Showing 18001 words to 21000 words out of 127932 words

Chapter 7 - DOCTOR SHAZIM HAUSA NOVEL

01 Apr 2025

6692

da dangin mahaifinku" ɗan nisawa yayi sannan yace "ammy ni ba haka nake nufi ba,kwai naga zaki yi kaɗaici ne,ke kaɗai fa a gida"
katse shi ammy tayi da cewa "in dai dan ta nine karka hanata zuwa abuja, idan bata nan baga ku nan ba kai da noraiz "
"ammy mu ba zama muke ba, idan muka fita tun safe sai dare fa muke da wowa"
"to naji sai dare kuke da wowa, itama idan ta je makaranta ba sai da yamma zata dunga dawowa ba?" ta ƙarasa faɗa da sigar tambaya tana tsare shi da idanu
"ammy dan Allah kiyi haƙuri tayi karatun ta nan, itama sai ta fi jin daɗi karatun, chan haya niyar innah kawai ta ishe ta" uhmm kawai ammay tace ba tare da ta sake cewa komi ba
Ba wanda ya sake magana cikin su har suka kammala  breakfast din , shazim ne ya fara ajiye fork din da yake cin arish,hannu ya mika ya yagi tissue din dake kan dinning ya goge bakinsa sannan ya dauki robar ruwa ya sha,mikewa ya yi ya nufi sofar da ya ajiye briefcase dinsa ya na fadin "Ammy ni zan wuce" cup din tea din da ta kai baki ta janye tana fadin "a dawo lafiya , Allah ya  ba da sa'a, an jima ka dan zanje gidan baba,may be baza ka same ni ba lokacin da zaka dawo, dan zanjima kilama sai dare ma zan dawo "
"Allah ya kaimu anjmar lafiya, ina gaishe da malam,  sai na dawo" ya fada yana nufar ƙofar ficewa daga parlorn, Noraiz  yace "a dawo lafiya Yaya, Idan na ajiye ammy gidan malam zan zo wurin ka in sha Allah "
"Allah ya kawo ka  lafiya " kawai ya fada yana ficewa, parking lot ya nufa motarsa wacce yasa aka wanke masa ya nufa, bude kofar motar yayi briefcase din sa ya aje da lab coat, sannan ya zagaya driver seat ya zauna , key yayima motar ya nufi main gate , gaisawa yayi  da ma'aikatan gidan sannan ya fice daman mai gadi yariga da ya bude masa gate,eko  ya nufa yana tafiya yana sauraron karatun alqur'ani a mota...

