Showing 27001 words to 30000 words out of 127932 words

Chapter 10 - DOCTOR SHAZIM HAUSA NOVEL

01 Apr 2025

6693

yi  suka bi bayan ta  , Aaimah  tace "wai Aunty uwani  ina Nuratu ne naga kwana biyu idan muka zo bama ganinta"( diyar Aunty uwani nin ce nuratu) Aunty uwani tace "Nuratu na kauye, an  kusa bikinta ina fatan za ku zo"cike da mamaki su Aairah suka ce "aure fa ki ka ce Aunty Uwani, yanzu nan nuratu harta isa aure"Aunty uwani tace
"eh mana,  duk sa'annin ta dake chan duk anyi masu aure har ma wanda basu kai taba ana masu aure, dan dai kawai ku kuna birni ne shiyyasa ku ke ganin kamar bata isa ba" Aairah tace " to Allah ya nuna mana lokacin, In sha Allah kuwa zamu je" haka suka ciga da fira Aunty Uwani na basu labarin ƙauye su kuma suna mamaki har suka kammala jera abincin kan dinning,sallar magrib da aka kira ne yasa su abie nufar masallaci shi da abdallah   Mom ɗakin  Aunty Rabi ta nufa domin gabatar da sallah , su Aairah kuwa ɗakin  Dadi suka nufa domin yin  tasu sallar, sun riga su mom dawowa parlor su da Dadi,suna ta zuba mata surutu su abie su ka shigo hara da uncle mustafa ( kannin abie wanda ke bi masa,  su biyar ne ɗiyan  dadi  abie shine na farko sai uncle mustafa daga nan sai aunty Rabi sai  uncle Ahmad sai Aunty Asma'u itace yar autar su, da Uncle mustafa ne ka ɗai  ke  katsina, kafin Abie ya dawo nan  shi kuma uncle Ahmad har yanzu  yana abuja sai Aunty Asma'u dake aure kano, Aunty Rabi kafin Allah yayi ma mijinta rasuwa  barno take Aure time din   .)  bakin su dauke da sallama suka shigo,amsa masu sallamar su kayi yayin da su Aaimah ke cewa  "uncle ina wuni"
amsa masu yayi cikin kulawa yana cewa "ya school naji yaya yace kun kammala, to Allah ya tai maka yasa a samu sakamako mai kyau" da ameen suka amsa mashi,dadi tace "yawwa mustafa naji daɗin zuwan ka, kamar kasan ina son ganinka kai da Mahammad "
abie yace "to fa mama Allah yasa lafiya "
"lafiya lau,maganar dai da na saba ce,  mu shiga daga ciki" da to suka amsa haɗi da miƙewa suka bi bayan dadi, bedroom ɗin ta suka shiga, wuri suka samu bakin gado suka zauna, kallon su dadi tayi sannan tace"a kullum bazan gaji da maku maganar ɗan  ƴar uwata ba, ba shi da wata a duniyar nan da zai  kalla a matsayin uwa a gare shi bayan ni , ban san wane hali yake  ciki ba, ƴar uwata zata ce ban riƙe alƙawari ba " uncle mustafa yace
"kiyi haƙuri mama,in sha Allah zamu nemo shi a duk idan yake a faɗin duniyar nan"
"mustafa kullum haka kuke cewa, amma har yau baku nemo man shi  ba, kullum sai nayi mafarkin shi yana cikin damuwa, yana buƙatar taimako na" abie yace "ki ƙara haƙuri mama, in sha Allah za'a gan shi, zanje har garin ku, nasan baza'a rasa wanda yasan inda ya koma  da zama ba"
"to shikenan Muhammad, zan zuba ido har lokacin da Allah zai bayyanar da shi" da ameen suka amsa, dadi tace "ku tashi ku koma parlor kuci abinci" to mama suka faɗa haɗi da miƙewa suka nufi parlor, a dinning suka samu su mom, wuri suka samu suma suka zauna,aunty rabi tayi sarving ɗin su , sai wurin karfe 9 da kusan minti 50 sannan suka bar gidan harda uncle mustafa su ka nufi gida,  suna isa gida, baaba larai ta fito tayi masu sannu da zuwa,  kowa ɗakin  sa ya nufa, snacks ɗin da suka zo dashi baaba larai ta kai kitchen ckin fridge bayan ta ɗauki wanda zataci, ɗakinta ta nufa ta kwanta ita ma.
Episode 14_15

