Showing 81001 words to 84000 words out of 130717 words

Chapter 28 - DUHU sark'ak'iya complete hausa novel

slimzy   

23 Oct 2025

180

ta bayyana tana kallon kwaryar saiga ruwa tana kokarin mika masa taji an daka mata tsawa ta bayanta mahaifinsu ne taja da baya ta sunkuyar da kanta kasa juraid da junaid kannen Abraham ne suka bayyana a wajen mahaifin Abraham ya shiga zagaye a wajen cikin wata irin murya Baba yace "Abraham"ya kira sunansa be amsa ba saboda tsananin fushi da tashin hankali da yake ciki zuhraliyya ta zube a gaban mahaifinsu "ina neman agajinka baba da ka kwance yaya Abraham ka duba halin da yake ciki sanan kayi masa uzuri da soyayya"gyaran murya baba yayi yana kallon wasu hawaye dake fita a idon Abraham yace "zan kwanceka amma ba yanzun ba Abraham sai zuwa wani lokaci sai kuma kayimun alkawari akan wanan bil'adamar"Abraham bece komiba hannuwansa sun kage a bankare yake ya kauda kansa gefe bayaso yayi magana saboda zugi da rad'adin dake cikin zuciyarsa a dankare"mahaifin Abraham dariya yayi ya bace ganin yadda Abraham yayi zuhraliyya ta mike tace"yaya ka kwantar da hankalinka zan daukar maka fansa akan cin amanar da husnah tayi maka "ta jinjina kai yayi ihu yayi gunji zuhraliyya tayi wani girgiza ta kara tsawo sosai ta dauki kwaryar ruwa tana shayar da Abraham yasha sanan ta koma daidai yadda take ta bace,

******
momy na parlor yaseer ya fito Baya cikin kwanciyar hankali daka kallesa zaka hango damuwa a tare dashi momy tace "ah ah ya naganka kai kadai?"

"ina kwana momy"ya gausheta a sanyaye,

"lafiya lau ina husnah?"damm gabansa ya fad'i tunawa da Artabun da yayi da ita taki koda tashi tayi wanka yacev"bacci takeyi bata tashi ba"momy ta jinjina kai "Masha Allah lafiya tasamu"yaseer yayi murmushin karfin hali yana kokarin zama momy tace "ai tafiya zakayi gidan ku dan yanzun mukai waya da hajiya zainab muneeba bata da lafiya kwana akayi akanta sanan daddynku na fushi dakai ka kwana a nan"damm gabansa ya fad'i meyasamu muneeba?tambayar da yayiwa kansa kenan kansa ya dau carji hankalinsa ya tashi d'ansa dake cikinta kawai yake tunani sam ya mance da ita ga husnah cikin wanan halin yanzun ya zaiyi? momy tace "kayi shiru naganka a burkice ko kana tsoron kaje matarka ta yankaka ka kwana a nan wajen husnah ne?"ya girhiza kai ya sauke ajiyar zucuya yana laluba aljihunsa yace"Bari in dauki makullina nabarosa daki intafi gidan"momy ta jinjina masa kai ta dauki wayarta ta shiga danne danne,

tura kofar yayi be ganta ba kukanta yakeji a toilet ya tsaya daga jikin toilet din cikin murya kasa kasa yace "husnah husnah meyasa kike kuka?kiyi shiru zanje gida indawo kinji zanzo mu fita anjima da yamma ko?"shiru tayi batare da ta amsa masa ba jin haka yasa ya kira sunanta a hankali ta amsa "naam"yace "muneeba batada lafiya ne shiyasa zan tafi banso intafi inbarki haka ba"idanuwanta jajir ta jinnina kai wato ma wajen matarsa zaije ya gama da ita ya keta mata haddi zai tafi ta rufe idonta kawai tanajin radadi jin shiru ya juya yadau makullinsa ya fice,

a hankali take watsa ruwa zucuyarta cunkushe da tunani ga zafi tanaji a kasanta haka ta fito daga wankan tana d'ingisa kafa yusrah ta turo kofar dakin ta shigo da sallama "Assalamu alaikum"husnah bata kalleta ba tana dingisa kafa tana tafiya a hankali yusrah sakin baki tayi tana kallonta juyowan da husnah zatayi taga fuskar yusrah ta koma mata ta zuhraliyya sakkk.... zuhraliyya na tsaye a gefe,

