Showing 6001 words to 9000 words out of 127932 words

Chapter 3 - DOCTOR SHAZIM HAUSA NOVEL

01 Apr 2025

6687

"this should be the last day da zaki Ƙara zuwa office ɗina, I hope you understand"
“ a fuwan sir,kayi mata haƙuri  bazata ƙara ba" hidaya ta faɗa  gaban ta na faɗuwa tsoron kar itama ya koreta
"nagama magana get out'
zubewa Victoria tayi akan gwiwowinta tana ci gaba da bashi haƙuri  harda kuka
“I said get out from my office" ya faɗa  da tsawa yana nuna mata hanyar fita,  fita tayi tana kuka kamar ranta zai fita "kema zaki iya tafiya" Ok sir hidaya ta faɗa  fita  itama tayi wajen office ɗin  ta samu Victoria da destiny suna ganin ta suka nufe ta rokonta suka shigayi a kan ta taya victoria ba ma dr haƙuri  " shikenan in sha Allah zan taya ta kar ku damu" hidaya ta faɗa tana sharema Victoria hawayen dake fuskarta tana cigaba da kwantar mata da hankali godiya su kayi mata sannan su ka koma office ɗin  da suke zama ita kuma ta wuce wurin patient domin tura ma dr su .
haka ya cigaba da ganin patient shi kuma wannan dattijon ruwan da aka sa mashi  na ƙarewa  yasa driver ya mai dashi ABNOOR aka bashi gado ,  bashi ne ya bar EKO ba sai wurin 12:30 sannan ya wuce ABNOOR nan ma yaga patient dayawa saboda yafi jimawa a nan a kan eko ,  abnoor  hospital ɗin  sane halak malak Ita kuma eko  aiki yake a chan,  sau biyu   yake zuwa eko  a sati idan yana lagos  saboda yana visiting wasu Hospital ɗin  ,  kuma in yaje 2 to 3 hours yake yi yaje abnoor    ,  amma  standard in da yafi zama abnoor  ne saboda chan har ranar Saturday yana zuwa in yana lagos  ,sai  wurin 6:00 ya tashi daga aiki dan har an fara kiraye kirayen sallar magrib masallacin hospital ɗin  ya nufa domin gabatar da sallah sai bayan angama  tukkun yanu fi gida,

