Showing 21001 words to 24000 words out of 127932 words

Chapter 8 - DOCTOR SHAZIM HAUSA NOVEL

01 Apr 2025

6691

ta" ya fada  yayin da  yake nufar dakin su, samunta yayi kwance kan gado kamar yanda Aaimah ta fita ta barta, duk ta rufe jikinta da blanket har fuska, ƙarasawa  gaban gadon abie  yayi yana kiran sunanta "Aairah"
"na'am abie" ta amsa mashi tana ɗanjan blanket din ta fito da fuskarta
" ya jikin naki?"
"da sauki abie"
" to Allah ya ƙara  sauki, Idan Abdallah  ya dawo sai ya duba ki kin ji" zanbur ta tashi daga kwance tana fadin
"amma dan Allah abei idan ya dawo dan Allah karka bari yayi man allura, yaba ni mgni kawai" tuni fuskarta ta koma kalar tausayi "to shikenan kwantar da hankalin ki magani kawai zai baki, kinji koma ki kwanta "
" to abie "
" Allah ya baki lafiya  " abie  ya fada hadi da nufar kofa ya fice....

✨SHAZIM ✨

Sai bayan da akayi sallar magrib  su ka bar abnoor shi da Noraiz , direct gidan malam suka nufa domin ammy na chan har da fatima wacce daga school  chan ta wuce
Suna shiga gidan parking su kayi sannan kowanen su ya fito daga motarshi saboda  Noraiz da motar shi yaje eko  wurin shazim
part din malam suka nufa
zaune suka same shi a parlorn shi yana duba wani littafin addini
sallama su kayi hadi da shiga cikin suka nemi wuri suka zauna

Amsa masu sallamar yayi yayin da yake cire medical glass din dake fuskar
gaishe dashi shazim yayi  yana tambayar  shi ya jiki
"Alhmdllh ya aiki"
''Alhmdllh malam''
"to Allah ya taima ka"
" ameen malam"
fira suka shiga yi sai da aka kira sallar isha sannan suka tashi
masallachi suka nufa harda malam  ana gamawa suka dawo ciki,za su nufi part ɗin ummy malam yace  noraiz ya tafi, shi kuma yana son magana da shi, wuce wa noraiz yayi,  su kuma shi da malam suka  shiga part ɗin malam, part ɗin ummy noraiz ya nufa, ammy da ummy ya samu a parlor fatima da yarinye kuma na kitchen
Zama yayi kan sofa kusa da ummy yana mata shagwaɓa akan yunwa yake ji
"ga abinci can su fatima na girkawa"
"gaskiya ni bazan iya jiran su gama ba" ammy tace "to sai dai karka jira ɗin" ummy tace "a'a baza ayi haka ba, bari naje kitchen ɗin baza a rasa abun da zai ci ba kafin su gama "ta faɗa haɗi da tashi ta nufi kitchen ɗin , ammy tace "da kin ƙyale shi ummy, sai kace ba namiji ba "
"A'a ke dai, wasa da ciki ai bai da amfani sai ulcer ta kama mutum"
"wallahi kuwa ummy" jifan shi ammy tayi da pillow.