husnah wani kallo takewa yusrah itako yusrah tsoro taji tace "lafiya Anty husnah kike kallona haka?yusrah ce fa?"fuskar yusrah ta rikide ta koma tata bayan tayi magana husnah tayi zuru to ya dazun taga fuskar zhuraliyya a tare da yusrah? ajiyar zucuya ta sauke "yusrah"tace a sanyaye tana kokarin zama yusrah tace "meyasameki Anty husnah?ko kafar taki ke ciwo har yanzun?"da sauri husnah ta jinjina kai yusrah tace "momy tace ki fito kiyi breakfast kisha maganinki"ta jinjina kai idon yusrah ya sauka akan zanin gadon da yayi kaca kaca da jini cikin sauri ta jita har tanacin tuntube, husnah ta dingisa kafa ta karasa jikin madubi idonta ya sauka akan wadda kw gefenta da sauri ta waiga Baya bataga kowa ba ta kara kallon madubin tayi tozali da fuskar zhuraliyya dik dige dige jiki ta harde hannuwanta bakinta na rawa tace "zhuraliyya"a hankali ta waigo bata ganta ba kyalkyalewa da dariya zhuraliyya tayi cikin dakin sautin dariya taji bata ga kowa ba cikin sauri ta bude wardrobe ta ciro wasu kaya ta zura idanuwantq zuru zuru tana kokarin fita bata ga tahowarta ba gani tayi Tasha gabanta taja da baya da sauri tace cikin tashin hankaki "meye hakan?neyasa kikazo ki tsoratani?shi Abraham din ne ya turo ki"cikin tsawa take maganar dikda yadda zuciyarta ke tsananin bugawa shiru babu kowa kawai ta bude kofar ta fito tana dingisa kafa tin daga nesa momy ke kallon yanayin tafiyarta tana isowa taga kujerun dining dim babu waje ta tsaya momy cikin faduwar gaba take kallom husnah tace "zauna mana husnah?"nusrah ta saci kallon husnah ta kauda kai momy ta nuna mata kujera ta zauna husnah mutum tagani zaune a kujerar tace "momy akwai mutum"a sanyaye momy ta kalli kujerar ba kowa tace "ba kowa"husnah ta had'iyi miyau idonta ya cicciko ita tana ganin mutum zhuraliyya na juyowa ta razana husnah ta kwalla kara ta fadi sumammiya....

*****
muneeba kwance tana sauke numfashi zazzabi ya rufeta tsananin kishi da damuwa yasa ciwon gaske ya kamata yaseer cikin sassarfa ya shigo dakin da sallamarsa ummah ya gani zaune tana rike da hannun muneeba sai Anty sadiya data jefesa da wani mugun kallo ya karasa yana fadin "muneeba sannu meyasameki ummah meke faruwa?"hawaye ne kebin fuskar muneeba tana kallonsa cikin tuhuma gashin kansa ta kalla taji gabanta ya fadi ta mike zumbur ta zauna ummah ta rukota ganin yadda tayi "sannu muneeba sannu kinji?"Yaser jiki a sanyaye yake kallonta ta fita hayyacinta yace "shirya mutafi asibiti"ta fashe da kuka hajiya rabi da sadiya suka fice a dakin yana kokarin riketa cikin tausayawa tace "kada katabani nidai karka tabani"ta kwalla kara yaji tsoro kardai itama ta kamu da aljanun.....

a wahalce Abraham ya warware daga daurin da babansa yayi masa tare da taimakon zabariyya wadda ta kasa jure ganinsa a daure tsananin kaunar da take masa.....


