu ta yi ta re da fa'din,
"Musa ni ce fa, Marwanatun ka ce fa".
Fassss tasssss tassss!!
Marwanatu ta ji saukan maruka a kumatukan ta. Musa na huci ya kalli Marwanatu ta re da fa'din,
"Za ki min baya ni ko SAI na ci uwar uwar ki yanzun nan? Na san ni dai 'kanwar ki na ke so Mufeeda, ban san yadda akai na koma sonki har na aure ki ba, ki min baya ni ko na kashe ki na kuma