Showing 24001 words to 27000 words out of 130717 words
BONUS PAGE NEXT PAGE SHIKENAN
*SLIMZY*βπ»π *DUHU....*π( *sark'ak'iya*)
*HWA*
*SLIMZY*βπ»
wattpadslimzy33
Daga Marubuciyar
π¦ *KADANGARUWA*π¦
*BONUS PAGE*
*11*
muneeba zaune a parlor ta dora kafarta daya kan daya tana daddana waya wani karamin mini skirt ne a jikinta ko rabin cinyarta bai kaiba sai Riga iya cibiyarta sai zuba kamshi takeyi na daukar hankali tana taunar chewing gum haka kawai takejin faduwar gaba batasan dalili ba sam hankalinta bai kwanta da wanan tafiyar da yaseer yayi da hafeex ba ta tura masa hotonta nicked dik dan hankalinsa ya tashi ya dawo gida tajishi shiru har tasa kaya hakan yasa tayi tsaki tayi dialing wayarsa idanuwanta sunyi jajir kishi ya turnuke ta....
yaseer na tsaye daga dan baya kadan duba da mutanen dake tsate tsaye a wajen wani daga cikin mutanen yace "wanan yarinyar mahaukaciya ce kuma daga daji take inba haka ba mai zaisa ta rinka kiran wani Abraham wai dan jinsin jinn Inba mara hankali ba wa zaiyi wanan"hafeez ransa ya Baci an kira Asmau da mahaukaciya ya juya yaga mai maganar ya cafki wuyansa ya shake"kar bakinka ya kara kuskuren kiran Asma'u da mahaukaciya idan ba haka ba wallahi saina hada maka jini da majina"ganin yadda idanuwan hafeez sukai jajir yasa mutumin yin shiru Yana mazurai da idanuwa hafeez ya hankad'asa ya nufi wajen husnah ta mike da sauri hawaye shabe shabe a idanuwanta tana kallon hafeez a sanyaye tace 'niba mahaukaciya bace inada hankalina kuma wallahi gaskiya na fada Abraham mijina ne ina matukar kaunarsa aka raboni da duniyarsu aka kawoni wanan duniyar sakamakon yan uwan mijina da basa sona waini ba jinsin su bace"damm gaban hafeez ya fadi yaseer ne ya dire wayar muneeba gaba daya haankalinsa ya koma gida yadda ta zuba masa shagwaba da kukan karya ya ture mutaneb dake tsaye yacev"dalla malam kazo mutafi kazo ka tara mutane ashe yarinyar ma....."bakinsa ne ya tsaya cakkk yana kallonta yadda hawaye ke malala a idanuwanta kamar an bude fanfo wani irin faduwar gaba ya tsinci kansa kallo daya yayi mata ya kauda kansa bugun zuciyarsa ya tsananta samun kansa yayi da kara juyawa batare da yasani ba,
momy ture jamaar wajen tayi ta karasa tana fadin "yaseer wai nikam lafiya ina hafeez din?"cakk bakinta ya tsaya gabanta na mugun faduwa idonta ya sauka akan husnah da hawaye ke malala a idanuwanta tace "Dan Allah ku taimakeni ku tayani neman mijina"dammm gaban momy ne ya yanke ya fadi tana kallonta Ido cikin ido husnah itama kallonta takeyi cikin wani yanayi Abraham ne ya karaso wajen yana waige waige da karfin gaske ya kira sunanta"HUSNA!!!" waige waige husnah keyi ta zabura tana kallon cikin mutanen dake tsaye momy kuwa tuni hawaye ya wanke mata fuska ta kai hannunta yana rawa tana kokarin rukon husnah ran yaseer a bace yace "momy mahaukaciyar zaki taba kema kinaso ki biyewa hafeez Kenan daya haukace da soyayyar mahaukaciya kinajin abinda take fada"momy ta juya tana kallon yaseer idanuwanta jajir hawaye sai ambaliya sukeyi a fuskarta husnah a sanyaye tace "bugun zucuyata ya tsananta bansan meke shirin faruwa dani ba inajin mijina a kusa dani amma nakasa ganinsa saidai inaji a jikina dik inda yake Yana tare dani Abraham kazo katafi dani kaji bazan sakeba karka rabu dani narjisu ta fito dani tabarni a nan takeso ta rabamu"kamar zautacciya take maganar ta fita hayyacinta fuskarta tayi jajir dankwalin kanta ya Zame gashin kanta ya barbazu a bayanta ta durkushe yaseer ya matso kusa dasu yace "lafiya momy?"momy tayi murmushi ta tsugunna ta ruko hannunta kanta na cikin kafafuwanta tacev"husnah"a sanyaye gabanta na tsananin faduwa bugun zuciyarta sauri da sauri fatanta ya zama husnarta ce husnah da sauri ta dago tacev"naam Abraham ka ganni?"sunayin tozali da momy taga bashi bane ta fashe da kuka tace "a ina kikasanni kikasan sunana"momy cikin farin ciki tana kuja ta juyo tacev"yaseer Allah ya