horn yayi a bakin wani katafaren gida naji da faɗa  dake Victorian Ice land , gida ne har gida wanda daga gani ba sai an faɗa maka ba kasan cewa an narkar da dukiya wajen ginasa, me gadi ne ya buɗe masa gate, ciki ya shiga   ya nufi parking space da ke chan cikin gidan,ɗakin mai gadine farko daka shigo gidan sai boys quarters daga chan gaba sai kayi ƴar tafiya sannan zaka iso part ɗin  masu gidan sai parking space dake gefe sai wani katon garden dake bayan part ɗin  masu gidan,ride's ne gasunan kala kala a kallah zasu kai 6 a parking space ɗin , parking  yayi, cikin gidan ya nufa,tura ƙofar shiga part ɗin  yayi bakinsa ɗauke da sallama,parlor ne me kyan gaske komai na cikin sa ya kasan ce golden and white color ne royal sofas ne masu kyan gaske set biyu sai wani ƙaton dining table mai chairs guda 10 , sai wasu bedroom guda 3 dake hannun dama sai kitchen da store atare, wani corridor ya nufa inda yana shiga nan ma wani madaidaicin parlorn me dauke da sofa a set 1 komai na cikin sa golden color ne sai dining mai dauke da chairs guda 5 sai two bedroom, daya daga cikin su ya nufa bakinsa ɗauke  da sallama, wata kyakyawar mace ce zaune a kan sallaya itama farace sosai suna Kama da dr  banbanchi Ita mace ce shikuma namiji zata yi kimanin shekara 50  , sanye take da hijab hannun ta reke da chasbaha tana ja , da alama sallah  ta gama, sallamar da yayi ta amsa mashi yayin da yake ƙarasa wa inda take zaune,wuri ya nema ya zauna  "an wuni lafiya ammy,  ya gida"ya faɗa ,  amsa mashi tayi da
"lafiya qlu Alhmdllh,ya aiki, ya  fama da patient kuma??" "alhmdllh ammy"
"Masha Allah" ta faɗa  haɗi  da cewa "ka tashi ka shiga ciki domin kasamu ka huta zansa fatima ta kawo maka dinner ɗinka" shi dama ba ma'a bocin cin abinci a dinning bane
"to shikenan ammy bari na wuce ciki" fito wa yayi daga bedroom ɗin  ya nufi stairs dake parlor wani  part ya shiga wanda da alama nasa ne tura ƙofar  yayi haɗi  dayin sallama, ya kutsa kai ciki parlor  ne shima madaidaici me kyan gaske komai na cikin sa ash and black ne ,bedroom ya nufa wanda shima bedroom ɗin  kayan cikin sa ash ne hatta da furnitures ɗin  dake ciki ash ne ɗan corridor ya nufa clothset ne sai gefe  laundry basket,  kayan jikin sa ya shiga ragewa ya koma daga shi sai boxer  bathroom yanu fa domin watsa ruwa after 15 minutes ya fito jikin sa sanye da bathrobe, wurin clothes set ɗinsa ya nufa jallabiya ya saka ajikin sa bathroom ɗin ya koma domin ɗauro  alwallah saboda time ɗin  sallah isha yayi
masallachin gidan ya nufa dan gabatarda sallah anagama sallah part ɗin  sa ya koma a parlor  ya zauna kan sofa  bai jima da zama ba yaji ana nocking  tambaya  yayi waye ne " fatima ce Yaya"
"ok shigo" ya faɗa turo ƙofar  tayi ta shigo bakinta ɗauke  da sallama kyakyawar matashiyar budurwace da aƙalla zata kai kima nin shekaru 18 zuwa 19 a duniya fara ce itama tana kamada ammyn su amma ba sosai ba dr dai shine ke kama da Ita sosai
"ina wuni Yaya, andawo lafiya?"
"lafiya lau"
"dama ammy ce tace na kawo maka dinner ɗin  ka"
"ok,zaki iya ajiyewa kan table" gyaɗa kai tayi tana ajiye mashi,ficewa tayi daga parlorn, jawo table din yayi , serving ɗin  kanshi yashiga yi, yana kammala cin abincin bedroom ɗinsa  ya koma laptop dinsa ya jawo dake kan bedside  aiki yashiga yi.

KATSINA.

Su Aaimah ne zaune a falon mom suna kallo, sanye suke da pajamas sky blue,   mom ce ta fito daga bedroom ɗin  ta,  ita ma sanye take da pajamas purple color,  waya ce kare a kunnanta da alama waya take, wuri tasamu kan sofa ta zauna tana cigaba da wayar 
"mom abie  ne Aaimah ta faɗa  yayin da take matsowa kusa da mom" daga mata kai mom tayi alamar eh
"mom dan Allah kice muna gaishe shi munkira shi bai ɗauka  ba"
"to kaji Wai twins ɗinka  nagaishe da kai, wai sun kiraka baka ɗauka ba" mom ta faɗa,mika ma Aaimah wayar tayi da a lama cewa yayi a basu wayar, amsa tayi tana faɗin " inawuni abie  ya Abuja, ya kuma aiki?" on the other hand abie  yace" lafiya lau Alhmdllh, ya gida ya kuma school"
"Alhmdllh abie"  ta bashi amsa
"abie  ko ka ce ina nake Aaimah ka ɗai  kasani" Aairah ta faɗa wacce ƙarasowarta kenan "afuwan yanzu zance kina ina sai kuma gaki,ya gida ya school?"
"Alhmdllh abie,  yaushe zaka dawo"
"jibi in sha Allah zan dawo"
"to Allah ya kaimu abie" ameen ya faɗa   sun jima suna waya  sannan suka yi sallam,  bedroom ɗin su  suka nufa domin bacci dan mom ta daɗe dashige wa nata bedroom ɗin.
Ep 5_6

FRIDAY.