✨HIDAYA✨

Tsaye take gefen titin anguwar su  tana jiran  abun hawa, kusan 5 minutes tana nan bata samu abun hawa ba, wata bakar motace ta shigo anguwar tasu, tunda motar ta shigo anguwar tasu take ma motar kallon kamar tasan mamalakinta, motar na ƙarasowa  kusa da ita tana rage gudu,  kallon motar kawai take sai da ta kawo dab da ita sannan aranta tace"wannan ai kamar motar dr kabir" parking motar a kayi hadi da sauke glass din motar, kyakyawan saurayine fari amma ba sosai chan ba, akallah zai yi kima nin shekara 28 zuwa 30, sanye yake da scrub suit blue color fuskar sa manne take da glass, hidaya  tace" ina kwana dr" amsa mata yayi da " lafiya lau , mi ki ke yi tsaye anan?" amsa ta bashi da "ina jiran abun hawa ne dr"
"ok to shigo ciki mu wuce "
" A'a dr ka tafi kawai zan samu abun hawa in sha Allah" hidaya ta fada,  glass din dake fuskar shi ya cire yana cewa "to fah, hidaya ko dai kina tsoron  na sayar dake ne iye " murmushi tayi hadi da cewa "A'a ba haka bane "
ajiyar zuciya ya sauke
"to inhar ba haka bane, to kishiga mu wuce " to kawai tace hadi da zagayawa ta shiga ciki, key yayima motar yana cewa "wallahi kina bani mamaki hidaya, sai kace wata ƙaramar yarinya in ki ka yi wani abun" murmushi kawai tayi masa ba tare da  tace komai ba, haka su kai ta tafiya yana janta da fira har suka iso  eko,parking lot din asibitin ya nufa yayi parking, har tasa hannu zata bude kofa ya da katar da ita yana cewa "wai hidaya tsorona ki ke ji ne, naga har wani sauri kike ki fita"
"A'a " kawai tace mashi tana duƙar da kanta ƙasa, "shikenan bakomi kina iya tafiya" ya fada, ficewa tayi daga motar shikuma ya tsaya tatara kayan sa dake back seat, tana fitowa motar shazim na parking, dr kabir ne ya fito hannun sa riƙe da  tarkacen sa yana cema hidaya su tafi,tafiya suke sun kusa kawo inda motar shazim take sai gashi ya fito,miƙa masa hannu  dr kabir yayi  suka gaisa,hidaya ma gaishe da shi tayi, da lafiya kawai ya amsa mata , wuce wa tayi tabar su shi da dr kabir tayi cikin asibitin, office din su da nurses kezama ta nufa, ba kowa ciki sai friend ɗin  ta maryam da alama wanda su ka zo duk sun fita.
"lafiya  yau ki ka yi late ? " maryam ta tambaya , ƙarasowa  inda take hidaya tayi tana cewa "ke dai bari,  banyi bacci bane jiya dawuri shiyyasa nayi late" dafa kafadar ta maryam tayi tana cewa "kingama yanke shawara yan da zaki tunkari dr da maganar koh"
"a'a gaskiya,  maryam ina jin tsoro ne, ban san ya dr zai dauki maganar tawa ba " hannun hidaya maryam taja suka zauna sannan tace " ki kwantar da hankalin ki hidaya In sha Allah alkairi ne zai biyo baya,  kinji" ajiyar zuciya hidaya ta sauke tana cewa "to Allah yasa haka maryam" da ameen maryam ta amsa mata tana cewa "tashi mu fita" ta fada tana jan hannun hidaya, fice wa su kayi suka nufi inda yan uwansu nurses suke, gaishe da junan su  suka shigayi , office din dr Shazim hidaya ta nufa tana cema maryam " sister bari naje office din dr na dawo"
"ok  sai kin dawo " maryam ta fada, office din hidaya ta nufa hadi da tura kufar ta shiga  bakinta ɗauke  da sallama.
amsa mata sallamar yayi, sannan tace "dr asa patient a layi " amsa ya bata  da" eh " har zata  fice sai kuma ta dawo sai da tayi 2_3 seconds sannan dai ta daure tace "afuwan dr dama ina so ne muyi wata mgn" ɗago kansa  yayi daga aikin da yake ya tsare ta da idanu alamar ina sauraronki,  magana  ta fara "dama dr maganar  Victoria ce" ɗaga mata hannu yayi alamar ya isa haka "wannan ya zama na ƙarshe  da zaki ƙara man maganar ta   a nan, in ba haka ba kema zaki bita , fatan kingane"
