Showing 3001 words to 6000 words out of 127932 words

Chapter 2 - DOCTOR SHAZIM HAUSA NOVEL

01 Apr 2025

6686

ku zauna ko sai ranku ya baci,sakarkarun banza da wofi,  wallahi kushiga hankalin ku kullum girma kuke amma ɗabi'un ku sak na yara”
kowace a cikin su ta nemi wurin zama, baaba larai ce ta matso zatayi serving ɗin ya abdallah tana faɗin " abdallah  an tashi lafiya"
"lafiya lau baaba,  ina kwana," Alhmdllh tace "mizan zuba maka?"
"a'a kibarshi kawai baaba Aairah ta zuba man,"
"to shikenan ni bari nawuce kitchen"
Aairah yace ma tayi serving ɗin sa ita kuma Aaimah tayi sauri ta chanzo hijab ɗin  ta tunda sungama breakfast ɗin su , to tace haɗi da tashi ta nufi  bedroom ɗin su.

Abie  ne ke saukowa shi da mom hannun ta riƙe da  jakar kayan sa  ,  "abie  kafito " ya abdallah  ya faɗa  ayayin da yake kar ɓar jakar kayan a hannun mom,yana faɗin "abie muje koh" yayin da yake fita daga parlorn , bayansa suka bi har da Aaimah wacce sakowarta kenan daga bedroom ɗin  su da taje chanzo hijab,"adawo lafiya,  alhaji Allah ya kiyaye hanya yakai ka lafiya ya dawo da kai lafiya" "ameen ya rabbi baaba larai" abie  ya amsa, fita sukayi compound ɗin  gidan wurin motar abie suka wuce wacce bala driver  ya daɗe  da fito da ita dan har ya abdallah ya saka ma abie  kayan shi a booth ɗin  motar bankwana suka shiga yi, su Aairah har da hawaye abie  sai lallashin su yake.

abdallah ne yace" dan Allah abie  ka kyale  yarannan  sai sun sa kayi late", "kuyi hakuri bazan jimaba zan dawo may be na dawo nan da 2 days kunji" "to abie  Allah yatsare hanya"
ameen abie yace
abdallah ne yace "to kuwuce ciki ku ɗauko school bag ɗin  ku na ajiye ku a school,  abie  Allah ya tsare"  ya faɗa   haɗi da tasa keyar su Aaimah zuwa ciki, mom ce ta matso kusa da abie  tana cewa "wallahi barrister kamar kar ka tafi nake ji"
" to fah yara shagwaɓa  uwa shagwaɓa  toni wazan kama" ya faɗa  yana dariya "uhmm kaima kasan wanda zaka Kama" ta faɗa tana ɓata rai,  "yau naji,shiyyasa kenan kika ƙi magana sai da yaran na ki suka shige ciki zakiyi man adawo lafiya , ashe shagwaɓa  za'ayiman ban sani ba ", mom tace "ok hakama zakace "ta faɗa haɗi da juyawa zata nufi ciki ,  hannun ta abie  ya riƙo yana faɗin  "Sorry kubrah,  kema kinsan wasa nake , karki damu bazan jima ba zan dawo in sha Allah"

"to shikenan Allah ya dawo man da kai lafiya" ameen abie  ya faɗa  yayin da yake shiga cikin mota,back seat ya shiga   bala driver na  gaba, key yayima motar, hanu mom ke ɗaga ma abie  shima yana ɗaga mata suka nufi gate,buɗe masu gate baba mai gadi yayi yana faɗin a dawo lafiya " mom na nan tsaye har sai da motar tafita daga gidan sannan ta juya tashiga ciki , dasu Aairah tacikaro suma sun fito a dawo lafiya tayi masu tawuce ciki abdallah  ne ya sauko daga upstairs part din sa  
Yana ce masu ku wuce mu Tafi.

  🌹~KAINAAT~🌹

Fita sukayi wajen mota suka shiga abdallah  ya jasu gate suka nufa wanda tun fitar abie  baba mai gadi yabar masu shi a buɗe, gaishe dashi suka yi ya amsa  yana masu adawo lafiya da ameen abdallah  ya amsa yayin da suke fita daga gidan,
abdallah  ne yace" dama ana duka a school ɗin  ku,wallahi da sai nasa  yau anyi maku shegen duka"
"dan Allah ya abdallah kayi hakuri bazamu ƙara ba"
"kun dai ci sa'a kawai da ba'a duka da kungane kuranku yau, da daga yau baza ku sake baccin safe ba, ace wai kuna bacci har school bus ta tafi kuga yan hutu koh?"

