Showing 24001 words to 27000 words out of 127932 words

Chapter 9 - DOCTOR SHAZIM HAUSA NOVEL

01 Apr 2025

6696

jikin sa. 
Zaune su ka same shi a parlorn shi yana duba littafi, sallama su ka yi hadi da shiga cikin,cikin parlorn,  amsa masu sallamar yayi yana tambayar  su ya aiki,  da alhmdllh suka amsa mashi
Shazim ya ce"ya ƙarfin jiki"
"Masha Allah jiki alhmdllh , yanzu ko ina ina iya  zuwa Alhmdllh"
"Masha Allah Malam, Allah ya ƙara sauki da nisan kwana mai amfani"
"Ameen ya Rabbi"
"Malam ko dai lokaci ne yayi, muyi shirin cin gumba" noraiz ya fada yana dariya
dakkuwa malam yayi mashi "lallai nuraddeen  ni kake ma fatan Mutuwa koh, to sai dai mahaifiyar ka ta mutum amma bani ba, ja'irin banza"
dariya Noraiz ya kwashe da ita yana fadin "yanzu nan malam baka san mutuwa"
Shazim dai na gefe yana jin su in ban da murmushi ba abun da yake
"mutuwa na kan kowa nuraddeen , yaushe musilmin ƙwarai zai guji mutuwa, kawai dai ana tsoron mi za'a riska in an je can"
"haka ne kam Malam, Allah dai yasa mu  mutu muna ma su Imani"
da Ameen suka Amsa su duka, nan malam ya shiga yi masu nasiha a kan ruƙo da gaskiya da kuma aiki da ita da tsare mutuncin kai, sannan ya ƙara yima shazim fada a kan  ya fitar da mata  yayi Aure shekarun sa ƙaruwa suke ba raguwa ba,  kuma mahaifiyar su bata da wani buri daya wuce taga ta aurar dasu baki daya shine kwanchiyar hankalin ta, saboda dangin mahaifin su gani suke kamar ita da malam su ka hana shi  yin aure, "Shazim ko baka so naga jikokin jajirtaccen jika na ne" duƙar da kanshi yayi ƙasa yana cewa "ba haka bane Malam,In sha Allah zanyi ƙoƙari nayi nan kusa"
"to Allah ya yarda, ya kuma za ba maka mace ta gari kai da ɗan uwanka, itama fatima Allah ya bata miji nagari"
da ameen suka amsa su duka har da ummy wacce shigowar ta kenan parlorn taji suna adu'a shine itama ta amsa da ameen.
gaishe da ita su kayi , cikin kulawa ta amsa tana tambayar su ammy,  shazim  maganar kasuwancin shi da yake son noraiz ya cigaba da kula da su yayi ma malam da noraiz ɗin kan shi, "eh wannan shawara ce mai kyau,dama ya kamata ka rage ma kanka wasu abubuwan,"
"hakane,dama jiran dawowar sa nake na tattara komi na miƙa masa"
"yayi hakan Allah ya taimaka,amma ko da noraiz ɗin ya amsa ka bar hameed su cigaba da kula tare, duk da noraiz abun da ya karanta kenan, zai ƙara samun wasu dabaru wurin hameed"
"eh daman shawarar da na yanke kenan"
"to Allah ya tai maka"da ameen suka amsa
sun jima  sosai gidan malam dan sai wajen Karfe 10 na dare  sannan suka tafi gida bayan malam ya sha maganin sa,da yake yana sa shi bacci .
Suna shiga gida parlorn Ammy suka nufa anan su ka sameta ita da  Fatima zaune, sallama su ka yi , amsa masu Ammy tayi tana cewa "nayi tunanin baba ya rike ku sai kwana, ashe zaku dawo"
"Wlh kuwa zamu dawo, ya gida"
"gida alhmdllh gashi nan"
fira suka ɗan taba Ammy nace masu ga dinner din su can kan dinning  suka ce sun koshi dan sun ci dinner gidan malam
basu  jima ba kowa ya nufi dakin sa saboda dare da yaja sosai.....