*WANAN LITTAFIN NA DUHU 300 KACAL ZAKI BIYA KI MALLAKI NAKI IDAN BAKI BIYABA KIKA KARANTAMUN BAN YAFEBA*

08036953516
07042277401


*SLIMZY*✍🏻
35
Tallabo husnah momy tayi tace "mikomun ruwan gorarcan yusrah"da sauri yusrah ta dauka ta mikawa momy addua ta tofa ciki sanan ta guntsi ruwan a bakinta ta fesa mata a fuska wata wawuyar ajiyar zucuya husnah tayi ta bude idanuwanta tana binsu da kallo take ta tuno da abinda ta ganni ta kalli kujerar bataga kowa ba ta yunkura jikinta ciwo yakeyi mata momy ta d'agota zafi taji ya ziyarceta a kasanta momy ta tsura mata ido tana karantarta tace "husnah meyake damunki?kafarkice takeyi miki ciwo?"husnah ta girgiza kai take ta tuno da yaseer yadda ya cakud'ata daren jiya ruwa ne ya kawo a idanuwanta Momy ta taimaka mata ta zaunar da ita a kujera tace "fadamun meyake damunki?wanan aljanin yazo ne?"sunkuyar da kai husnah tayi hawaye na zubo mata hankalin hajiya saude yayi mugun tashi tace "kifadamun yaseer yayi miki wani abu ne?"gyada mata kai tayi momy ta soma tafa hannu ta kalli yan matanta biyu tace "kubani waje"suka bar wajen tace "yaseer ya taba jikinki ko?"ta jinjinawa momy kai ta fashe da kuka tace "nafada masa banaso kada yayimun shine yayi fushi ni kuma banason yayi fushi kinga yayi hatsari saboda ni"mommy ta jinjina kai tace "tabdijan lallai yaseer zanci ubansa a gidan nan wato ko kunyata baiji ba ya kusanceki? innahlillahi wa innah ilaihi rajiun"husnah ta share hawayenta ta sunkuyar da kai momy ta matsa mata da plate din soyayyen dankali da kwai ta had'a mata tea mai zafi cike da tausayawa "ci abincinki kinji?kirabu dashi zaizo gidan nan ya sameni"husnah cakula abincin takeyi gaba daya hankalinta baya wajen ta juyo ta kalli plate din abincin wasu tsutsotsi ta gani cikin plate din manya manya suna yawo ta kalli cup din wani irin ruwa bakinkirin ne ciki ta kalli momy,"ci abincin mana husnah"girgiza kai husnah tayi tace "momy tsutsotsi ne gasu nan cikin kwanon bazan iyaci ba"momy ta kalli dankalin ta kalli kofin ruwan tea din"girgiza kai tayi ta mike tabar wajen inuwar mutum kawai ta gani a gabanta tana d'ago kai sukai ido hudu da Abraham zabura tayi ta mike wani irin kallo yakeyi mata wasu jijiyoyi ne koraye suka fito cikin idonsa wajen bakin idanuwansa ya koma mai ruwan toka farin kuma ya koma ja ta matukar tsorata momy ce ta dawo da karatun kurani yayiwa momy wani kallo ya bace,
a furgice Momy taga husnah tace "yadai husnah?"ta girgiza kai tace "momy banajin yunwa Bari inje wajensu yusrah kitchen na tayasu aiki"momy ta jinjina kai a hankali take taka kafarta ta girgiza kai kawai ta shiga laluben layin yaseer bata samesa ba dole zataje gidan su yau din nan....
*****
rungume muneeba yayi cikin sigar lallashi yace"kiyi shiru kiyi Hakuri nima bansan cewar hakan zai faru zam kwana can ba banje da niyyar kwana ba ankira malam ne mai bada magani shine na tsaya in shafawa husnah magani tunda ni mijinta ne"tana kokarin kurban ruwan tea batasam lokacin data furzar ba ta shiga tari sakamakon sarketa da yayi idanuwanta suka firfito ya rukota"lafiya?menene muneeba?"yake tambayarta cikin kulawa tace "yaseer ni yanzun kake fadawa cewa ka shafawa husnah magani?"wani kishi ne ya rufe mata idanuwa tace"kaje kaci amanata kenan?me kukayi daga shafa maganin?"cikin daga murya take masa magana abinda yaseer ya tsana kenan a rayuwarsa ya harzuka cikin bacin rai yace "kwanciya nayi da ita ko itadin ba matata bace?ko karuwa ce ita?"bude baki tayi tana kallonsa ta dafe kirjinta hawaye ya soma zuba a idanuwanta tace "yaseer ni kake fadawa ka kwanta da husnah?"

"na kwanta da ita me zakiyi?"yace yana kokarin mikewa ta rushe da kuka har ya kai kofa ya tsaya tausayinta yad'an kamasa dikda haushinta da yakeji ta yaya zata rinka challenging dinsa?yasan tana bashi tausayi saboda cikinsa da take dauke dashi ganin ya tsaya kawai ta soma wani irin tari tasa hannunta a wuyanta da sauri ya dawo cikin dakin "kingani ko?kinga abinda nake fada miki muneeba meyasa kikeso ki kashe kanki ne akan abinda Allah ya halarta?husnah fa matatacw kuma kece kika matsamun da bimcike yasa nafada miki abinda nafada miki har ya bata miki rai"ta sunkuyo kawai ta soma kwara amai a wajen ya dafe kansa daya dau zafi,ya furgar da iska mai zafi daga bakinsa ya dafe kansa ya runtse idonsa husnah ya tuno yadda ta mike tana d'ingisa kafa ko wani hali take ciki oho,tambayar da yayiwa kansa kenan sam bayason nisa da ita matsowa yayi ya zubawa muneeba ido yadda take kwara amai tana gamawa ta durkushe ta soma myrkususun ciwon ciki hankalin yaseer yayi mugun tashi nan ya tube rigarsa kasantuwar weekend ne ba aiki ya soma gyara wajen sanan ya dawo ya ciccibeta ya nufi toilet da ita da kansa ya tube mata kayan jikinta ta faki idonsa tayi murmushi dikda tsananin kishin dake cin ta tayi hakan ne dan ta d'aga masa hankali tsuru yayi da ido yana kallonta fuskarta ce take masa gizo tana komawa husnah yasan ba husnah bace tsabar tunanin husnah da yakeyi ne ya janyo hakan ko taci abinci ma bai saniba yayi mata wanka ya fito da ita ya nad'eta a towel sanan yana kokarin fita cikin murya mai tsananin Jin jiki tace "sweetheart karka tafi kabarni nasan nibaka sona dama husnah kakeso"cak ya tsaya badan ransa yaso ba ya dawo cikin dakin ya zauna gefen gado ya cije lebe yana kallon kiran momy ya kasa dauka tsoron me zata fada masa yakeyi haka kawai yake jin kansa cikin fad'uwar gaba....