sauko wa yake daga stairs jikin sa sanye da baƙaƙen suit hannun sa riƙe da briefcase, ammy ce zaune kan sofa ƙaraso wa yayi kusa da ita
"Ina kwana Ammy, ina fatan kin tashi lafiya?" ya faɗa yayin da yake samu wuri kusa da Ammy ya zauna
"lafiya lau Shazim har ka fito?"
"eh ammy ya bata amsa
"ga breakfast din ka nan kan dinning"
"to ammy,kin kuwa yi waya da NORAIZ?"
( kaninsa mai bimasa yayan fatima da yake baya nan yana kasar portland yana masters) ya fada yayin da yake nufar dinning
"eh, naji yace yana nan zuwa ranar sunday ( lahadi ) ammy ta faɗa " eh ammy haka ya faɗa man jiya"
"to Allah ya kaimu lafiya,Jiya uncle ɗin ku ya kirani, yace kai ka ɗai suke jira"
shiru yayi baice komai ba sai da ammy ta sake cewa "da kai fa nake magana, ni ban san mikake nufi ba , da anyi magana sai kayi shiru, tun yaushe ake abu ɗaya sai yawo ka ke ma mutane da hankali"
"kiyi haƙuri ammy, wallahi ban gama abun da nake ba, kuma ni fa bani da wata wacce zance ina so, nafi son su bar na samu wacce nake so"
"to bari kaji na faɗa maka ni ba ruwana daga yanzu bazan sake shiga maganar ba, duk hukuncin da suka yanke akan ka ba bu ruwana"
shazim yace "dan Allah ammy kar kice haka, idan kika zare hannunki innah zata iya zuga su su yanke man hukuncin da duk su kaga dama"
"to idan har baka son haka ta faru to dole sai ka nema ma kanka mafita"
"in sha Allah ammy"
"to Allah ya yarda"
"ameen ammy "

fatima  ce ta fito daga bedroom dinta dake kusa da na Ammy, sanye take da uniform , dinning ta nufo Ita ma domin breakfast
"Ina kwana Yaya, an tashi lafiya"
"lafiya lau" ya bata Amsa, yana gama breakfast ya mike yana daukar briefcase ɗin shi "Ammy ni zan wuce, to a dawo lafiya,Allah ya bada sa'a" "ameen Ammy" fita yayi zuwa parking lot, gaisawa ya tsaya yi da masu aikin gidan tun daga kan maibama flower ruwa Har izuwa kan maigadi sannan ya fice daga gidan, ABNOOR ya nufa domin yau baya zuwa EKO.

ABDULƘADIR   ABUBAKAR NURADDEEN PRIVATE  HOSPITAL ( ABNOOR ).

Direct office din sa ya nufa briefcase din sa ya aje akan table, zama yayi haɗi da buɗe laptop din sa, aiki yafara kafin time din daya ke duba patient yayi.
sallama a kayi haɗi da turo kofar,wani matashin saurayi ne wanda zasu yi sa'anni da shazim ɗin.
Amsa mashi sallama yayi, shigowa yayi daga ciki, hannu ya miƙa ma shazim suka yi musabaha , sannan ya zauna kan  kujerar dake gaban table din
"shazim  amma yanzu ka shigo, dan na zo baka nan?"
"eh shigowata kenan nakama aiki"
"ai ku manya ne agogo sarkin aiki"
"haka dai ka ke gani majeed,  karfin haline kawai"
"wlh kuwa ai kana ƙoƙari"
"to ya za'ayi,dole a nema"
"hakane dama maganar kayan da suka kusa ƙarewa ne"
"kai ai kuwa gara daka tuna man,dan har na manta, zanyi magana da su yau in sha Allah"
"to shikenan,ni bari nakoma office"
"to shikenan nima yanzu zanje duba patient in sha Allah, saboda da time din sallah nayi zan tashi sai kuma gobe Idan Allah ya kaimu"
"ameen" majeed  ya fada barin office din yayi, shi ma shazim bai jima ba ya fita, dakin marasa lafiya ya nufa, sai 12:10 sannan ya dawo office, yana shiga ba wani jimawa yayi ba ya haɗa kan kayansa ya fito direct gida ya nufa bedroom din ammy ya fara zuwa gaisawa kawai su kayi ya nufi part din sa. bedroom din sa ya nufa kayan jikin sa ya shiga ragewa ya nufi bathroom after 10 minutes ya fito kugunsa daure da towel dressin mirror ya nufa mai ya shafa mai dankaran kamshi, comb yasa ya shiga combing din kansa sannan ya shafesa da man aloe da hair spray, clothes set ɗinsa ya nufa shaf shaf ya shirya cikin wata shadda ƴar ubansu milk color ba karamin
kyau yayi ba,hula ya dauko ya daura brown color, feshe jikin sa yayi da turare mai ƙamshi,sannan ya nufi  shoe rag dinsa, takalmi ya dauko me kyan gaske shima brown color. masha Allah kawai zamu ce dan ba karamin kyau yayi ba,wayoyin sa dake bedside ya dauka fita yayi daga bedroom din sai zuba kamshi yake,down stairs ya nufa parlorn ammy,a zaune ya sameta tana karatun Qur'an.
tana kai aya tace "sai masallaci kena"
"eh ammy" ya bata amsa
"to shikenan a dawo lpy nima zanje gida domin na ƙarasa  duba jikin baba"
"to saikin dawo, Allah ya bashi lafiya, nima in sha Allah yanzu daga masallaci zan biya na gaishe shi,saina dawo" ya faɗa haɗi da kama hanyar fita,Ammy na cewa a dawo lafiya, da innah  asabe ya cikaro ( mai Aikin su) zata shiga wurin Ammy, gaishe da Ita yayi ta amsa mashi da ita
"lafiya lau Shazim,har za'a tafi masallaci kenan?"
"eh" ya bata amsa haɗi da ficewa daga falon ya nufi parking space motarshi ya shiga,mai gadi ya buɗe masa gate ya fice.