Haka rayuwa ta cigaba da tafiya wataran dadi wataran akasin haka su Aairah sun fara zana jara bawar gama secondary school  har sun  kammala, haka zalika fatima ma ta gama  Noraiz  watan shi 2 da sati 3 da dawowa kenan.  

Zaune  ammy take bakin bed, wayar tace da ke kan bedside ta fara ringing ɗaukra wayar tayi tana kallon mai kiran, ya ya Ahmad shi ne sunan mai kiran nata, dafe kan ta tayi tana faɗin "ya salam,Allah ya sa bawani abun bane" picking tayi haɗi da kara wayar a kunne tana sallama, amsa mata sallamar na ciki wayar yayi, gaisawa suka yi, tana tambayar yasu hajiya asiya da su kairiyya, da lafiya lau ya amsa mata sannan yace
"wai A'isha mi ku ke nufi ne ke da shazim, tun yaushe nake faɗin idan na kira shi bana samun shi"
"kayi haƙuri yaya, tun ranar da ka kira na faɗa mashi ya kira ka, na yi tuna nin ya kira"
"yaushe zai kira,yasan zan mashi maganar da ya tsana, wacce yake ganin bamu kai matsayin da za muyi mashi ita ba"
"ba haka bane yaya, dan Allah kayi haƙuri, zanyi mashi magana ya kira ka yau"
"to, daman na kira ne dan in faɗa maki ina son ganinshi shi da ƴan uwan shi a cikin satin nan"
"to yaya, zan faɗa mashi"
"to shikenan, sai anjima"
"to Allah ya kaimu"da ameen ya amsa haɗi da yin rejectin, a jiye wayar ammy tayi tana faɗin
"na rasa gane halin shazim, idan har bai jaman abun magana a wurin su hankali shi baya kwanciya, amma na san maganin shi" ta faɗa haɗi da miƙewa ta nufi part ɗin shi, yana parlor zaune,  tambayar shi tayi ina wayar shi, "gata nan ammy, lafiya"
"kira ya ya ahmad yanzun nan "
"amma ammy mi yasa"
"zaka kira shi ko kuwa sai ka gama tambaya ta dalili"
"A'a" kawai yace haɗi da ɗaukar wayarshi yayi dialing number uncle Ahmad, tana fara ringing, aka ɗauka, sallama yayi haɗi da cewa "ina wuni uncle" da lafiya uncle ahmad ya amsa, sannan ya ɗaura da cewa "shazim laifin mi muka yi maka da idan mun kira ka baka ɗauka, kuma kai ba zaka iya kiran mu ba?"
"bakomi uncle"
"to shikenan, ina son ganin ka abuja kai da ƙannan ka a cikin satin nan"shiru yayi baice komi ba, uncle ahmad ne yace "baka ji mi nace ba ne"
"A'a naji, amma uncle aiki na ya zanyi da shi"
"Ina sauraron zuwan ku kana ji na ko"
"eh naji" rejecting uncle Ahmad yayi batare da ya saurari mi shazim ɗin zai sake cewa ba,
"sai ku shirya kai da su"
"haba ammy, ni bazan je ba"
"to wallahi bari kaji ba zaka dinga ja man zagi wurin su ba kaji na faɗa maka, gara ma tun wuri ka shirya ku tafi"
"to, amma sai next week "
"Allah ya nu na mana"ammy ta ce haɗi da ficewa ta bar part ɗin...
  13
   