"ok sir in sha Allah bazan sake ba" ta fada tana ficewa daga    office din , direct wurin patient ta wuce,  ta shiga aikin ta ,a haka Victoria da destiny suka same ta,  wuri suka samu suka zauna kusa da ita , gaisawa su kayi sannan Victoria tace "hidaya ya maganar  mu ne" ajiyar zuciya hidaya tayi sannan tace "gaskiya kiyi haƙuri  Victoria, ko yanzu daga wurin dr na ke nayi nayi ya haƙuri  amma yaki,  dan har cewa yayi kona daina masa magnar ki ko nima ya koreni " wani kallon banza  Victoria tayi mata sannan ta ce "munafukar banza, wannan nasan duk shirinki ne, to kisani kamar yanda kika rabani da dr nima sai na rabaki dashi" mikewa hidaya tayi tana cewa "ki je kiyi duk abun da za kiyi Victoria, tun da ke baki da mutunci" faɗa ne ya kaure a tsakanin su har Victoria na neman kaima hidaya duka,  destiny na jenyeta,   su maryam ne suka zo wurin saboda hayaniyar Victoria data jawo hankalin su, nan suka shiga cewa gaskiya baki da mutunci Victoria, komawa Victoria tayi kansu tana ce masu munafukai tasan ai da hadin bakin su, ai kuwa abun yayi masu zafi nan suka shiga maida mata da martani.
hayaniyar su ce ta damesa harta na neman haddasa masa ciwan kai hakan yasa shi ajiye abun da yake yi,  landline din dake office din ya dauka, dialing numbers yayi ana picking call din yace
"ka same ni a office dina" yana gama faɗa yayi rejecting kiran bayan kamar 30 seconds sai gashi anturo kofar, wani security ne ya shigo gaishe da shazim yayi yana faɗin "dr gani"
"wai hayaniyar mi nake ji ne?" "afuwan dr bari naje na duba "ok" kawai yace masa, fita security yayi inda su Victoria su ke ya nufa nan ya same su har lokacin basu dai na fadan da suke,  hidaya sai kuka take saboda a rayuwarta ta tsani fitina,  su maryam ne ke maida ma Victoria martanin, ɗaya daga cikin nurses ɗin  mata security ya tambaya   mike faruwa amsa ta bashi "zuwana kenan na same su suna hayaniya ban san miye maƙasudun faɗan na su ba "
"to shikenan" shine kawai abun da security ya faɗa ya  komawa office ɗin  shazim  ya sanar dashi cewa "sir su nurse Victoria ne ke hayaniya, ina jin dai wani abun ne ya ha dasu"
"Mtssww"shazim  yaja tsaki  a ranshi yace "nonsense kawai dasu,zasu wani tada ma mutane hankali,sakarkaru banza "
achan kuwa waje dr kabir ne ya fito daga office ɗinsa  ya nufi in da su Victoria suke  shima hayaniyar su ce ta dame shi, yana isowa wurin dukan su su kayi shiru tsaki yaja hadi da cewa"wallahi kun bani mamaki matuƙa,ashe baku da hankali ban sani ba" ya fada hadi danuna hidaya ya na cewa "wacece nan,mi kuma akayi mata take kuka" da yake a duƙe take shiyyasa bai gane ko wacece ba, maryam  tace "nurse hidaya ce" matsowa yayi kusa da ita yana fadi "mike da munta ne " amsa maryam ta bashi da cewa "Victoria ce ke ci mata mutunci,ita kuma bata iya ramawa,shine take kuka, mukuma..." hannu ya daga ma maryam yana cewa"ya isa haka, oya tashi " yace ma hidaya,  mikewa tayi  fuskar nan duk tayi sharkaf da hawaye "wuce muje" yace,  binsa tayi a baya har office ɗinsa , toilet ya nuna mata "shiga ki wanke fuskar ki" shiga tayi ta wanke fuskarta sannan ta fito
wuri ya nuna mata kan sofa da ke cikin office din,
zama tayi tana sauke ajiyar zuciya
ita bakomai yafi bata haushi ba wai a ce daga taimako Victoria zata yi mata haka, gyaran murya dr kabir yayi haɗi da zama kan sofar yana fuskantarta "hidaya nasan wannan ba halinki ba ne, miyasa ki ke biye ma mutane irin waɗanna,  ke da ita bafa ɗaya ba ne, al'adar ku ba ɗaya ba kwata kwata ita batasan kunya ba saboda ba'a koya mata ba, amma ke duk wanda ya ganki zai yimaki kallon wacce bata san mutuncin kanta ba,please hidaya karki sake"
"in sha Allah hakan ba zata sake faruwa ba nagode"
"bakomai karki damu, tashi ki tafi ki cigaba da abun da ki ke"
"ok" ta faɗa hadi da mikewa ta fice, wurin patient ta koma  ta cigaba da turama dr su.