amshi adduarmu da mukayi shekara da shekaru yaseer yau Allah ya karba"yaseer kallon momy yakeyi cikin rashin fahimta ya kalli hafeez Wanda ke tsaye kamar mutum mutumi yace "anya momy me kikeso kice kin Santa ne?a ina momy dan Allah kuzo mubar nan wajen"yace a kufule yana kallon agogo gaba daya ya rasa Gane kansa tunda yayi tozali da wanan yarinyar momy ta girgiza kai tace "husnarka ce yaseer,husnah yar uwarka kuma matarka da akai muku aure tun haihuwarta wadda ta bace tanada shekara biyu yau da batabta kimanin shekara sha takwas kenan"yaseer yayi shocked yana kallon momy da takeso itama kanta ya juye a fusace cikin zafin rai da zafin zuciya yace "momy wai meyasa kukemun zancen wata husnah da bansanta ba idan ma da ita na saketa!!!"gaban momy ya fadi ta zabura ta shararawa yaseer mari "ka tafka kuskure babba yaseer meyake damunka?koda yake babu laifinka amma wanan yarinyar husnah ce "husnah kallonsu takeyi kamar tababbu itama ta juya tana kallon hafeez da idanuwansa suja kad'a sukai jajir kamar gauta,
yaseer ya dafe gefen fuskarsa cike da takaicin momy ya koma gefe ya Shiga dialing number muneeba....tana kishingide tana kallon tashar star life taji vibration da sauri ta dauka cike da shagwaba tace "sweettttt ka dawo ne nazo na bude maka kofa?"tana kokarin mikewa tsaki taji yaja tace "lafiya dai ko?"idanuwansa jajir yake kallon momy rungume da husnah yace "inafa lafiya ni dik nakosa in dawo inji duminki ga momy nan ta biyeea hafeez daga zuwa zamu wuce akwai wata budurwarsa shine muna zuwa fa momy na ganinta ta kirata da husnah ta amsa wai husnarta ce data bata"zabura muneeba tayi ta kalli wayar taga tabbas waya takeyi ba kunnenta bane tace "husnah?wace husna ce tata kuma babu wata husnah sweet karka kuskura ka yarda ni babu wata husnah"ta kashe wayar ta zube Turus cikin tashin hankali ta tuna da maganar da boka nakan tudu ya fada mata akan husnah na nan da rai tana wata duniyar ta zabura kamar zararriya ta nufi bedroom dinta cikin sauri ta zaro after dress abayarta ta zura ta nufi sashen mahaifiyarta,
yaseer kara burkicewa yayi yace "gaskiya bazai yuwuba ga muneeba can ta burkice fatansa karta rikice masa bari yasamu momy mutane dankam wajen.... Abraham ne ya bullo ganin jamaa babu mai ganinsa sai husnah tana ganinsa cikin farin ciki tayi tsalle ta share hawayenta gani tayi ya tsaya cakkk yana kallonta yana hawaye ga mahaifiyarta a gefe tace"nasan bazaka taba barina ba nasan zakazo gareni kazo ko?kazo katafi dani kaji nayi kewarka"ta shiga mika masa hannu tana bude hannuwa alamun ya rungumeta ya girgiza mata kai hawaye tagani a idanuwansa mutanen wajen harda masu daukar husnah video cakk ta tsaya ganin yana hawaye yana kallonta yace mata "ki kwabtar da hankalinki husnah dik inda kike ina tare dake gani nazo gareki"murmushi sukaga tayi a kufule yaseer yace "momy Dan Allah kuzo mubar nan wajen mubar wanan mahaunaciyar"wani kallo Abraham yayiwa yaseer wanda baisan Yana ganinsaba cikin zuciyarsa yace da sannu zan shayarvdakai mamaki momy tace "ai kamata zamuyi mutafi da ita saboda ka duba halin da take ciki wanan ya tabbatar mun da cewar husnah aljanu ne suka sacemun yarinya"ta fashe da kuka tana laluben wayarta hafeez ya nisa zuwa yanzun mugun haushin yaseer yakeyi dakyar ya hadiyi miyau yace "momy mutafi da ita"galala yaseer yayi husnah ta turje a kasa tana tsananin tsoronsu tace "ina zaku tafi dani?kunsanni ne ko kuma kunaso ku rabani da mijina ne?"momy ta girgiza kai takai hannu zata shafata husnah ta ture hannunta taja da baya ta matsa jikin Abraham gabaki daya ta rikice ta makarkalkale Abraham yadda tayi da hannunta ya Basu mamaki rungumeta yayi sosai yana sauke numfashi yana shafa kanta cikin takaici babu yadda ya iya haka yace "tare zamu tafi tafi dik inda kike a fadin duniya tare zamuyi rayuwa,ruwa da iska rani da damuna babu abinda zai rabani dake husnah"ya shafa kanta ya mike....