WASHE GARI

Tunda suka yi sallar asuba basu koma bacci ba saboda ɗokin zuwa wurin ƙunshi da gyaran kai da za suje, ko da gari yayi haske wanka kawai suka yi suka shirya  sannan suka nufi ɗakin Mom, koda suka shiga basu sameta ba kitchen  suka wuce anan suka same ta ita da baaba larai su na shirya breakfast gaishe da su su kayi, Mom tace"wai ba dai har kunshirya ba"
"munshirya ,tafiya ma za muyi" suka bata amsa
Mom tace"to sai ku bari  kuyi breakfast tukunnan"
Aairah tace "ba fa direct saloon din zamu wuce ba, sai fa munje gidan Aunty Safiya tare da Najma zamu tafi"
"duk da haka dai kujira kuyi breakfast sannan" mom ta faɗa,  da to suka amsa mata,  dole su ka tsaya sai da suka yi breakfast ɗin sannan mudi ya kaisu gidan  ya dawo, basu wani jima ba  saboda ko da su ka je Najma harta shirya su kawai take jira, basu wani bata time ba mus'af  ya kaisu shagon saloon ɗin  da zasu je, wurin ya haɗu babu wani nau in gyaran jiki da basa yi, kama daga wankin kai har izuwa kunshi da gyaran ƙafa......