A chan parlorn malam,
"shazim bana son mu cire hannun mu akan lamarin su zo su yanke maka hukuncin da baka so ba, gara tun wuri ka nema ma kanka masalaha"
"in sha Allah malam,zanyi ƙoƙari,ka basu haƙuri"
"haka kake cewa kullum, har hakan yasa suna tunanin ni ke goya maka baya, kuma miyasa idan sun kira ka ba su samun ka, mansoor ma ya kirani yace yanata ne manka amma baya samu "
"bakomi, ina jin network ne "
"to kayi ƙoƙari ka kira su"da to ya amsa,tashi yayi yace zaije wurin ummy su gaisa, da to kawai malam ya amsa, part ɗin ummy ya nufa, a parlor ya same ta noraiz na kusa da ita yana cin abinci, wuri ya samu ya zauna yana gaishe ta
amsa mashi  tayi cikin kulawa hadi da tambayar shi ya aiki
"aiki Alhmdllh ummy, ya malam  da jiki "
ummy tace " jiki da sauki Alhmdllh  "
"to masha Allah, Allah ya ƙara sauki "
" Ameen" fatima ce ta nufo idan suke, gaishe da shazim tayi tana cema ummy sun gama, ga abinci can kan dinning, da to ummy ta amsa, wurin dinning fatima ta koma tana cewa"ummy na malam fa, part ɗin sa za'a kai masa"
"A'a, zai shi go "bata rufe baki ba sai ga malam ɗin ya shigo, tashi suka yi dukan su suka nufi dining ɗin, bayan da suka gama,shazim ya sake duba jikin malam  ya sake rubuta mashi magunguna
Sannan suka yi masu sallama,suka kama hanyar gida Ammy da shazim mota daya suka koma yayin da fatima da Noraiz suka shiga tasu suma
Suna shiga gida Innah Asabe ta fito tana masu sannu da zuwa da tambayar jikin Malam, nan Ammy ke fada mata jiki da sauki Alhmdllh,  sannan kowa yakama hanyar bedroom dinsa, ita ma Innah Asabe nata dakin ta nufa...
Episode  11_ 12

Har yanzu kwance take kan gado kamar yanda abie ya barta sallah ce kawai take tashi tayi,  Aaimah na zaune kusa da ita tana duba book dinsu na school saboda exam da suke facing, nocking suka ji anayi Aaimah ce tace "waye" daga chan wajen taji ance "za kizo ki buɗe  ko sai kingama tambayar waye sannan"  ba shiri ta sauko daga gadon hartana niyyar faduwa saboda jin muryar wanda ke nocking din bakowa bane face ya Abdallah,  buɗe  kofar tayi tsaye yake jikinsa sanye da  gajeran wando iya gwiwa sai riga mara nauyi mai gajeran hannu
Matsawa Aaimah tayi gefe shi kuma  ya wuce ciki dai dai bakin bed din ya tsaya yana cema Aairah ta tashi, tashi tayi zaune, shima zama yayi bakin gadon yana fadin "minene ke damun ki"
"kaina ke ciwo sai zazzabi, amma naji sauki dan yanzu bana jin zazzabi"
"ok" ya fada yana kallon ta domin yasan karya take allurace kawai bata so
kuma dole sai yayi mata ita ,  hannun shi ya daura saman wuyanta zafi yaji zau "ki ka ce ya sauka zazzabin bayan gashi nan jikin ki da zafi"
"to yaya dan Allah ka bani  magani kawai, wlh bana son kayi man allura dan Allah"
"a haka zaki zama Nurse ɗin ki na gudun allura,wa zai zauna ki yi mashi ita kenan bayan ke ma ba so ki ke ba?"
"dan Allah dai yaya" tafa tana hada hannuwanta
wuri ɗaya alamar yayi hakuri.
"shikenan to" ya fada hadi da ficewa daga dakin
dawowa Aaimah tayi kusa da ita tana cewa "ai kuwa  nasan allurar zai maki , tun da jikin ki har yanzu da zafi" mi Aairah za tayi inba kuka ba , kuka rurus kamar wata ƙaramar ya rinya Aaimah kuma sai ƙara bata tsoro take
tashi tayi daga gadon ta fice daga dakin bedroom din Mom ta nufa, Mom fitowar ta kenan daga bathroom Aairah ta shigo kamar wacce a ka koro,  bed din mom ta nufa ta haye hadi da jan blanket ta rufe  jikinta tana cigaba da kuka
kusa da ita mom ta ƙaraso tana fadin " ke kuma lafiya kamar an koro ki, mikike ma kuka ne"
"Mom ya abdallah  ne zaiman allura"
"Yau ni naga takaina ni kubrah, shine kika shigo kamar an koroki"
Mom bata rufe baki ba sai ga ya abdallah yashi go hannunsa rike da leda,ya je  dakin su bai sameta ba
tada Aairah mom tayi magani ya fara bata da kuwa zai mata allura sun sha buduri har Mom , sai da  yayi mata jan ido tukun a ka samu ta tsaya a ka yi allurar, dama haka yake fama dasu ita da Aaimah In dai a kace ba su da lafiya to fa sai sun kusa tara masu mutane a gidan saboda allur kawai,  amma kullum Iƙirarin su shi ne su zama nurses.
kuka Aairah tasha Ba na wasa ba, sai dai ta kwana dakin Mom Aaimah ma nan ta dawo ta kwanta saboda bata iya kwana dakin su ita kadai...