“Kayi hakuri dan Allah wallahi baza mu ƙara ba"
"ni dallah  ku man shiru,sai bada hakuri kamar masu tuban gagaskiya  bayan nasan ƙarawa za kuyi" ya faɗa  yayin da yake hawa kan titin ring road  in da a nan ne school ɗin  su take.
A bakin gate ɗin  school ɗin  yayi parking tare da cewa "ku fito ku wuce ciki, fita su ka yi suna yi mashi adawo lafiya Allah ya sa yace, motar yayi ma key ya bar wajen tare da Kama hanyar hospital ɗin  da yake aiki...
Ep 3_4

LITTLE ANGELS PRIMARY AND SECONDARY SCHOOL. shine sunan school ɗin,
Kamar yanda school uniform ɗin  suka kasance pink and white color haka fentin school ɗin  shima pink and white color ne.
Cikin school ɗin  suka shiga Masha Allah school ce mekyan gaske  ta yayan masu arziki Upstairs ce makarantar wanda ya kasan ce down na yara up kuma na manya ne, up stairs suka nufa domin an daɗe da gama  ASSEMBLY shiyyasa su ka nufi class,  S. S. 3 shine class ɗin  su , shiga su kayi ciki,master ɗin  su suka samu yana shirin fita,domin ya gama abunda ya kaishi.

"Aairah  And Aaimah   Muhammad  hashim , why are you coming late" mastern ya faɗa
“Sorry sir we have wake up too late,that the reason why we came to school late,it will never Happen again" Aaimah ta faɗa  yayin da Aairah  ke ta ɓata fuska irin tafi ƙarfin  ta bashi amma sa.

"this should be the last,  get sitet"mastern ya faɗa haɗi da ficewa daga class ɗin .

Kallan juna su kayi su na kwashewa da dariya, Aairah tace "Why are you coming late" tana kwaikwayan maganar master ɗin , dariya su ka sake kwashe wa da Ita,
Aaimah tace this should be the last. wannan karan duka yan class ɗin  ke dariya.

Sit ɗin  su suka zauna suna cigaba da dariya,
"Allah ya shirya ku twins domin yanzu abun naku sai adu'a,musamman ma ke Aairah da uncle Hamza na magana sai wani harar sa kike,"
"bazaki gane bane Aeesha" Aairah ta faɗa  wacce aka kira da Aeesha tace "to ganar dani"

"Ke wallahi haushi uncle hamza nake ji,dafa Ina masa kallon mutumin arziki ashe dan banza ne, baki ji munce ya dai na zuwa gida yi ma na lesson ba, Ai korar sa ya abdallah  yayi, saboda abun da ke kai shi bashi yake yiba, Ko kunya baijiba yace wai yana son Aaimah,sai kuma yana lesson kiga yana ƙoƙarin taɓa ma mutun hannun,ai kuwa rannan ashe duk abun da yake faɗa  a kunnan ya abdallah,  shine fa ya kore shi yace karya Kara ganin sa, to Wallahi in taƙaice maki ko mu dukan da mukasha wurin ya abdallah  sai kin tausaya mana,dan Wallahi buguwa mu ka yi kamar gangar church,kuma mom tace ba ruwan ta gashi abie  baya gari, shiyyasa duk na ganshi Nake jin kamar na shaƙe sa"
Aairah  ta faɗa   tana hura hanci, Allah ya shirya sa to Aeesha ta faɗa  ,  Ameen  dai.
be silent biology teacher su ne yace haka wanda shigowar sa kenan yasame su suna ta surutu, natsuwa suka yi suna sauraron lesson ɗin  da yake masu.