Wannan Kenan

✨Ammy_Fatima _Noraiz ✨

Zaune suke kan dinning suna breakfast, shazim  ya shigo jikin sa sanye da jogging suit white color,sai p_cap black color ,  wurin su Ammy ya nufo yana faɗin "ina kwana Ammy"
da lafiya lau  Ammy ta amsa mashi "Ammy ai da kun bari na dawo sai muyi breakfast ɗin tare"
"kai da shigowar ka ba yanzu ba, waye zai tsaya jiranka"
"amma Ammy ba gashi nashigo da wuri ba"
"yau koh" Ammy ta faɗa
Noraiz ne ya ce  "yaya da ƙarfe nawa zaka je abnoor  yau"
"yau bazan jeba"
"amma yaya saboda mi"
"haka nan, zamu je wani wuri ne shiyyasa, idan kun kammala breakfast  ɗin,  Ammy ku shirya" Fatima  tace "wannan wane bazata ne  haka yay "
Ammy ma cewa tayi "ina zaka kaimu" murmushi yayi haɗi da cewa "surprise ne, ku dai kawai ku shirya"
daɗi  suka ji saboda  sun san wani abun mamakin ne yake son yi masu bazata dashi, saboda shi idan ya so fa akwai wasa da dariya,  in kuwa baiso ba tofa zaka same shi kadaran kada ham, duk da daman akwai kyakyawar alaƙa tsakanin sa da ahlinsa, wani lokacin in yana tare da su zaka same shi kamar bashi ba,cigaba su kayi da breakfast, shi kuma part ɗinsa ya nufa domin watsa ruwa sannan ya dawo yayi breakfast , san da ya kammala nasa breakfast din dukan su sun shirya shima komawa yayi part dinsa ya shirya cikin wani haɗaɗen yadi wanda yasha ɗinkin  zama ni wurin su ya dawo,  Ammy  ce tace  "kai Masha Allah  ba ƙaramin  kyua kayi ba"
"nagode sosai ammy" gaba yayi yana faɗin "to ku taso mu tafi" tashi su kayi su ka bi bayan shi zuwa  compound din gdn, anan suka samu motar da zasu fita da ita ilya ya gama gyara ta ya fito da ita compound  , nufar motar suka yi, shi ya shiga ma zaunin driver ya yin da Noraiz ke kusa da shi Ammy da fatima kuwa baya suka shiga,  reverse yayi ya nufi gate,  a dawo lafiya su ilya suka shiga yi masu, driving yake , su  Ammy sun zuba ido ne suga shin ina kuma zai kai su, wani katafaren shopping mall na ji da faɗa  ya nufa dasu,sabon mall ne daga gani ba'a jima da fara aiki a cikin sa ba,  parking yayi a parking lot ɗin wuri sannan yace "Ammy ku fito, mushiga ciki " to kawai Ammy tace sannan suka fito,sai da suka fito su duka sannan yace "kowa ya kalli sama" kamar yan da yace haka suka  ɗaga kansu suna kallon saman shopping mall, in da aka rubuta (WHITE HOUSE SHOPPING MALL) da man yan baƙi ammy sauke kanta tayi tana kallon shazim cike da  alamar tambaya, ganin kallon da ammy keyi masa yasa shi yin murmushi yana faɗin "surprise "  cike da mamaki ammy tace "wai ni kam ina zaka kai son kuɗi ne shazim"matsowa yayi kusa da ita haɗi da dafa kafaɗar ta yace"ammy ina da ku idan ban nemi kuɗi ba mizan yi"
"haba shazim business nawa kake "
"Ammy koma nawa nake, wannan ba wani abu bane, ki sa mashi albarka kawai"
"to Allah yasa albarka ya ba da sa'a "da ameen suka amsa su duka, shazim yace "Mu shiga ciki"  ciki suka shiga ya na gaba suna binshi a baya,wani matashin saurayi ne da a ƙalla zai yi kimanin shekaru 27 a duniya ya nufo su, gaishe da ammy yayi da shazim,gaishe da shi  noraiz da fatima su kayi, da fara'a a fuskar shi ya amsa masu, shazim yace "ya aikin hameed?"
"Alhmdllh, komai na tafiya dai dai"
"masha Allah,muje ina son nu na ma su ammy ko wane part"
"ok to shikenan "ciki su ka wuce, wura re ya shiga nuna masu shi da hameed , sai da ya kaisu ko ina a cikin mall ɗin sannan suka ya da zango a office ɗin shi, hameed kuma ya koma wurin ma'aikata ,office ɗin ya haɗu sosai kamar ba office ba, ammy na kan sofa   su fatima na ƙasa kan carpet, shi kuma yana zaune kan swivel chair,ammy ta ce"shazim wuri yayi kyau Allah ya taimaka "
"ameen Ammy"  
ammy tace "yanzu wa zai kula da nan? "
"a kwai wani ƙanin hameed shi  zai kula da nan, hameed kuma noraiz sai su  cigaba da kula da wan can business ɗin amma za su riƙa kawo mashi ziyar dan su tabbatar da komai na tafiya" 
"to shikenan, hakan yayi kyau"
sun jima a office ɗin sai da rana tayi sanyi suka fito,yace su shiga ciki  kowa ya zabi abun da yake so,
da sauri fatima ta  jawo masu cart, suka shiga jidar abun da ransu ke so musamman Fatima da Noraiz, Ammy kuwa shazim ke tura mata nata cart din tana daukar abun da take so, sai da kowa ya dauki abun da yake so,  ma'aikanta wurin suka kwashe kayan suka zuba  masu a booth, sallama suka yi ma su,har parking lot hameed ya raka su,( bayan aikin asibiti shazim yana business sosai tun kafin ya fara aiki da buɗe abnoor yake business, yana sai da motoci wanda hameed ke kula da shi  yana da boutique  da gidan gona sai white house da ya buɗe yanzu, amma ba shi ke kula da su ba akwai masu kula mashida su ) mai makon ya kaisu gida wata hanyar ya kuma sake ɗauka , in da ake sai da  laptop's  ya nufa dasu yana parking suka fito shi da noraiz , su ka shiga ciki, noraiz ya zaɓar ma fatima laptop mai kyan gaske,kuɗi ya biya  suka fito zuwa mota, daga nan wuren bu ɗe ido yai ta kaisu, Ammy ba ƙaramin  dadi tajiba saboda rabon ta da ta shiga gari da sunan miƙe ƙafa har ta manta, sai da yamma likis sannan suka koma gida, godiya suka shiga yi mashi, shi kuma yana cewa dan Allah su bari mana,wannan ai wajibi ne a gare sa daya yi masu fiye ma da haka
Ammy tace "duk da haka shazim, bakaji mi hausawa suka ce ba?, yaba kyauta tukwici, tunda bamu da tukwicin da zamu baka shine muke godiya"
"to shikenan" kawai ya iya cewa , ilya ne da mai bama flowers ruwa suka shigo da kayan da suka zo dasu, su kuma kowa daki ya nufa domin watsa ruwa ,Fatima na shiga ɗaki wayanta dake ringing cikin bag ta ciro,ya dr ne ke kira, katsewa kiran yayi zata kira sai kuma wani kiran ya sake shigowa,picking tayi haɗi da sallama amsa mata sallamar yayi yana cewa"yar ƙanwata ya kike ya gida ya su Ammy? "
"lafiya lau Yaya"
"masha Allah,  ina gaishe da su sosai"
"zasuji Insha Allah "
"miye labari "
"ai ni yaya fushi nake da kai, "
"to fah, kaina bisa wuya ni kuwa mi na ai kata"
"wai ace nayi graduation, Amma yaya ko irin text dinnan na congratulations ban samu daga gareka ba kai da ya mansoor "
"Allah sarki fatima, kiyi hakuri kin ji, so naima ace nazo har Lagos din, amma kuma wasu yan abu bu wa ne suka sha kaina, amma kiyi haƙuri  kinji"
"shikenan yaya bakomi, dama yanzu baka wani ji dani,"
"kai , ya za ki ce haka "
"haka ne mana, yau she rabonka da zuwa Lagos, tun kuna mutunci da ya shazim sosai "
murmushi yayi mai sauti yana cewa"waya ce maki bama mutunci sosai yanzu"
"to baga shi nan ba yanzu baka son zuwa Lagos "
Fatima kenan, ya fada a zuciyar shi  , a zahiri kuwa cewa yayi"fatima yana yin aiki ne kawai ba wani abu ba, amma In sha Allah ina nan zuwa Lagos very soon "
"to Allah ya kaimu ya nuna mana lokacin" da ameen ya amsa fira suka shiga yi daga bisani suka yi sallama, ya mansoor ta kira shima tayi mashi ciwan baki rashin kiranta da baiyi ba, haƙuri ya shiga bata, sun jima suna waya,  
a chan parlor kuwa Ammy ce ta fito daga ɗakin  ta, Innah asabe ta samu a kitchen tana jera kayan da suka siyo, gaishe da Ammy tayi, amsa mata Ammy tayi cikin kulawa,  Inna asabe tace "mi za'a dafa yau da daddare "
"A'a ba sai an dafa komai ba munyi takeaway da muka fita"
"to shikenan "kawai Inna Asabe tace, gyara kitchen din kawai suka yi.....