WASHE GARI...

Alhmdllh ta tashi da jikin da sauki sosai bedroom dinsu ta koma tayi wanka tasa kaya mara sa nauyi
ko da Aaimah ta shigo tana tambayar ta ya jikin
"da sauki sosai"
"to Allah ya Ƙara sauki, hajiyar allura "
harara  ta bugama Aaimah, ita kuwa mi Aaimah zatayi inba dariya ba tana fadin "wallahi sister duk mijin da ya aure ki zai sha fama musamman idan shi likita ne, dan wallahi na san tara mishi mutane zaki riƙa yi muddin baki da lafiya yace xai yi maki allura"
"kice duk mijin daya aure mu dai, sai kace kema allurar ki ke so zaki wani tasa ni gaba kina man dariyar banza"
"ai wlh kinsan gara ni dake wllh"
"wlh karya ne bawani nan"
"to uwayen musu da safiya zaku fara ma mutane musun tsiya da ku ka saba, ba kamar ke Aairah daga samun sauki har zaki fara ɗan banzan surutun da ku ka saba"
Mom ta fada wacce shigowar ta kenan tasame su suna ta gaddamar da su ka saba  "ke kinyi wankan ko ko dai sai kungama musun tukkuna"
"A'a yanzu zanyi" Aaimah ta fada tana nufar toilet ta shiga, kusa da Aairah Mom ta matso tana fadin "ya jikin, duk nama ga kinji sauki tunda gashi harki na musu"
murmushi tayi hadi da daura kanta saman kafadar Mom tana cewa"da sauki Mom, Aaimah ce da raini wayau waini take ma sharrin bana son allura sai kace ita ma so take" murmushi kawai mom tayi tana fadin Allah ya shirye ku,ameen MomAairah ta fada

✨VICTORIA✨

sanye take da uniform din ta, fita tayi daga office din su direct elevator ta nufa  numbobi ta danna  kofar elevator ce ta bude wasu nurses ne ciki shiga tayi ita ma
elevator na tsayawa kowa ya fice alamar sun kawo in da za su , fita tayi itama direct office din Dr Shazim  ta nufa sai da ta zo bakin kofar office din tukun ta tsaya, waige waige tashiga yi alamar rashin gaskiya
sai da ta tabbatar ba mai ganin ta tukun ta sanya key din dake hannun ta ta bude office din da sauri  ta shige ciki saboda jin alamar kamar mutum na tunkaro office din

tsi office din yake alamar ba kowa a cikin sa , sai  ac dake aiki
wurin freezer dake office din ta nufa.
budewa tayi,  cike yake da drinks kala kala, gani nayi ta dauko kwalin daya daga cikin drinks din ta a jiye saman wani dan ƙara min table dake kusa da fridge
Sannan ta sake dauko wani, a ta kaice dai  sai da ta ɗauko kusan kowace color dake ciki sannan ta maida ta rufe. 
Hannu tasa cikin aljihun wandon kayan ta, ta fito da wani gari cikin wata yar ƙaramar roba fari tas dashi , buɗe  marfin kowane kwali  na drinks din tayi sannan ta dibi wannan garin ta zuba ta girgiza,  daya Bayan daya sai da ta tabbatar ta girgiza ko wane ya girgizu sannan ta mai da  ta rufe
maida su tayi ciki ta jera su kamar yanda ta same su, rufe fridge  tayi sannan ta kama hanya ta fice ta nufi elevator ta sake danna numbobi kamar ɗazu sai ga kofar ta bude
sai da gaban ta ya faɗi sakamakwan ganin hidaya da maryam da tayi ciki tasan dole suyi zargin wani abu saboda  a wannan floor din daga office din dr shazim sai na dr kabir sauran wuraren ɗakunan marasa lafiya ne da wurin da patient ke zama dan ganin likita in sun zo, kuma gashi lokacin da  patient ke zama bai yi ba,  an dai buɗe  offices ne domin sharewa da moping.dan doctors ɗin ba bu wanda yazo
kallon kallo suka shiga yima juna ita da hidaya dan ita maryam harara kawai ta bita da ita
martanin harar ta maida ma maryam hadi da jan tsaki ta shige cikin elevator, fita su ka yi dama nan su ka nufo
"Aikin baza harara a duhu, yar wahala kawai" maryam ta fada hadi da jan hannun hidaya su ka wuce , itama tsakin tayi hadi dacewa "oho dai dr ne dai saina rabata dashi,  kuma kema zan dawo kan ki ne inna gama da ita"
Haka dai taita banbaminta a banza har ta kai inda zata sauka