_F. M. C  MEDICAL CENTER_

zaune yake a office ɗin shi da ke Amenity, waya ce a kunnan sa da alama waya yake.
"haba dude ai dole nace haka tsawan shekarar mu nawa muna tare ace baka taba ziyar ta ta ba,su mom ma a suna ka ɗai  suka sanka sai waya, ai tare bata ce haka ba amma nasan maganin ka, zan haɗa ka kawai da ammy ne nasan ita zata saka kazo ba dan kashirya ba,ko nasa mom  takiraka may be kazo"  ya abdallah ya faɗa, On the other hand na cikin wayar yace “sorry my man ba haka bane, nima ina san zuwa to ayyuka ne suka man yawa shiyyasa, amma in sha Allah ina nan zuwa very soon”
“ai nima ina da tarin ayyuka amma Nake ajiye su na ziyarceka,idan kuma Sai zanyi aure zaka zo naji to, duk da in zanyi sai tare da kai, don ina samun mata zan haɗa ka da ammy  kaima ka fito da taka ko a bayar da kai sadaka"  abdallah ya faɗa  yana dariya.
"haba kaima kasan wa za'a bayar sadaka,In dai aure za ka yi bisimillah ban hanaka ba,amma ni ba yanzu ba.
"shikenan tun da kai bazaka chanza ba kullum ace mutum amsar sa ɗaya, ina gaishe da su ammy "ya abdallah  ya faɗa .
"zasuji in sha Allah nima ka gaishe  man dasu mom  kace mata ina nan zuwa very soon "
"Allah yasa domin kuwa na san halinka,"
“Karka damu dude zan zo in sha Allah, to shikenan sai anjima , Abdallah  ya faɗa ,
"ok nagode sai anjima" kashe wayar yayi, haɗi  da fita daga office ɗin zuwa dakin tiyata.
 
10:00 am
LAGOS.

_EKO HOSPITAL._

Patient ne zazzaune wanda da alama sun zo ganin likita ne.
wata  Nurse ce tafito daga Office  aƙalla za tayi kimanin shekara 25, sanye take da fararen kaya riga da wando, hulace kawai akan ta saɓanin wasu nurses ɗin  da ke sanye da baby hijab.
baƙa ce amma ba baƙi sosai ba,wurin patient din ta nufa “DR na hanya” ta faɗa yayin da take amsar Katin patient ɗin, wani dattijo ne zaune shi bai bada card ɗin shi ba da alama ma baiji mi nurse ɗin tace ba,"hey, bring your card"
nurse ɗin  ta faɗa  ganin bai ba da na shi ba "ƴata ni bana da kati,yau nafara zuwa"
dattijon ya faɗa  dakyar da alama ba karamin jin jiki yake ba,cikin harshen hausa tafara magana duk da ba ta yi kama da hausawa ba kuma bawani iya hausar ta yi ba sosai " to ya ka ke so ayi,katin ka ke so nabaka ne komi?"
"a'a naji ance  ana bada magani kyauta shiyyasa na zo" dattijon yafada, wani kallon rainin wayau take ma dattijon har ya gama magana, cikin karaji da ɗaga murya tace "hey hausa people na bani mamaki, to bari kiji nan ba charity hospital  bane, dan haka ki tashi kiba mutane wurin, in ban da abunki ta ina wannan hospital ɗin  tayi kama da charity hospital  koh ance maki irin hospital ɗin kune na Arewa??" nurse din ta faɗa  tana nuna mashi hanyar fita.
 "haba Victoria kin manta mi doctor yace ne duk lokacin da marasa ƙarfi suka zo?" wata kyakyawar nurse ke faɗin haka, chocolate color ce a ƙalla za ta yi kimanin shekara 23 itama sanye take da fararen kaya rigada wando sai farar baby hijab, zuwan ta ke nan tasamu victoria  nayima dattijo masifa Ita bahaushiya ce saɓanin victoria
"ina ruwana, ai yanzu ba ya nan sai dai in ke ce zaki faɗa  masa”
Kasa tashi dattijon yayi jikinsa sai rawa yake, tsawa ta dakama dattijo, haɗi dacewa  "I said get out from this hosp..., kasa ƙarasawa tayi adalilin saukar wani  mahaukacin mari dataji a kuncinta,ba tai aune ba ta sake jin wani marin a dayan kunchinta bashiri ta kife ƙasa, gaba ɗaya hankalin patient dana nurses ya dawo kan  wanda yayi marin.