✨Victoria✨

"destiny wai  kina ganin abun da  gurutu ya bamu yana aiki kuwa, kusan fa wata daya kenan bawani chanji"
Destiny tace"karki damu na yarda da Gurutu, mukara lokaci kawai, idan ma muka ji shiru mu sake Komawa kawai"
"gaskiya  abun da za'ayi kenan gara kawai mu koma"
destiny tace "to shikenan amma mu ƙara lokaci mugani"
 
✨Hidaya✨

Zaune take bakin gado wayar ta dake gefan ta ce ta fara ringing picking tayi hadi da  manna   wayar a kunne tana fadin "hello maryam ya ki ke ya gida"on the other hand maryam tace"lafiya lau hidaya"
hidaya tace  "Masha Allah"
"mi ki ke yine haka naji kamar muryar ki tayi ƙasa? " maryam ta tambaya, amsa hidaya ta bata da "lafiya lau, kawai dai ina kwance ne"
Maryam tace"ok to yayi, ya labari  doctor kinsan kwana biyu ban shigo hospital ba, ina dai fatan kin fada masa abun dake ranki"
sauke ajiyar zuciya hidaya tayi, sannan tace"ina fa maryam,wallahi da na gansa rasa duk wani kwarin gwiwata nake, sai kawai naji na kasa faɗa masa"
Maryam tace"gaskiya hidaya kina da aiki, yanzu faɗa masan ne yake baki wahala"
"hmm maryam kenan dan dai kawai ba ke bace a matsayi na ba ne shiyyasa"
"ba haka bane hidaya, daurewa kawai za kiyi ki faɗa masa" 
"to shikenan maryam zanyi ƙoƙari naga na fada masa nagode sosai"
"bakomi idan ma kin kasa sai mu nemi number shi, kota waya ne sai ki fada masa, fata na kawai shine ya amince dake amatsayin abokiyr rayuwa, in ga ta tsiyar su destiny da Victoria "
"to Allah yasa ya soni koda bai kai wanda nake masa ba" hidaya ta fada
"to ameen sister,  ki cigaba  da adu'a In sha Allah dr naki ne ke kaɗai"
"to Allah yasa" 
da ameen maryam ta amsa mata sun dan jima suna wayar daga bisani suka yi sallama...