A chan kuma hidaya ce ke ce ma maryam "nifa  kinsan  gani nake Victoria kamar bata da gaskiya?"
"mikika gani? "Maryam ta tambaya
"bakiga tana ganin mu ba duk tawani sha jinin jikinta,  bayan haka ma mita zo yi floor ɗin  su Dr, yanzu ba lokacin fara aiki ba, ni sai nake ganin kamar wani abun tayi"
"hmm haka ne fa kuma, ke ita ta sani chan taje taji da rashin gaskiyarta,ai Allah na sama yana kallon duk wani abu da za tayi, koma mi tayi dan kanta hidaya ita da Allahn daya halicceta"

"Wlh kuwa ita da mahaliccinta" hidaya ta fada abun da ya kawo  su suka shiga yi, suka ture zan chan Victoria gefe

Tana shiga  office din su destiny ta samu  da wasu  daga cikin nurses din da suke  zama office din
wurin destiny ta kara sa tana fadin "sister shigowar ki kena? "
"Eh yanzu nazo, nama yi tuna nin ba kizo ba, sai da naga jakan ki a locker tukun, amma daga ina haka.? "
"Mu fita daga waje na fada maki,nan kinga mutane,  kuma kin san su da bakar gulma yanzu za kiji magana wani wuri."
"haka ne kuma" destiny ta fada tana jan hannun Victoria su ka fice daga office din
sai da suka shiga wani dan corridor ku sa da office din su sannan Victoria tace"daga office din dr nake"
"kai da gaske ki ke"
"da gaske nake mana, kaji destiny na taɓa maki wasa ne, daga can nake"
"Amma ina fatan ba wanda ya ganki  ko, kuma kinyi yanda gurutu yace mu yi"
"Sosai ma kuwa, ai kamar yanda yace nayi haka nayi"
"Yawwa yanzu sai dai mu tsaya jiran sakamako kawai"
"hakane kam, kinga mu koma office kar wani ma ya fito"
"kuma fa haka"
Office din suka koma dumin shirin fita,ba su samu kowa a office din ba duk sun fita , suma basu wani jima ba suka fice..