✨noraiz✨

Parlorn ammy ya shigo jikinsa sanye da kananu  kaya farar riga da bakin wando, yana shigowa Ammy na fitowa daga bedroom dinta sanye take da hijab har kasa
"yawwa Ammy harkin shirya kenan?" "eh" Ammy ta fada, ficewa su ka yi,  parking lot suka nufa wurin wata baƙar mota ƙirar rang rover,back seat ya bude mata tukun ya zagaya driver seat ya zauna hadi da yima motar key ya nufi gate, megadi ne ya tashi ya bude masu gate, gaishe da Ammy yayi, amsa mashi tayi cikin kulawa sannan Noraiz yayima motar key su ka fice daga gidan.
tafiya su ka yi mai ɗan nisa, a bakin gate ɗin wani gida Noraiz ya yi horn.
ƙofar dake jikin gate din gidan aka bude,wani mutum ne ya leƙo yana ganin motar Noraiz ya koma da sauri
gate din gidan  aka bude ciki Noraiz  ya danna kan hancin motar, parking lot din dake gidan Noraiz ya nufa ya yi parking, fitowa su ka yi shi da Ammy suka wuce cikin gidan
part biyu ne gidan , ɗaya daga cikin part ɗin  suka nufa, da sallama abakin su suka shiga cikin parlorn
parlorn ne mai girman gaske  wani dattijone zaune kan carpet sai wata yar tsohuwa dake kusa da shi tana mika masa magani da ruwa.
wurin su suka ƙarasa wannan yar tsohuwar ce ta dago tana amsa ma su sallamar da su kayi, haɗi da cewa "oyoyo ango saukar yaushe" noraiz na murmushi yace "jiya" yayin da  suke samun wurin zama  kan carpet,ammy tace "ina kwana ummy, ya jikin baba"
ummy tace "lafiya lau, jiki  Alhmdllh" masha Allah Ammy tace , sannan ta kalli baba tana faɗin "ina kwana   baba,  ya ƙarfin  jiki" 
"jiki Alhmdllh da sauki,
wa nake gani kamar NURADDEEN? " Baba ya tambaya.
murmushi Noraiz yayi yana faɗin "shine mlm, ya ƙarfin jiki?"
"jiki Alhmdllh nuraddeen, saukar yaushe"
"jiya" Noraiz ya bashi amsa
"masha Allah,ya karatu?"
"Alhmdllh mlm" jin jina kai malam yayi yana faɗin "masha Allah, ina wannan ƙaton gwawron yayan na ka,mai gudun aure" murmushi Noraiz yayi yana bashi amsa da yana hospital
"Masha Allah, Allah ya taimaka" ya fada, sun jima suna fira har kusan 12  sannan Noraiz yace "malam zanje wurin yaya"
"to a dawo lafiya"
"Allah yasa" Noraiz ya fada, sallama yayi ma su hadi da nufar kofar fita daga parlorn ya fice.
kallon ammy malam yayi yana faɗin" jiya Ahmad ya kira ni kan maganar shazim, sun ji shi shiru, kuma suna ta kiran shi basu samu, har mansoor sai da ya kirani shima bai samun shi a waya ko da ya kira shi"
"eh haka yace man nima da ya kirani "
"kin faɗa ma shazim ɗin?"
"eh na faɗa mashi,amma har yanzu amsa ɗaya ce,bashi da wacce yake so" ɗan nisawa malam yayi sannan yace "na lura so yake mu cire hannun mu daga maganar, mu ƙyale shi da su Ahmad ɗin, su yanke mashi duk hukuncin da suka ga dama"
"haka nima nace mashi, zamu cire hannun mu a lamarin suyi duk abun da suka ga dama"
ummy tace "ba haka za'ayi ba malam, ina ga a ƙara mashi lokaci ko da ba mai tsayi ba"
malam yace "lokaci na nawa za'a bashi zainab, tun yaushe ake bashi lokaci"
"duk da haka dai, a ƙara mashi ko da wata ɗaya ne "malam yace "to shikenan"

Noraiz yana shiga cikin eko parking yayi a parking lot, fitowa yayi ya nufi cikin hospital, da yake office din shazim chansama yake hakan yasa shi hawan elevator ta sauke shi a floor ɗin da office ɗin ya ke.
A bakin office din ya tsaya,nocking yayi daga ciki aka bashi iznin shiga
ƙofar ya tura ya shiga, shazim ya samu zaune yana aiki cikin laptop
sallamar da yayi shazim ya amsa mashi, wuri ya samu cikin ɗaya daga kujerun office din ya zauna
"ya aiki yaya?"
"Alhmdllh" kawai shazim yace yana yana tambayar  jikin malam
"Alhmdllh yaya,ya ji sauki" dr kabir ne ya shigo office din yana ganin Noraiz yace
"saukar yaushe Noraiz?"
"jiya Yaya, ya Aiki " Noraiz ya fada
"Alhmdllh Noraiz, ya school "
"school Alhmdllh "
"masha Allah" fira suka shiga yi ta yaushe gamo shida dr kabir shazim na sauraron su yana aikin gaban sa,  kiran sallar zuhur ne ya katse masu firar  su ka fice zuwa masallaci domin yin sallah
daga cana abnoor  shazim da Noraiz ɗin su ka wuce.

