Showing 84001 words to 87000 words out of 127932 words

Chapter 29 - DOCTOR SHAZIM HAUSA NOVEL

01 Apr 2025

6720

ina nan ai ban taɓa ganin ka ba "
"In sha Allah abie ina nan zuwa , zan maka zuwan baza ta "
"to Allah yasa, ya jikin fatima"
"da sauƙi abie "
"to Allah ya ƙara sauƙi, ga mom ɗin ku nan za ku gaisa " abie ya faɗa, to shazim yace , muryar mom yaji tana cewa "shazim ya gida "
"lafiya lau mom,ina kwana "
"lafiya lau, ya su ammyn ku "
"lafiya lau su ke "
"Ashe fatima ba lafiya,to Allah ya bata lafiya "
"Ameen ya Allah "
"Ammyn ku na kusa "
"A'a tana part ɗin ta "
"to shikenan ka gaishe man da ita dan Allah "
"in sha Allah za taji "
"yawwa to nagode sai anjima " mom ta faɗa haɗi da yin rejecting,cire wayar yayi daga kunnan shi haɗi da miƙa ma Abdallah , amsa Abdallah yayi.
bedroom shazim ya shiga, kamar yanda yace ma Ammy wanka yayi jallabiya ya sa ya fice zuwa part Ammyn zaune take kamar ɗazu, sai dai yanzu ita kaɗai ce noraiz na part ɗin shi sa'ada kuma na ɗakin fatima,  zama yayi kan sofar da kusa da wacce Ammy ke zaune
"Ammy " ya kira sunan ta  a hankali , juyowa tayi tana kallon shi, magana ya soma cikin natsuwa
"Ammy kiyi haƙuri da abun da zan faɗa maki "
"ina sauraron ka shazim, haƙuri kuma ya zama dole tun da bazan goge abun da ya riga ya faru ba " ajiyar zuciya ya ɗan sauke, duk abun da ya faru a Abuja sai da ya sanar da ita har da irin matakin da ya ɗauka a kan luqman sai da ya faɗa mata, Ammy taci kuka kuma taji haushin hukuncin da su uncle Ahmad su ka yanke ma shazim dan kwata kwata bata son feenah , saboda rashin tarbiyar ta da rashin kamun kanta taso ace da kairiyya suka haɗa shi bawai da feenah ba, sannan ranta yayi matuƙar baci da luqman ta so ace shazim yayi mashi hukunci fiye da wanda yayi mashi, ta san duk abun da ya faru a kwai sa hannun innah da gwaggo Uwani
na sara miyasa innah bata ƙaunata da su shazim wai mi nayi mata ne a rayuwa, duk abun sadiq yayi mata amma da wannan zata saka mashi, ya Allah ka kawo man ƙarahen wannan al'amarin Ammy ta faɗa a zuciyar ta
kallon shazim tayi tace " yanzu yaushe su ka ce sun tsaida ranar bikin "
"ni ban san yaushe za su tsaida ba, bana ma so na san lokacin "
"shi luqman da yace yana son fatimar sun amsa cewa zasu bashi "
"a lokacin basu amsa ba, amma na san zasu amsa ne,amma ki kwantar da hankalin ki Ammy babu mai ma fatima auren dole da wannan yaron in dai ina raye"
"shazim bana son ka nuna ba su isa da kai ba ko dan Ibrahim ya kula da rayuwar ku "
"Ammy ni bazan nuna masu basu isa da ni  ba, amma bazan bari su zalinci fatima ba"
"shikenan, amma auren naka da feenah fa, na so ace da kairiyya su ka haɗa ka  ba wai feenah "
"dan Allah ma Ammy ki bar wannan zancen, ni bazan auri wannan yarinyar ba ko kuwa mi zasu yi"
"shikenan, fatima yan zu miye yake damun ta "
"jikin ta da suƙi, kawai dai alurar da nake mata ce ke sata bacci saboda firgitar da take yi ne, amma in sha Allah nan da zuwa anjima ma zata iya farkawa "
"Allah ya bata lafiya, amma gaskiya luqman bai kayuta man ba, mi yasa zai yi man haka a rayuwa"
"Ammy kar ki damu da batun luqman yanzu abun da yaso ya aikata Allah bai bashi sa'a ba ta dalilin ciwan fatimar daya tashi sai yaji tsoro bai mata komai ba,  dan haka ki kwantar da hankalin ki kawai"