✨Hidaya✨

Zaune su ke ita da maryam da sauran nurses din asibiti,fira su ke yi kafin doctors su shigo kowa ya kama  gaban sa zuwa in da yake nasa aikin.
suna a nan zaune dr shazim ya shigo shi da dr  kabir da Noraiz, yana gaba Noraiz da kabir na bayan shi
gaishe da su nurses din su ka shiga yi,Noraiz da Dr kabir ne kawai suka amsa masu Shazim kuwa hannu kawai ya iya daga masu
Suna zuwa bakin office din shi briefcase dinsa dake hannun Noraiz ya amsa
saboda  shi Noraiz office din Dr kabir zai wuce
Office din ya shiga,  ko ina fes an gyara sai kamshin  fresheners
tarkacen sa ya ajiye saman table hadi da zama kan chair dinsa,laptop ɗinsa ya jawo ya fara aiki a ciki, nocking  aka yi "Come in" ya ba da izin, hidaya ce ta shigo bakin ta dauke da sallama,hannunta riƙe da  files,amsa mata sallamar yayi "good morning Dr, dama nace zan iya fara turo patient"
kai kawai  ya daga mata alamar eh "ok" ta fada  hadi da ficewa ta koma wurin patient
wurin 12:00 ya gama  ganin patient din da zai gani time din har Noraiz ya dawo office din ,
"Yaya wai baka da wani abun ci ne a office dinnan?"
Noraiz ya fada yayin da yake bude fridge dake office din "to a cici ni bana ajiye komai daya danganci abinci a eko , zaka iya bari Sai munje abnoor tukunnan" kwalin lemu ya ɗauka sannan ya
rufe fridge ɗin , yana fadin "bari nas ha wannan kafin mu tafi" wurin zaman shi ya koma ya zauna hadi da bude marfin lemun, Dr kabir ne ya shigo da sallama a bakin sa  hannun sa ɗauke da  basket din abinci yana cewa "wallahi Momma har yanzu kallon yaro take man, wai abinci tasa aka biyo ni da shi saboda kawai banyi breakfast  na fito ba"
"dama ai kai yaro ne" shazim yafa yana murmushi "haba dai kai ka san wanene yaro wallahi"
"ai duk auta yaro ne"da yake kabir shine auta a wurin momman shi
"lallaima Shazim, wallahi ka rainani" katse su Noraiz ya yi yana cewa
"wallahi Momma ni ta taimaka kamar  tasan yunwa nake ji" kallon shi Shazim yayi yana girgiza kai da fadin
"Allah ya shirye ka Noraiz, duka ƙarfe  12 amma sai wani complain din yunwa kake, sai kace wani karamin yaro"
"Yaya kasan fa ina fama da ulcer" ya fada yana shafa cikin sa
"ulcer ko ragannci?"
Shi dai dr kabir binsu kawai yake da idanu yana murmushi
"to yanzu dai ku kale wannan musun, kai Noraiz zo ka zuba abinci kaci" Dr kabir ya fada
dawowa Noraiz yayi kan sofar da Dr kabir yake , plate ya dauka da serving spoon ya buɗe  food flask farar shinkafa ce,  zubawa yayi sannan ya bude dayar flask din wacce pepper soup ce a ciki,sai da ya buɗe  kowane  flask dake cikin basket din tukun ya koma gefe yana ci, Dr kabir ya zuba ma Shazim yana cema noraiz "wato ɗan tsako sami ka ki dangi ko"
dariya kawai Noraiz yayi
"Ok bakin maganar ya mutu kenan" Dr kabir ya fada yana murmushi, shima dai Shazim murmushi yayi yana cewa "baka san waye noraiz ba a kan abinci"  daga nan su kayi shiru kowa na aikin bama cikin sa
sai da suka gama Dr kabir ya nufi fridge ya dauko masu lemu da ruwa
Shi noraiz ruwa kawai ya amsa saboda ya dauko lemu tun dazu sai da suka gama tsab sannan suka tashi shazim duka tarkacen sa ya haɗa saboda da sun dawo sallah abnoor  zasu wuce shida Noraiz..

✨Aairah ✨

Alhmdllh jiki yayi sauki sosai dan yanzu haka zaune take parlor suna fira ita da Mom da Aaimah wacce taki zuwa school saboda Aairah bata je ba.
abie ne ya shigo daga masallachi sallar zuhur wurin su ya nufa zama yayi kan sofar da Aairah take yana faɗin    "ah lallai jiki yayi sauki Masha Allah" ya faɗa yana shafa kanta
Mom  tace"Jiya kana part ɗinka  da ka ga budirin yin allura"
abie yace "Allah dai ya shirya yaran nan da dan bazan tsoron allura, a haka zaku zama nurses din da ku ke so kuna tsoron allura?"
Aaimah  tace"duk da haka abie mu na iyawa Allah"
abie yace "to Allah dai yasa"
Aairah tace "ameen abie"
sun jima suna fira har wurin ƙarfe 3:00 sannan suka tashi

✨ Shazim ✨

Yau da wuri suka  bar abnoor  saɓanin kullum da sai yayi sallar magrib da isha sannan ya ke komawa gida, duk da  yanzun ma ba gida suka nufa ba gidan malam suka nufa domin su kara duba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login