✨Noraiz-Fatima✨

zaune suke  parlorn Ammy, fatima na duba wani novel  yanzu ba school  sai Islamiyya, shi kuma yana aiki a laptop ɗin  sa, aje novel din tayi tana cewa
"ya noor  ka kuwa tuntubar man big bro maganar school  ɗin dan Allah?" ture laptop ɗin  yayi yana cewa "kima bar wannan maganar,dan wallahi yace kusa da Ammy za ki yi karatu,ki tambayi  Ammy ma a gabanta yace haka, har sa baki tayi amma yace a'a"
"hai wai shi ya Shazim miyasa yake haka dan Allah,to yaya ita Ammy mi zai hana tace sai nayi "
"kawai kiyi haƙuri  kiyi karatun ki anan a kwai makarantu masu kyau kamar na can zaki samu duk abun da ki ke so, kuma na san zai sama maki mai kyau da tsada"
"ya noor ya zanyi dole na hakura, Allah ka ɗai yasan dalilin sa na hana ni"
"nasan bazai wuce saboda innah ba"
"anya dai, Allah yasa haka alkairi ne"
"ameen "Noraiz ya faɗa 
(Suna da saurin fahimtar dan uwansu saboda sun ɗauke  shi tamkar mahaifin su da suka rasa tun basu san kan su ba,   sabanin wasu yan uwan idan akace mahaifin su baya da rai,za ka samu rashin jituwa da ƴan uwansu musamman suna son wani abu,da ɗan uwan yanuna masu illar dake ciki abun maimakon su fahimce shi, sai kasamu suna kullatar shi a rai wasu harsu kai da faɗin  dan yaga mahaifin su baya da rai shiyyasa yake masu abun da duk yaga dama,za su dunga ɗaukar shi a matsayin mai tauye masu haƙƙi 
abu buwa iri iri dai, Allah kasa mana ƙaunar ƴan uwan mu da fahimtar su, ka bamu ikwan rufa ma junan mu asiri ameen 🙏 )

Ammy ce ta fito daga bedroom dinta tana cewa "yaya da kanwa mi ake shiryawa ne,nake jin ƙusƙus tun a ɗaki?"
"sirri Ammy,ki zauna ayi dake"
Noraiz ya fada  yana nuna mata  kan sofa,  zama tayi  tana faɗin " ina sauraro kuwa, wane sirrin ne ake shiryawa"
fatima tace "ammy maganar makaranta ce"
"mi ya faru?"
"bakomi, ya noor ya sanar dani yan da ku ka yi da ya shazim"
"hakane sai dai kiyi haƙuri "
"dama ya zanyi ammy dole na haƙura, amma ban san mi yasa ya shazim bai son zama na abuja ba "
"nima kaina ban san dalili ba nasan dai bai wuce innah"
sun jima suna tattaunawa kan maganar, sai ga shazim ɗin ya shigo da alama daga abnoor  yake saboda yau friday dama bai cika jima wa ba saboda zuwa masallaci,  wurin su ya nufo ya na faɗin "Ammy ina wuni,mi a ke shiryawa ne na ganku zazzune a parlor?"
"lafiya lau ya aiki, sirri ne kaima zo ka zauna" murmushi yayi yana neman wuri kusa da Ammy ya zauna, gaishe da shi su fatima su kayi noraiz nacewa "ashe dama na bi ka, naga ka dawo da wuri"
"ai  kafi son zaman gida ne  sai kace wata mace, zan ga yan da zaka ƙare idan kafara Aiki"
"ai koh lallai " Ammy ta fada hadi tana mangare ma shazim  kai, sosa wurin yayi yana fadin "Ammy haka ne fa, in ba mace ba miya haɗa  namiji  da zaman gida dan Allah?" dariya fatima da Noraiz suka yi ganin yan da shazim ke bata fuska , maka masu harara yayi, shiru suka yi suna ƙumshe dariya, basu wani jimaba suna fira suka tashi domin shirin zuwa masallaci ammy kuma da fatima suka tafi daki domin yin sallah suma....