_Abun da ya faru, lokacin da fatima ta fice daga parlorn da suke taro,luqman  shi kuma haushin ta nuna bata son shi ne yasa shi fita ya bi bayanta ya tare ta yana mata masifa ita harta isa tace bata son shi daga zai taimaka mata shine zatace bata sonshi, angaya mata shima son ta yake, kawai dan an haɗa shi da Allah ne akan yace yana son ta ne yasa yace yana son ta,maganar daya faɗa ce ta wai an haɗa shi da Allah yace yana son tace ta ɓata mata rai ta kai ga zazzaga mashi masifa son ranta hartana ce mashi ɗan shaye shaye, shikuma haushin rashin kunyar da tayi mashi ne yasa shi cewa yau sai ya nuna mata cewa shi cikaken ɗan iska ne,  shine ya saɓeta kan kafaɗa, tana kuka ta kai mashi duka a baya har cizon shi tayi amma ya ƙi sauke ta har sai da ya isa ɗakin shi sannan yayi wurigi da ita kan gadon shi haɗi da maida ƙofa ya rufe ba tausayi ya afaka mata,kuka ta shiga yi tana roƙwanshi daya ƙyale ta amma sam sam bai saurare ta ba,dan ma kar ta sa wani ya jisu ne yasa shi rufe mata baki da nashi,sumbatar ta ya shiga yi ba arziƙi tun tana kuka har ta kai ga fara kai mashi duka ta ko ina har da cizo da ya kushi, wani ya kushi  ne da takai mashi a gadon bayan shi ne yasa shi haɗa ta da bango har kanta ya fashe ta kifa ƙasa azabar zafin da taji ne yasa ta fasa ƙara wanda hakan ya jawo hankalin dady daya shigo part ɗaukar key ɗin mota saboda suma da feenah tayi zai kaita asibiti, kasancewar ɗakin luqman ɗin yana kusa da na shi shiyyasa yaji ihun da fatima ta tayi, har ya shiga ɗakin ya same ta yashe a ƙasa shikuma luqman tsaye yana zare ido duk ya tsorata, anan sai da dady ya wanke shi da mari kafin yasa shi su ka kama fatimar suka shiga part ɗin shi da ita duk yayi hakan ne dan kar shazim ya san abun da ya faru yayi tunanin suma kawai tayi na tsoro bai san lalurar ta ce ta tashi ba, sai da suka ya yayyafa mata ruwa ta ƙi tashi sannan hankalin dady da na luqman ɗin kanshi ya ƙara tashi
momy kuma motsin su ne yasa nufar part ɗin dadyn amma sai ya hanata ganin fatimar ba irin tambayar da bata yi mashi ba dan taji ihun fatima amma dady yace ba komai, da sa'ada ta faɗa mata ba'aga fatima bane yasa ta zargin ko dai fatima ce_

"shikenan shazim, amma taya zan yarda bai keta man haddin yarinya ba"
"nasa matar uncle ɗin Abdallah tayi mata awo kuma sakamakon ya nuna cewa ba abun da ya same ta "
"to shikenan Allah ya bata lafiya,  kaga ma ko gaisawa ba muyi da Abdallah ba nagama kamar har da Abdulmajeed ku ka shi go "
"Eh tare muke da shi "
"to bari nasa sa'ada ta kawo maku breakfast naji kace ba kuyi break ba kuka taho "
"Eh Ammy " shazim ya faɗa haɗi da tashi ya nufi part ɗin shi wurin su Abdallah.