Alhaji badamasi ne ya shiga dakin momy bai ganta ba ya fito ya dudduba bai ganta ba kitchen ya laika mai aikice keta faman had'a abincin rana tana ganinsa ta tsugunna "Barka da war haka Alhaji"
"barka,ina zainab take?kota shiga sashensu yaseer ne na duba dakinta bansameta ba gashi nan ma babu ita"jimm kadan tayi tace "tare suka fita da yaseer bata dan jin dadi ne kamar sunje asibiti"
muneeba ce ta shigo cikin sauri ko ganin gabanta batayi tana ganin daddy ta kirkiro murmushi ya washe baki yace "munee kece da rana tsaka"
"ehh daddy na shigo ne can din shiru"jin motsi ya fito da hajiya rabi taba ganin Alhaji badamasi ta natsu ta kirkiro kunya ta tsugunna ta gaisheshi yacev"yanzun nake tambayar inda zainab take ashe ta fita"ummahn tace "hmmm ai bata fadamunba da zata fita"yayi jimmm bata fada ba?yace "mai aikinta tacemun taje asibiti batada lafiya"a ran hajiya rabi tace bakin ciki zai kasheta saima an daura aurenmu gobe nida kai alhaji badamasi katse mata tunani ringin wayarsa tayi ta kalli muneeba wadda keta gumi ta kosa daddy ya kauce ta labartawa momy tashin hankalin daya duso ta daddy yace"gashi tana kirana "
"hello zainab yanzun nadawo gida da rana ina tambayar inda kike kina ina ne?"momy ta share hawayenta tace "Alhamdulillah gamunan dawowa"daddy gabansa ya fadi jin muryarta a dishe alamar tana kuka yace"lafiya kike kuka ko har yanzun baki hakura akan maganar Aurena ba?"ta girgiza kai kamar Yana ganinta tace"yau shekara goma sha takwas rabonmu da husnah yau Allah ya had'a fuskokinmu nida yata can na tsinceta "ta fada masa wajen wani shock yayi yacev"what?husnah fa kikace kin tabbatar husnah kika gani zainab?"zaro ido hajiya rabi tayi ta dafe kirji ta Kasa boye mamakinta da tsoronta a fili tacev"husnah kuma wace husnah data mutu kodai taga yar mutane tanaso ta daukota ta laqaba maka alhaji"dagawa hajiya rabi hannu yayi yacev"gani nan zan sameku a wajen bari inzo"ya kashe wayar jikinsa na rawa anga husnah idan yaje wajen ya tabbatar zaigani in husnah ce iidan ba ita bace ficewa yayi cikin sauri yabar hularsa a parlor,
muneeba ta rushe da kuka "ummah nashiga uku husnah fa husnah ta dawo husnar da akwai auren yaseer akanta shikenan munzama mu biyu kedashi"ummahnta ta rungumeta cikin tsananin bakin ciki da hassada tace "husnah bazata taba zama mallakin yaseer ba indai ina raye husnah da mahaifiyarta bazasu taba farin ciki a cikin wanan gidan ba harabada ki share hawayenki"ta share mata hawaye Anry sadiya kanwar hajiya rabi ce ta shigo cikin parlorn tacev"meye na kuka keda yaseer ke hannunki ko babu boka babu malam kissa kadaib ta isheki ki kwace miji kuma kinadani"ta bugi kirji muneeba gaba daya a rikice take.....