✨Aairah_Aaimah✨

Ana kammala masu saloon din da kunshi  mus'af   yazo  ɗaukar  su " kai masha Allah sweetie, irin wannan kyau haka kin kuwa ga yanda kunshi nan yayi kyau?"
"nagode sosai" Aairah ta fada
Aaimah ce tace
"da yake ya mus'af Aairah kaɗai ka sani  shiyyasa kace nata yayi kyau mu ko ka kalli namu, abun yar wariyar launin fata ce"
"No Aaimah ba haka bane, na qalbie ne ya ɗauke man hankali, amma kuma naku yayi kyau sosai"cewa Aaimah tayi
"shikenan ya mus'af bakomi"
"mu tafi koh"mus'af ya faɗa nufar motar su ka yi, Aairah ta shiga gaba,sai Aaimah da najma a baya,
gidan su Aairah ya nufa dasu,  parking yayi a compound , su Aairah suka fita , masu decoration suka samu a compound suna decorating,  main entrance din gidan suka nufa,   koda suka shiga ciki baaba larai da Mom da Aunty rabi suka samu a parlorn, suna aikin zuba souvenirs cikin jakunkuna masu dauke da sunan Aairah da Aaimah, shiga suka yi parlorn bakin su ɗauke da sallama, amsa masu sallamar su  Mom su ka yi, da gudu su Aairah suka nufi Aunty rabi, suna fadin "oyoyo Aunty, ashe kin zo"
Aunty rabi tace "na zo Mom ɗinku ke faɗa man kuna wurin salloon, buɗe mugani " ta faɗa tana cire hular dake kan Aairah
kai masha Allah, gaskiya yayi kyau"
"na gode sosai Aunty" Aairah ta fada, Aaimah cewa tayi" to ni bari na tashi,  tun da na lura Aunty ba tani ki ke ba ta Aairah kike"
Aunty rabi tace "sorry Aaimah,  ke ma ina ta ke, mu ga naki kema" mom ce tace "to tunda abun  ƴar wariyar launin fata ce ,matso kinji ƴata naga naki harda ƙunshin" ta faɗa tana miƙama najmah hannun,   da sauri najmah ta ƙarasa wurin Mom, nan tashiga nuna mata,sallama mus'af yayi,gaba ɗaya su ka kai duban su gare shi
Mom ce tace "wai dama mus'af tare kuke?"
"eh"  yaba  Mom amsa, gai sawa su kayi har da su Aunty Rabi da baaba larai , mus'af bai wani jima ba yayi masu sallama ya wuce gida, shi ka ɗai ya tafi, a  nan Najma zata kwana.
zama su kayi nan parlor suna taya su mom aikin da suke, har suka kammala sannan suka wuce daki, wanka ko wace cikin su tayi da  sallah  magrib wacce ake kira, basu fita daga daki ba sai da suka yi har sallar isha sannan suka fice daga dakin suka nufi parlor , yanzu ma mom da Aunty Rabi suka samu a parlorn, zama suka yi sai ga abie da ya abdallah  sun shigo.

✨Lagos✨

Ammy da Fatima ne zaune a parlor bayan sun yi sallar magrib da isha suka dawo parlor  suna duba kayayya kin da suka yi shopping, fatima tace "wallahi kayan nan sunyi kyau sosai Ammy "
Ammy ta ce"ai kuwa  sunyi kyau sosai"
Fatima tace" amma Ammy yaushe yaya yace zamu tafi abuja,amma dai cikin wannan week ɗin ko"
"to sai dai Idan ya dawo in tambaye shi, dan gaskiya ni bai faɗa min yaushe zaku tafi ba, duk da munyi magana yace next week amma ban ga yana wani shiri na alamar tafiyar ba "
"ok to shikenan Ammy" nan suka shiga duba kayan suna yaba kyan su, 
Noraiz  ya shigo  bakinsa ɗauke da sallama, amsa mashi sallamar su kayi,  Ammy na ce wa "ina ka baro Yayan naka"
Amsa Noraiz yaba ma Ammy da
"tare muke dashi, yana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login