Ɗakin fatima Ammy ta nufa, zaune ta samu sa'ada bakin gado ta zuba uban tagumi
Sallama Ammy tayi sa'ada bata amsa ba ganin kamar hankalin ta baya tare da jikin ta ne ya sata shiga ciki  kusa da sa'ada ta ƙarasa, dafa kafaɗar ta tayi tace " sa'ada lafiya kika zuba uban tagumi ina sallama bakya ji "
" ba komai Ammy "
"ya za kice ba komai bayan na ganki cikin damuwa haka, ko dai duk a kan fatima ne " ɗaga mata kai sa'ada tayi alamar eh
"ki kwantar da hankalin ki za ta samu sauƙi in sha Allah "
" to Ammy "
"yawwa, zo ki je part ɗin shazim ki kai masu breakfast,ke ma kizo kiyi "
"to Ammy ta faɗa haɗi da miƙewa su ka fita zuwa dinning, jera mata kayan breakfast ɗin Ammy tayi a tray, trayn ɗin bai ɗauke kayan duka ba hakan yasa Ammy cewa taje ta dawo sai ta kai masu sauran da to ta amsa har ta kama hanya zata nufi sama sai ga noraiz ya sauko amsar trayn yayi yace taje ta ɗauko sauran dan yaji lokacin da Ammy ke cewa taje ta dawo ta ɗauki sairan, " to ya noraiz " ta faɗa haɗi da komawa ta ɗauko sauran ta bi bayan shi, a bakin ƙofar part ɗin suka tsaya.

Sa'ada tayi nocking, shazim ne yazo ya buɗe masu, amsar trayn da ke hannun sa'ada yayi noraiz kuma ya shiga da wanda ke hannun sa, juyawa sa'ada tayi ta koma parlorn Ammy
"yawwa har kun kai masu "
"Eh "
"to kema jeki kiyi naki breakfast ɗin" da to ta amsa haɗi da nufar dinning ta zauna ,noraiz ma da ya shigo parlorn  dinning ɗin ya nufa  samun wuri yayi ya zauna , sa'ada tayi serving ɗin shi
Ammy kuma ɗakin ta ta nufa ta kira malam da ummy ta sanar da su da wowar su shazim da kuma rashin lafiyar fatima, malam ranshi yayi matuƙar ɓaci ya kuma ce wallahi babu wanda zai Aura ma  fatima luqman, idan da yayi shiru innah na abun da ta gadama akan su yanzu bazai yi shiru ba sai dai duk abun da zai faru ya faru.
"in sha Allah ina nan zuwa anjima na duba jikin fatimar "
"ai baba da kun barshi, jikin nata da sauƙi "
"A'a, sai na zo "
"to shikenan Allah ya kawo ku lafiya " da Ameen malam ya amsa,  rejecting kiran yayi.

wanda shazim ya kira a waya ne yazo, magungunan ne ya kawo mashi wanda zai cigaba da ba fatima.

sai bayan sallar asr majeed ya tafi gida, akan zai dawo da daddare ya sake duba jikin fatimar,Abdallah kuwa kamar ya shaƙe majeed haka yake ji, shima majeed ɗin haushin Abdallah yake ji dan gani yake duk wannan abun da yake yana yi ne saboda kishi, ya lura son fatimar yake
ko wannan su kishi ne ke ɗawai niya da shi.