✨ Aairah ✨

dawowar su kenan daga school dan ko uniform basu cire ba suka haye bed saboda ba ƙaramin  gajiya su kayi ba ' dan Aairah da wani irin zazzabi ta dawo 

Mom ce ta shigo ɗakin tana cewa "lafiya kuke, ko uniform ba ku cireba kun kama bacci"
"wallahi  mom mun gaji ne sosai shiyyasa, kuma ma Aairah bata jin daɗi,zazzabi ne a jikin ta"
"wani aiki ku kayi ne a  makarantar" mom ta fada yayin da take ƙarasawa  kan bed,  hannunta ta ɗaura  saman wuyan Aairah "ya salam" mom ta fada saboda jin zafin dake fita daga jikin Aairah "mi ke damunki?"
"zazzabi ne da ciwan kai"
"ok yaka mata ki tashi ki cire uniform ki  watsa ruwa, bari naje na dauko maki magani kafin yayan ku ya dawo" tashi tayi zaune mom tace ma Aaimah ta shiga bathroom ta hada mata ruwan wanka, to tace hadi da nufar toilet, ficewa mom tayi daga daki 
Uniform ɗin jikinta ta cire  ta daura towel,  Aaimah ta fito tana cewa sister kishiga ga ruwan chan " to nagode  sister" ta fada tana nufar toilet ɗin
kayan jikinta ita ma ta cire Aairah na fitowa ta shiga
bed Aairah tahau tana jan blanket,wani irin sanyi take ji saboda wankan da tayi.
Mom ce ta shigo hannun ta ɗauke  da tere wanda ta haɗa ma Aairah abinci 
"wai kwanciyar kika sake?" wurin ta mom ta nufo,  table ɗin  dake ɗakin  ta jawo ta daura tray da ta shigo dashi,  hawa tayi kan gadon tana fadin "tashi ki ci abinci ga maganinan"
tashi tayi zaune "baki sa kaya ba kenan?" mom ta fada tana nufar wardrobe din su, riga mara nauyi mom ta dauko mata
"tashi kisa" mom ta fada yayin da take mika mata rigar,
amsa tayi tana tashi ta sanya rigar sannan ta dawo kan gadon ta zauna abincin da  ta haɗa mata tamika mata
tana gama ci mom ta bata magani tasha sannan ta koma ta kwanta blanket Mom taja mata
ta haɗa tiren da Aairah taci abinci ta fice da shi yayin da take cema Aaimah inta gama shiri ta fito taci abinci ita ma 
shaf shaf Aaimah  ta shirya sannan ta dawo kusa da Aairah
"sister ya jikin naki"
"da sauki " Aairah ta fada
"ok Allah ya kara sauki, bari naje naci abinci na dawo "
gyada mata kai Aairah tayi alamar sai kin dawo
ficewa Aaimah tayi daga bedroom din , parlor ta nufa Mom ta samu kan dinning ita da abie 
ƙarasawa tayi wurin su tana cewa "ina wuni abie"
"lafiya lau,yanzu Mom din ku ke fada man Aairah ba lafiya,  ya jikin nata?"
"da sauki abie "
"to Allah ya bata lafiya, Idan Abdallah  ya dawo sai ya duba ta,in ma taka ma ayi mata allura, koh mi kenan dai " abie  ya fada, Aaimah a jiye spoon din dake hannun tayi tana dariya hadi da fadin "kace yau akwai daru,Aairah za a yima allura?, tashin hankali kenan"
"ka jita sai kace ba jirgi daya ya kwasu ku ba,  kema son  allurar kike ne?" Mom tafa hadi da mangare mata kai, sosa inda Mom ta mangareta tayi tana turo baki da fadin "Allah gara ni da Aairah Mom" 
"Bawani nan" Mom ta fada,suna gama cin abincin abee ya mike yana cewa "bari naje na duba jikin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login