_KATSINA._
AIRAH

Zaune take bakin gado jikinta daure da towel da alama wanka zatayi .
"sister gaskiya kiyi sauri ki fito nima nayi wanka, kin san yau abie  zai dawo kuma mom tace muje gidan granny mu gaishe ta,har so nake muje gidan aunty safiya ( kanwar Mom wacce suke uwa daya uba daya) mun kwana biyu ba muje ba"
Aairah ta fada.
fitowa Aaimah tayi daga bathroom jikinta daure da towel "ba wani nan sis, zaki ziyara ne ko dai za kije ganin ya MUS'AF dan nasan halinki sarai"
"Amma wlh Aaimah kin bani da sharri,yau she nace maki saboda  shi zanje gidan ni dai ziyara zani bawai saboda  ya mus'af ba,dan wallahi ki bari kar ki jaman ya Abdallah yaji wannan maganar"
"ai kuwa saina fada masa,nace ba kiji gargaɗin da yayi maki ba, ni wallahi har mamaki ki ke bani,kirasa dawa za kiyi soyayya sai ya mus'af , harka duk ta yarinta" "eh naji matar babban mutum, sai mi ko da ace na girmi ya mus'af  ina ruwan ki" Aairah ta fada tana hura hanchi
"Allah ya baki hakuri Aairah  ni nayi nan" Aaimah ta fada tana nufar dressing mirror bathroom Aairah ta shiga shaf shaf Aaimah ta shirya cikin atamfa super Red color ɗinkin riga da skirt,tana nan tsaye tana fesa turare Aairah ta fito sai ɓata rai take.
shiryawa itama tayi cikin atamfa color daya data Aaimah tana gamawa ba tai ma Aaimah magana ba taka ma hanyar fita daga bedroom din, murmushi Aaimah tayi tana cewa " kina fa iya cewa kinji haushi" bata bata amsa ba sai tsaki da taja
"haba twin sis kiyi hakuri, bazan sake ba kinji ta ya mus'af,  sorry pls" Aaimah ta fada tana matsowa kusa da Aairah sake bata hakuri tayi tana cewa "haba abun gidan ya mus'af  kiyi dariya mana dan Allah" tafa da tana langwaɓar da kai, murmushi kawai tayi tana cewa "wallahi Aaimah ki daina kushe man ya mus'af,  In dai kina so mu zauna lafiya da ke"
"kaina bisa wuya na daina in sha Allah" Aaimah ta fada tana jan hannun Aairah su ka fita,bedroom din mom su ka nufa, samun ta su ka yi a zaune gaban dressing mirror tana saka sarka a wuyanta sanye take da wani hadaden less brown color ta sha daurin ture kaga tsiya hannunta ya sha adon ɗan hannu da zobe kalar sarkarta, har suna haɗa baki wurin faɗin masha Allah Aaimah ce ta ce "kice yau an tashi rikita mana abie  kenan,wannan kwaliyya haka mom,ai sai ya ka sa gane ki, yayi tunanin sabuwar amarya aka kawo masa"
Aairah tayi charab tace "ba ki ga harda ture kaga tsiya ba,  lallai duk wanda ya ture ya taro match ba yan ball" murmushi  kawai mom tayi tana cewa "kun rainani ko, na lura ni kuka maida granny da dadi"
Aa wane mu kawai dai munga kin hadu kar abie  ya rikice" "Allah ya shirya ku" mom  ta faɗa da ameen suka amsa, Aairah tace "daman mom  daga gidan granny  zamu wuce gidan aunty safiya  dan Allah"
"shikenan Idan kunje kuce ina gaishe ta"
"to shikenan mom  za taji In sha Allah amma sai abie  ya shigo sannan zamu tafi"
"to shikenan mom  ta fada..