Kamar yanda malam yace da daddare su ka zo shi da ummy,  majeed  ya dawo shi da mamar shi daya faɗa mata fatimar bata da lafiya shi ne tace zata zo ta gaishe da ita, sun daɗe a gidan daga baya su ka tafi, su malam kuma shazim cewa yayi dan Allah su kwana nan,
"A'a aboki gida zan koma, ai nace sai ranar da ka zama babban mutum tukun zan dawo gidan nan "
"dan Allah dai malam  iya yau fa "
"ahab sai dai kayi kuma, komai dare sai na tafi gida fatimar dai ta farka  " ba yanda bai yi da malam ba amma yace a'a bazai kwana ba ba dan ya so ba ya haƙura, tun suna sa rana farkawar fatima har suka fara fdda rai malam ma har ya ce ummy ta zo su koma gida, Ammy ma ta so ace sun kwana Amma yace A'a gobe dai zasu dawo idan ta farka, rakiya su kayi masu har parking lot idan drivern malam yake sai da suka ga tafiyar su tukun suka koma ciki.
kowa shirin kwanciya yayi ya nufi ɗakin shi, Ammy ta so ta kwana medical room ɗin wurin fatima gudun kar ta farka cikin dare amma shazim yace ta bari shi zai kwana ɗaki ita ta tafi ta kwanta kawai, tafiya tayi amma gaba ɗaya hankalin ta na kan fatima ko da ta tafi ɗakin ta bata kwanta ba alwala tayi ta shiga nafilfilo tana roƙwan Allah ya fatima lafiya, sa'ada kuma a ɗakin fatima ta kwana.
Shazim bedroom ɗin shi ya shiga yayi wanka ya canza kayan da ke jikin shi zuwa na bacci parlor ya dawo wurin Abdallah dake zaune yana latsa wayar shi shima sanye yake da pajamas, kallon shi shazim yayi yace " ka shiga ka kwanta ni zan kwana wurin fatima dan ina kyautata zaton zata iya farkawa a kowane lokaci "
"bana jin bacci, kai idan kana ji zaka iya kwanciya ni sai na zauna na jira ta farka " murmushi shazim yayi dama ya san in dai yace haka to Abdallah bazai kwanta ba
"ko ina jin bacci dole na haƙura"
"kai kana ma ji ke nan "
"na san kai ma kana ji sai dai ka ƙi kwanciya "
"to ina ji bazan kwanta ba"
"to ai shikenan " shazim ya faɗa haɗi da miƙewa ya ɗauki laptop ɗin shi, tashi Abdallah yayi ya bi bayan shi, medical room ɗin su ka nufa kan sofa suka zauna, shazim na aiki a laptop yayin da Abdallah ke aikin latsar waya...

Episode  46_47_

suna ɗan taɓa fira jefi jefi, har shazim ya gama abun da yake a laptop fatima bata farka ba, wajen Asuba ta fara mutsu mutsun farkawa, da sauri su ka ƙarasa wurin ta, sai kiran sunan Ammy take da shazim,sai ƙoƙarin tashe take mai da ta yayi ya kwantar "ya shazim ina Ammy " fatima ta faɗa
" Ammy tana ɗaki bacci take, ya jikin naki "
"ya shazim ina nake "
"kina gida ya jikin "
"ya shazim ina ta kiran ka amma baka zo ba "
"yanzu ai  gani a kusa da ke "
"ya noor ma da Ammy duk na kira su amma basu amsa man ba, ya luqman so yayi ya kashe ni ya shazim " ta faɗa hawaye na bin idanuwan ta, sosai ran Abdallah  ya ƙara ɓaci da abun da fatima ta faɗa
"kiyi haƙuri kinji, bazan sake bari wani abu ya faru dake ba in sha Allah, ki kwantar da hankalin ki "
"dan Allah ya shazim kar ka bari su Aura man shi wallahi bana son shi "
"bazan taɓa bari su aura maki shi ba karki damu "
"yaya ina son ganin Ammy "
"Ammy bacci ta ke fatima, dare ne yanzu ki bari sai da safe za tazo kinji "
Abdallah na gefe ya ƙura mata ido ji yake kamar ya mayar da ciwan a jikin shi tsabar yan da yake jinta a cikin jikin shi
"zaki sha ruwa ne " shazim ya faɗa ganin tana miƙa hannu alamar wani abun zata ɗauka, gyaɗa mashi kai tayi
" Eh ya shazim "  hannun yasa ya ɗauko ruwan da ke kan table ɗin da magungunan ta ke kai cire marfin robar yayi da kanshi ya bata a baki, bata wani sha sosai ba ta kauda kai, ajiye robar shazim yayi yana cemata " ki koma ki kwanta " da to ta amsa haɗi da komawa ta kwanta drip ɗin da ke jikin ta ya cire mata
  "zaki sha tea ko " ya tambaye ta, ɗaga mashi kai tayi alamar eh
"Ok bari na kawo maki sai kisha maganin ki daga nan " ya faɗa haɗi da tashi ya bar gaban gadon kallon Abdallah dake tsaye ya zuba ma fatima ido kamar ya cinye ta yayi " lafiya dai ko?" ya tambayi Abdallah haɗi da tsare shi da idanu, kawata kawata hankalin Abdallah na kan fatima bai ma san shazim na mashi magana ba, har sai da shazim ya ɗan taɓa shi tukun ya dawo cikin hankalin shi, zuba mashi ido yayi yana kallon shi
"malam lafiya ka wani tsare ni da idanu " Abdallah ya faɗa yana wani shana mur
"kai zan tamabaya ai wannan " shazim ya faɗa yana zuba mashi harara, jin muryar  Abdallah ne yasa fatima juyowa da sauri ta kalli inda suke tsaye shi da shazim
"Ya dr " fatima ta kira sunan shi cikin muryar marasa lafiya, matsawa yayi kusa da ita yana faɗin "na'am fatima, ya jikin na ki" hawaye ne su ka taru a  idanuwan ta tace "ya dr, yaushe ka zo "
"tare muka zo da ke, ya jikin " ya faɗa haɗi da neman wuri bakin gadon ya zauna, fita shazim yayi zuwa part ɗin shi .