******
daga kitchen ta fito tana jin fitsari nusrah tace "Anty husnah ina zakijene naga har yanzun kina dingisa kafa"murmushi tayi "fitsari nakeji nusrah yanzun zan dawo ai naji sauki"ta fito daga kitchen din yusrah na ganin ta fita ta matso kusa da yar uwarta tace "nifa a tsorace nake da Antu husnah gani nakeyi kamar ba ita bace kinsan aljanun nan"nusrah tayi ajiyar zuciya tace "haka ne amma fa yau kam tabbas itace saidai alamunta sum nuna tana cikin damuwa"suka girgiza kai dukkansu suka cigaba da aikinsu,

tana shiga dakin kofa ta rufe cikin sauri take kokarin shiga toilet din taga mutum kwance kan gadonta ta murza idonta "wanene waye wanan kwance akan gado na"a sanyaye tayi maganar d'agowa yayi daga kwanciyar da yayi kafin kiftawar ido har ta gansa a gabansa cikin fargaba da faduwar gaba take kallonsa ta tsaresa da Ido shima ita yake kallo saidai baizo mata a kamar ban tsoroba a kammanninsa ta gansa fad'awa jikinsa tayi ya tureta gefe tsananin tausayinsa yasa batasan lokacin data fada jikinsa ba kallomsa takeyi cikin tsananin mamaki ya girgiza kai ya cije baki fuskarsa tayi bakin kirin yace"Babu sauran soyayyarki a cikin zuciyata husnah"dam gabanta ya fadi tayi masa wani kallo ta kauda kanta gefe bugun zucuyarta ya tsananta yace"kinci amanata husnah dama ku bil'adama haka kuke amma zan koya miki hankali zakisan kin cutar dani husnah inaji ina gani jiya kika mikawa d'an uwanki bil'adama jikinki ya kwanta dake lokacin da kike tsananin kaunata kin mance yadda naso in kusanceki kika hanani?"hawaye ke zubowa a idanuwansa yana kallonta jikinta a sanyaye momy ta turo kofar ta shigo ganinta tsaye cak yasa tace"lafiya?"girgiza kai tayi bata gansa ba yana cikin dakin kuma cikin jin haushinta yake kawai ya shige jikinta, momy tace "husnah zan fita zani gidansu innah daga nan zan wuce gidanku can akwai maganar da zamuyi"jinjinawa momy kai kawai akayi ta fice dikda jikinta bai bataba tasan wanan ba husnah bace saidai ta kasa gasgata hakan tana fita ya fita daga jikin husnah dakin ne ya shiga jujjuya mata cikin minti biyar kawai taga ko ina ya zama kogi ruwa nayo kanta ta fito aguje nusrah tana kokarin riketa ta bankadeta ta fadi kasa waje tayi tana gudu kamar zararriya nusrat ta window ta leka tana kwalawa mai gadi kira "karka bar Anty husnah ta fito"

Abraham harde hannuwansa yayi a kirjinsa daga gefe yana kallon yadda ta fita a hayyacinta tsananin tsoro da furgici ta kalli gidan sauyawa gidan ya shigayi wasu dogayen bishiyoyi take ganinta wajen,yacev"husnah saina koya miki hankali sai kinsan baacin amanar aljani sanan wanan abun dake cikin mararki saina rabaki dashi"yana kallonta cike da tsana,

maigadi yace"ina zakije husnah?"fuskar mai gadin ce ta koma mata Abraham fadi takeyi "nidai karabu dani kabarni in fita karka sake maidani duniyar Aljanu kaji ina tsananin sonka bazan iya rayuwa dakai ba jinsin mu daya ba kalli yadda muke cikin daji nida kai ka maidani wajensu momy"sakin baki mai gadi yayi yana kallonta yusrah kuka takeyi ta kasa matsawa wajen husnah wadda ta runtse idi ihu kawai takeyi tana fuzge fuzgen zata gudu....