******
ganin taron jamaa yasa daddy ya parker motarsa daga nesa ya fito yana taka kafafuwansa ya shiga turmitsitsin mutane tun daga nesa idonsa ya sauka akan husna wadda kanta babu dankwali ya kalli goshinta ya haska masa fuska tabbas wanan yarsa ce husnah yana tura mutane ya shiga hajiya zainab ta fashe da kuka ya kamo hannun husnah ba musu ta mike ta rikesa Abraham na rike da dayan hannunta ta juya tana magana daddy sakin baki yayi Yana kallonta yadda take magana kamar zararriya tacev"tare zamuyi rayuwa ko mijina?nasan bazaka barni ba kaji nifa bansan wadanan mutanen ba amma zan bisu tunda kace tare zamuyi rayuwa"
"innahlillahi wa innah ilaihi rajiun"daddy yacev tabbas Aljanu ne suka sace masa yarsa ya ruko hannunta cikin bakin ciki ya waiga Yana neman yaseer ta hangensa gefe yaseer na mamakin yadda daddy ya biyewa momy zasu dauki wanan yarinyar mara hankali yace "yaseer zo nan mu riketa mukaita mota"hannunta ya sumbule a jikin na Abraham ta turje yaseer ba yadda zaiyi cikin bakin ciki ya fuzgeta yayi mota da ita hafeez yayi ajiyar zuciya burinsa ya cika muradinsa ya ganta yanzun yasan Inda zai ganta ashema ta gida ce yau zai labartawa ummahnsa labari mai dadi kasan zucuyarsa mugun haushin yaseer yakeyi ya jefata a mota ya rufe daddy ya zauna a gaban mota yaseer ya karbi key ya tada motar hafeez da momy mota daya suka shiga,
Abraham mikewa yayi yana yawo a sararin samaniya a sama yana kallon yadda motarsu husnah ke tafiya dole zai koma duniyarsu zaije yayi bankwana da jinsunsu zaije ya azabtar da narjisu kafin daga bisani yazo su shimfida rayuwa sabuwa shida matarsa husnah.....
narjisu ce cikin jinsinsu tana numfarfashi jin kugiya na ihu tasan Abraham na hanya ta dubi hajiya babba tacev"Abraham ya zama nawa tunda aka dauramun aure dashi saidai nasan bazai yafemun ba zai azabtar dani amma rabbas tsugunu bata kareba dan baxansa idon ganinsa Yana rayuwa da jinsun bil'adama ba"zuhraliyya hawayen rashin husnah takeyi ta saba da ita sosai yanxun ya zaayi ta ziyarci husnah?ya zaayi taje ta sanar da ita shirin narjisu?dibbbb Abraham ya sauka a cikinsu yayi kan narjisu......
******
fitowa da husnah sukayi momy da hafeez yaseer kuwa sashensu ya nufa muneeba na ganin haka ta nufi sashenta ko kallon inda husnah take batayiba tsananin kishi daya rufe mata ido burinta kawai ta shiga ta shiryawa yaseer maganganu tayi masa kuka,
daddy gefe ya koma gidan iyayensa ya kira ya sanar musu da ganin husnah da yan uwansa maza da mata ya shiga kiran waya yana fada musu ganin husnah....
kalle kalle husnah keyi a cikin gidan sam hankalinta yaki kwanciya gefe da gefe take kallo ko zatagansa daddy yace "husnah"ta waigo tana kallonsa yace "menene?"ya ruko hannunta tace "mijina nake nema"murmushi yayi yace "ga mijinki can ya shiga sashensa wajen yar uwarki mijinki yaseer"tana kallonsa wani iri tace "sunan mijina Abraham ba yaseer ba dan jinsin jinn"gaban daddy ya fadi hajiya rabi kuwa ji tayi tamkar ta fashe kissa kawai zatayi amfani dashi wajen ribatar zucuyar daddy akan husnah kar ya taba yarda yarsa ce....
yaseer na Shiga muneeba ta shigo ta fada jikinsa ya cire mata rigar jikinta kamshin turarenta ya baibaiyeshi yaja numfashi ya sauke ta fashe da kuka yana bin kayan jikinta da wani irin kallo idanuwansa sun kankance tsananin damuwar da yake ciki wanda besan daliliba gabaki daya hankalinsa da tunaninsa sun gushe tunda yayi tozali da husnah muneeba ta dago fuskarta hawaye na zuba tacev"ya yaseer yanzun shikenan wanan ta zama husnah bakuyi bincike ba bakuyi komiba kun daukota kun kawota?sanan idan wanan ta kasance husnah shikenan fa mun zama mu biyu matanka"ya rungumeta sosai "cikin bacin rai nake sam ganin yarinyar nan ya gusar mun da tunani nashiga matsananciyar damuwa,muneeba bansanta ba bansan daga inda ta fitoba amma daddy da momy suna lakabamun ita a matsayin matata yarinyar da gabaki daya mahaukaciya ce alamu sun nuna matar aljan ce tayaya zasu lakabamun ita?tou wallahi akwai matsala dan zan samu daddy akan hakan kar hankalinsa ya gushe a kan wanan yarinyar renom Aljanu"wani farin ciki ne ya lullube muneeba ta share hawayenta ta Shiga shafa fuskarsa a hankaki ya runtse idanuwansa fuskar husnah yake gani dazun ji yayi ta hade bakinsa da nata tana sauke numfashi tana tsotson lebensa yana shafa kanta a zahiri yana tare da ita amma a bad'ini hankalinsa ya gushe gaba daya daga jikinsa.......