Tsaye yake jikinsa sanye da scrub suit blue color, ƙafarsa na sanye da black din takalmi sai hannunsa dake riƙe da  briefcase da lab coat ɗin  sa,  dogone  yana da tsayi,fari ne sosai kyakyawan gaske, yana da dogon hanci sai eyes masu black ɗin  eyeball, small mouth me ɗauke da red lips, sumar kan sa wacce tasha gyara ko nace take kan shan gyara black color ta leƙo ta cikin Arab Turban ɗin dake kanshi ta ɗan sauko har saman neck ɗin shi,kallo ɗaya zaka mashi ka kira shi da balarabe ko kuma halfcast akallah zai kai kima nin shekaru 28 zuwa da 30.

Good morning sir, nurses ɗin suka shiga gaishe da shi, hannu kawai yake ɗaga masu yana kiran security,
ƙarasowa  security ɗin  su ka yi suna gaishe da shi cikin girmamawa, amsa masu yayi yana  nuna masu dattijon ya
ce su shigar mashi dashi office ɗin shi yayin da yake ba ɗaya daga cikin securityn key din office ɗin  shi,  kamashi su ka yi suka ɗaurashi akan wheelchair wannan nurse ɗin ce wacce tayima victoria magana ta matso kusa da shi, hannu ta mika zata anshi briefcase ɗin dake hannun shi  dakatar da Ita yayi,  magana ya fara cikin harshen turanci nurse "hidaya me nace ne gameda masu zuwa neman taimako? "
" kace duk wanda yazo neman tai mako ah EKO aturashi ABNOOR,  kuma itama nurse Victoria ta sani kuma sai da nasake faɗa mata da tana ma datijjon faɗa"
"shikenan koma dai miye Wannan yazama nakarshe, in dan kuwa ba haka ba dukkan ku sai ranku ya ɓaci "ya fada haɗi da nufar office ɗin  shi

    🌹~ KAINAAT ~ 🌹

Tasowa victoria tayi daga duƙewar da tayi domin ta maru, haryanzu bata dawo dai dai ba,  masifa tafara yima nurse Hidaya akan Ita ta  haɗa ta da dr haryayi mata wannan marin,  "to bari kiji Victoria garama tun wuri kifita daga harkata,basai da na gargaɗe ki ba, amma mikika ce ke kina ganin dr  shazim bazai iya yimaki komai ba ke yar gaban goshi,  ke dai kawai za fin mari ne yasa zaki sauke a kaina mizai hana shi dr bazaki bishi office kiyi mashi masifar ba "hidaya ta faɗa   tana dariya sauran nurses ɗin  ma dariya suke saboda  sun san magana  ce hidaya ta faɗa ma victoria  saboda  ba ƙaramin  so take ma DR. SHAZIM  ba,  mutsww victoria taja tsaki saboda haushin dariyar da suke mata ta kuma gane miyasa su dariya wuce wa tayi office ɗin  dr  saboda  itace ke tura mashi da patient, 
Shiga tayi cikin office ɗin  haɗi dacewa,  good morning sir  zaune yake yana rubutu ajikin file wanda da alama na wannan dattijon ne yayin da dattijon ke kwance  bisa gadon marasa lafiya a office ɗin , ko kallon inda take bai yi ba,sake gaishe da shi tayi,  kira man nurse hidaya abun da kawai ya ce mata kenan, hakuri ta shiga bashi dan bazata iya daina aiki dashi ba domin in har chanzata zaiyi da nurse hidaya to sai dai tabar hospital ɗin saboda  bazata juri ganin shi tare da wata ba,   tsawa yada kamata domin yaga bata da niyyar fita daga office ɗin yace " get out from my office" ya na nuna mata hanya,  fita tayi daga office ɗin  zuwa office ɗinsu  na nurses,tana shiga ta  fashe  da kuka,  tana faɗin  bazai yuwu ba wlh dr  shazim  nawa ne ni ka ɗai, babu wacce ta isa ta raɓesa sai ni,taƙara fashewa dawani kukan,  wata nurse ce tashi go office ɗin wacce itama daga ganin ta ba muslma bace tana cewa , "ai yanzu kika fara kuka victoria, tadama ba sai da na faɗa  maki ba kitashi tsaye  amma kika ƙi ji,wanda kuwa duk yaƙi ji ba yaƙi gani ba, to wallahi  Idan ba kiyi wasa ba kina nan sake da baki hidaya zata kwace shi, sai dai  kizama ƴar kallo"
"haba destiny yaza ki man wannan mummunan maganar,   kisan kuwa yanda nake son dr shazim kuwa,da kinsan yanda nake son shi da baki ce haka ba"
" victoria kenan ina ga bakisan halin hausa peoples bane, zaki sha mamaki in kika tsaya wasa domin kuwa Ita hidaya yarensu ɗaya bayan nan religion ɗin  suma ɗaya kina ganin zai kula ki ne yana ganin hidaya, kawai kitashi tsaye"
"to ya zanyi ki bani shawara pls"wani munafukin murmushi destiny tayi haɗi  da cewa yanzu dai kifara kira mashi hidaya tukkun nan zuwa anjima sai muyi magana"
" haba destiny  yaza ki ce nakirata, sai dai yaji haushi amma ni bazan kira taba wlh" "kaji sakarya,idan baki kira mashi ita ba taya zai gane kintuba, kuma itama hidayan ki roketa akan ta tayaki bashi hakuri nasan zatayi,"
"uhmmm shikenan ta faɗa  haɗi  da barin office ɗin  domin kiran hidayar, dariya destiny ta kwashe da Ita haɗi da cewa "zaki gane baki da hankali Victoria, zaki san cewa ni ba kanwar lasa bace, yanda ki ka ƙi brother samuel to haka zaki rasa shazim  shima sakarya kawai" .