*****
muneeba kwance a kirjin yaseer yana wasa da gashin kanta tunanin husnah yakeyi inama itace haka ta saki jiki dashi suyi soyayya? yana tsananin son matarsa tunowa da daren jiya yasa yayi wata ajiyar zucuya hade da murmushi dago kai muneeba tayi ta zura masa ido baima san tana kallonsa ba wayarsa ce ta shiga ruri tunanin ko momyce yakeyi yana kokarin tashi muneeba ta rungumesa sosai batasi yabarta yadan matsa yace"wayata kw ringing bari in duba"tadan matsa ranta a bace tana kallomsa ganin number yusrah yasa yayi saurin dauka yace"hello?"kafin yusrah tayi magana yaji ihun husnah da sambatun da takeyi taba fad'in ni bazan zauna a dajin nan ba ku kyaleni"cikin rudewa yusrah tace "yaya yaseer kazo kuzo Anty husnah ce momy kuma ta fita bata nan gashinan zata fita tabar gidan"innahlillahi wa innahilaihi rajiun ya furta a zucuyarsa yace "gani nan zuwa kada kubari ta fita kiyi magana da malam shuaibu mai gadi"ya dire wayar ya ture muneeba ko ganin gabansa beyi ya zura rigarsa ya fice muneeba wata Ashar tayi tace "wato dole ma ta mike tsaye akan yarinyar nan yanzun suna soyayyarsu itada mijinta tana cikin nishadi shine zaa kirashi yaje batada lafiya?aljanu karyar banza ta duro Daga gadon yau bazaa kwana ba gidan boka zataje kota halin yaya...

*****
cikin farin ciki ummah hadiza ke magana da hajiya saude tana fuskantar innah "tabbas wanan shawara ce kika kawo hajiya saude kawai ayi tarewar yaseer da husnah su tare a gidansu inyaso maganar magani wanan ba matsala bane ni zan koma gidan da zama kawai tare da nusrah ko yusrah harta rabu da aljanin"momy ta jinnina kai cike da gamsuwa tace "bazan lamumcu iskancin banza ba kar qzo ayi ciki a gida na daga nan can gidan nasu zani insamu zainab akan maganar nan nasan batada matsala zata amince"innah washe baki kawai takeyi tanacin doya da miya suka cigaba da tattaunawa

*****
dik yadda yaseer yaso ya gane hanyar gidansu ya kasa cikin mota yake dik kwanar da yayi sai yaga wajen sai fili ko bushiyoyi ya dimauce cikin tashin hankali yake"fitowa yayi daga motar kawai yana kallon gabas da yamma kudu da arewa kansa juyewa yayi besan inda zaibi ba ganin bishiyoyi na zagayesa yayi kawai..... Abraham ne ya fito masa yana dariya "kaji dadin kwanciya da matar aljan ko?har kayi nasarar yi mata ciki amma ka kwanta da ita na karshe nine zan zama gurbinka a wajen danginka da matarka da ita husnah bazasu sake ganinka ba"yana gama magana ya daga hannunsa wata igiya ya gani hannunsa yana jujjuyawa zai bude baki yayi addua ya kasa sakamakon harshensa daya cika bakinsa sai dariya da Abraham yake masa cike dav tsana.....


*WANAN LITTAFIN NA DUHU 300 KACAL ZAKI BIYA KI MALLAKI NAKI IDAN BAKI BIYABA KIKA KARANTAMUN BAN YAFE BA*

08036953516
07042277401



*SLIMZY*✍🏻
36
Rungumar yaseer Abraham yayi suka bace cikin minti biyu ya gansa cikin wasu bishiyoyi masu tsawo da tsananin DUHU kalle kalle yaseeer yakeyi cike da tsoro kukan tsuntsaye ne kawai yakeji a wajen Abraham cikin kakkausar murya yace "a nan zakayi rayuwa yaseee kayi kuskuren shiga gonata kayi kuskuren son matata kayi kuskuren kusantarta"yaseeer ya runtse ido gumi kawai ke karyo masa yayi yunkurin taka kafarsa ya kasa dariya Abraham yayi yace "kasan inane nan?"yaseer ya kallesa yace"nan ba duniyar mutane bace

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login