hannun ta Abdallah ya kamo  yana faɗin  "fatima ina tambayar jikin ki kinyi shiru "
"ya dr da sauƙi "
"Allah ya ƙara sauƙi "
"Ameen" shazim ne ya shigo hannun shi ɗauke da cup ɗin tea sai turiri yake,kusa da gadon ya matso, amsar cup ɗin Abdallah yayi yana faɗin
"tashi ki zauna kisha tea ɗin " yunƙurin tashi tayi, aje cup  ɗin yayi  kan table domin ya tai maka mata ta tashi  tun kafin ya ajiye shazim ya kamata ya tayar da ita zaune,
" thanks" Abdallah yace, harara shazim ya zuba mashi murmushi kawai Abdallah yayi   da kanshi ya shiga bata tea shazim kuma na duba mata magungunan da ya kamata ta sha, da ta kammala sha amsar magungunan Abdallah yayi ya miƙa mata da kanshi tasha, matsowa shazim yayi da allura a hannun shi yana faɗin " to malam matsa " juyowa Abdallah yayi yana kallon shazim dake tsaye hannun shi riƙe da allura,
"ka matsa nace bawai ka kalleni ba "
matsawa Abdallah yayi yana faɗin
"ka dai yi a hankali dan nasan halinka, ban da mugunta"
"ka san Allah zanyi maka ita idan baka yiman shiru ba ɗan rainin wayau kawai " shazim ya faɗa yana nuna ma Abdallah allurar da ke hannun sa
"zaka iya" Abdallah ya faɗa haɗi da nufar kan sofa ya zauna, fatima dai sai binsu take da idanu abun ba ƙaramin burgeta yake ba,  matsowa shazim yayi kusa da ita yana faɗin "miƙo man hannun ki " hannun rigar da ke jikin ta taja haɗi da miƙa mashi hannun, a damtsen hannun ta yayi mata alurar yana tsirawa  ta rintse  ido da sauri Abdallah yace "wai Allah, dan Allah kayi mata a sannu "
"ka takura man fah, ai da zuwa kayi ka amsa kayi mata da kanka" shazim ya faɗa
"bana iya yi mata allura ai " tsaki shazim yaja
" aikin banza da na wofi "
" kai kaga aikin banza " fatima sai murmushi take dan ba kaɗan su ke sata nisha ɗi ba, lura da hakan ne ma yasa shazim biye ma Abdallah har sai da wani baccin ya sake ɗaukar ta tukun su ka bar ɗakin dan lokacin sallar asuba yayi, alwala su kayi a part ɗin shazim su ka nufi masallaci tare da noraiz su ka tafi, lokacin da su ka dawo Ammy da sa'ada  su ka samu a medical room ɗin tare da fatima da ta sake farkawa, gaishe da Ammy su kayi haɗi da zama

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login