wurin su hidaya Victoria ta nufa,tana zuwa ta tsaye tayi tana riƙe da ƙugu tace
"kizo dr nakira” tana faɗa ta juya kai gefe "wakenan acikin mu?" wata a cikin nurses ɗin  dake zaune  ta faɗa , "tasan kanta ai"acewar Victoria, sarai sun gane hidaya take nufi saboda sun San tana yar tsama da Ita amma sai suka nuna basu gane ba "hidaya kinsan fa ke nake nufi amma kinyi kamar baki ganeba zanje na faɗa  masa bazaki zoba"
" ke jiman Victoria da karfin halin, kin faɗi sunanta ne daza kice ta ƙizuwa"
"ah to gane mana hanya sister maryam" acewar wata daga cikin nurses ɗin  "haba Victoria ni na rasa me hidaya ta tare maki a hospital ɗin nan,ai ko bakomi ƴar uwarki ce tawurin aiki,  amma ace kullum baki da abokiyar faɗa  sai Ita"
"karka faɗa man mgnr banza mana Joseph ina ruwanka" victoria ta faɗa tana wani huci
 "sorry shawara ce" barin wurin yayi wanda aka kira da Joseph
"mike faruwa ne anan cewar destiny wacce isowarta kenan, a'a hidaya Victoria bata faɗa  maki dr na kira ba nagan ki zaune ko har kin dawo daga wurin shi ne??"
"A'a destiny yanzu zanje"ok destiny ta faɗa haɗi  da cewa "kefa Victoria naga kinyi tsaye ku tafi mana" bin bayan hidaya destiny da Victoria su kayi suna ɗan yin nisa da sauran nurse's ɗin  destiny ta ɗan taba Victoria alamar ta roki hidaya akan ta taya ta ba dr  haƙuri, ganin baza tayi ba ne yasa destiny dakatar da hidaya tana cewa "kiyi hakuri hidaya akan abun da Victoria tayi maki,haushin dariyar da kuka yi mata ne ɗazu yasa tayi maki haka,  amma kiyi hakuri"
"shikenan bakomi, ni da man ba waina riƙe ta ba ne" "shikenan amma ki taya ta ba ma dr hakuri pls karya cireta daga cikin nurses ɗin  dake tura mashi patient pls" a ranta take faɗan"ok shiyyasa kenan tazo ta ciman mutun ci"amma  a zahiri sai tace "bakomai yawuce in sha Allah zan taya ta" thanks Victoria ta faɗa  yayin da suka kawo office ɗin  shiga ciki su ka yi sallama hidaya tayi yayin da Victoria ke bayan ta
“good morning dr" hidaya ta faɗa
"morning,ki saka patient a layi amma mutum 15 kawai zan duba  sauran kiturasu office ɗin  DR KABIR" Dr shazim ya faɗa ba tare da ya ɗago ya kalle su ba
 "sorry sir  ni ina iya tura su" a cewar Victoria data ga yayi kamar bai san tana wurin ba, 

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login