*LITTAFINA NA KUDI NE KI BIYA KI KARANTA IDAN BAKI BIYABA KIKA KARANTA ZAKI BIYANI HAKKINA A INDA BABU DAN BAN YAFE BA*
*NAIRA 300 KACAL ZAKI BIYA DAN MALLAKAR WANAN LITTAFI*
3126584401
FIDDAUSI MUSA
FIRST BANK
SHAIDAR BIYA 08038953516 KO KATIN MTN TA WANAN NUMBER
DOMIN KARIN BAYANI KI TUNTUBI MARUBUCUYAR TA WANAN LAYI 07042277401
*SLIMZY*βπ»
π *DUHU...*π( *sark'ak'iya*)
*HWA*
*SLIMZY*βπ»
wattpadslimzy33
Daga Marubuciyar
π¦ *KADANGARUWA*π¦
*BONUS PAGE DIK WANDA ZAI BIYA 300 KACAL AKWAI DETAILS A KASA*
*12*
Bakinkirin fuskar Abraham ta koma takunsa da gunjinsa a cikin dajin ba karamin kadawa Aljanun dake nahiyar ciki yayi ba bacewa suka rikayi ganin yadda hayaki ke futa a jikinsa narjisu babu tsoro a tare da ita ta shiryawa wanan fad'an gabaki daya Ahalin jinsin Abraham cikin tashin hankaki suke musamman mahaifiyarsa da tasan lokaci yayi da zata rasa d'an nata cikin Ahalin aljanu yana zuwa ya doso ta ta bude idanuwanta ta daga kanta da gashinta keja kasa ya barbazu ya rufe Mata fuska dikda irin tsoron da take ciki bai hanata jajircewa ba wajen tattaro karfi da wata iska da take tare da ita bude idanuwanta tayi da suma furfito suka koma bakinkirin tamkar gawayi babu alamar fari a idanuwanta wani Abu Baki ke fitowa daga idanuwanta yana nufo Abraham wanda ya kasance mummunan dafi ne dake jikinta dafi irin na macizai Abraham na ganin haka yayi tsalle ya ware tafin hannuwansa wata wuta mai tartsatsi fara tasss take fitowa ya bude bakinsa ya soma Aman wuta narjisu naganin haka ta kidime tayi tsalle zata bace ya mike hannuwansa ya cafko gashin kanta daya kama da wuta yace "ina zakije narjisu..... narjisu ina zakije inace kin shirya fad'a dani kin shirya hallaka kanki da kanki?"cikin daga murya yake maganar babu Alamar tausayi tayi tsalle ta fuzge gashin kanta ta koma gefe tana tsaye tana yawo a iska ta wulwula hannuwanta sama saiga dunkulen abu kamar kwallo mai haske ta wullo masa yasa hannusa ya ware ya kare kansa wanan mulmule ya tarwatse saiga tururi "yace mu cigaba saina karar da karfinki sanan in hallakaki".....mahaifiyar Abraham kiran sunansa takeyi cikin magiya ganin yadda suke karawa da narjisu tace "Abraham kabari kadaina ka dubi girmana ka dubi darajata"Abraham ya kalli mamansa da yake tsananin so abinda ta hanga a kwayar idanuwansa yasa taja da baya ya girgiza kai ransa nayi masa kuna yace "harda sa hannunki mamah wajen rabani da farin cikina wajen dauke husnah daga gareni ku maidata duniyarsu to kin biye musu zako tafka asara dan kin rabu dani kenan rabuwa ta harabada yabzun ma nazo ne inyi maganin wanan ahaidaniyar"da kumbarsa yake nuna narjisu wani abu kamar walkiya ya fito ta haske cikin idanuwanta tayi mummunar kara ta zube a wajen ya karasa gabanta takunsa kadai saida kasa ta ansa ya tsaya a gabanta yayi mugun girma Baka ganin karshen tsawonsa da fadinsa wadu kayoyi ke fitowa ta jikinsa suna hayakin wuta ya shiga cirewa da kumbarsa yana sokawa narjisu tana