Ya Abdallah ne ya shigo bedroom din sanye yake da shadda maroon color, sallama yayi hadi da shigowa, gaishe da shi su Aairah su kayi sun ficewa zuwa falo, zama su kayi kan sofa suna kallo.
a chan kuma bedroom din mom  gaishe sa Ita Abdallah  yayi, amsa mashi tayi tana cewa "har ka dawo daga masallachin?"
"eh mom"  ya bata amsa "abinci fa, a kai maka part dinka ko za ka sauko kaci a dinning"
"a'a a barshi nan zan sauko Idan abie  ya shigo sai muci tare da ku,nayi waya da shi da ina kan hanya wai ashe ya dawo yana gidan dadi  (kakar su ta wurin uba mahaifiyar Abee) amma yanzu zai baro gidan"
"to shikenan bari nasa ajera abinci kan dinning sai muci tare da da shi,dama nayi tunanin basu kusa isowa ba" "to shikenan mom ni na wuce part dina kafin ya kai da shigowa" ya faɗa yana ficewa itama mom  fita tayi direct kitchen ta wuce a chan ta samu baba larai na zuba abinci cikin warmers "yawwa baba kice harkin kwashe kafin na zo,  halan kinga najima ban dawo ba sallah nayi sai nace bari kawai nayi har da wanka tun da nasan lokacin da zan dawo na san a bincin ya nuna kuma barrister na hanya shiyyasa" "A'a nima sai da nayi wankan da naga baki sauko bane kuma ya nuna sai nace bari kawai na kwashe, to shikenan bari na jerasu a dinning" mom  ta faɗa tana daukar warmers din ta nufi dinning bala  driver ne ya shigo hannun sa dauke da kaya suna cikin gaisawa da mom  su ka ji sallamar abie daga bayan su, saukowa su Aairah su ka yi da gudu jin sallamar abie,  nufar sa su ka yi da gudu, hugging din su yayi yana murmushi sun bi sun makalkale shi mom  ce ta matso tana cewa 'ku sa ke sa mana,  kunbi kun makalkalesa"
"mom  kwana biyu fa baya nan"
"to ko baya nan fa , ya kwaso gajiya shine zaku kara masa wata, ku sake sa nace" sakin sa su ka yi kan sofa suka  zauna,  shi kuma up stairs ya haura shi da mom , bala ne ya sake shigowa da wasu kayan na abie,   jakar kayan abie  kadai bala ya kai sama sauran kayan kuma kitchen ya nufa dasu .
AFTER 25 minutes......

abie  ne da mom  ke saukowa daga up stairs abie  har ya chanza kayan jikin shi da alama wanka yayi dinning su ka nufa, tasowasu Aairah su kabyi su ma suka nufo dinning din
"Aairah maza kije ki kira yayan ku" mom ta fada, tashi Aairah tayi direct part din ya abdallah  ta nufa tsit parlorn  shi yake ba ko wa sai kamshi kawai dake tashi ya hadu parlorn  golding color ne komai na ciki , bedroom din sa ta nufa nocking tayi tambaya yayi waye
"Aairah ce yaya, mom ta ce ka sauko abie  ya dawo"
"ok gani nan zuwa" yace fita tayi daga part din ta koma wurin su mom
"ya ce ga shi nan zuwa" ta fada yayin da take samun wurin zama, serving din su Aaimah ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login