✨KATSINA✨

Abie ne da Abdallah  ke saukowa daga up stairs zasu tafi masallaci, da Mom suka ci karo a parlor ta fito daga kitchen hannun ta ɗauke  da food flask "Masha Allah irin wannan kyau haka barrister, gaskiya  kar ka sa matan mutane suyi ta kalle man miji" dariya abie yayi abdallah  kuwa duƙar  da kai yayi yana murmushi a zuciyar shi yana fadin "Mom duk da an tsufa amma ana kishi, Allah ya bani mace irin Mom" nace ameen dr
"da har ina cewa zan ƙara maki a bokiyar zama, amma ki ke faɗin  haka"
"tab wallahi  kaima kasan wasa kake, ai auren mu in kaji ana auren zobe, ba saki ba yaji ba kishiya"
dariya abie ya sake kwashewa da ita yana faɗin  "za kuwa kisan ba wasa nake ba, dan daga nan zance zan wuce" in ban da dariya ba abun da Abdallah  ke ma iyayen nasa, yana kallon su cikin birgewa
"ka dai faɗa,nawa jine kawai"
"ai kuwa zaki san bawasa nake ba, kaga abdallah  wuce mu tafi kar mu makara" ficewa su kayi suna jin Mom na masu a dawo lafiya
bedroom ɗin  su Aairah ta wuce, bude ƙofar  tayi ta shiga
shiri ta same su suna yi  "yawwa kun shirya kenan"
"eh"suka bata amsa
"yawwa kuyi sauri ku ƙarasa , ga abinci can kitchen mungama ku jera kan dinning sannan su mudi ma ku tabbatar kun kai masu nasu, nizan shiga nayi wanka ne kunji"
Aairah tace
"In sha Allah za muyi yan da ki ka ce, amma Mom wai ya maganar walimar mu ne, munga ba'a fara shirin komai ba,kuma fa jibi ne"
Mom tace" tana nan mana ba jibi bane, jira nake anjima yayan ku ya kaimu shopping ko kuma abie din ku,saimu siyo duk abun da ya dace"
Aaimah tace"to shikenan Mom Allah ya kaimu an jimar" ameen Mom tace hadi da ficewa daga dakin tana sake tuna masu aikin da ta sa su, suna gama shirin suka fita domin yin abun da Mom tasa su, suna kammalawa nan main parlor suka tsaya suna kallo
su abie ne da ya abdallah  su ka shigo,sannu da dawowa su kayi masu hadi da gaisawa, amsa masu su kayi abie ya samu kan sofa kusa dasu ya zauna  ya yin da shi kuma ya Abdallah ya haye up stairs, fira suka shiga yi da abie akan walimar da za'a yi masu , sun jima suna fira har Mom ta sauko tana cewa "shiyyasa naga barrister bai shigo ba, ashe kuna nan kun tasa shi gaba da abun da kuka saba watan surutu ba"
Aairah tace"kai Mom bafa surutu muke masa ba, maganar walimar mu fa mu ke yi" dinning Mom ta nufa tana faɗin 
"to yayi,sai ku taso ga abinci na jiran ku" ta sowa suka yi har da abie suka nufo dinning din, abie nace ma
"Aaimah je ki kira yayan ku, kinji"
"to abie" ta fada hadi da nufar up stairs ta nufi part din Abdallah,samun shi tayi yana waya jira tayi sai da ya gama sannan tace "yaya ka zo mu ci abinci" da to kawai ya amsa mata, ya yin da ita kuma ta fice  tabar ɗakin,komawa  dinning din tayi, wurin zaman ta na ɗazu ta koma ta zauna plate taja wanda Mom  tayi serving ɗin  kowa, shiru kowa yayi anata bama ciki hakkin sa, sai da suka kusa kammalawa sannan abdallah  ya sauko ya nufo dinning ɗin,  Mom  tace "lafiya baka fito ba tun time din da aka kira ka?"
"Ina wani ɗan aiki ne shiyyasa" ya fada hadi da neman wurin zama ya zauna plate ɗin  abinci Mom ta miko masa, Nagode ya faɗa  hadi da daukar spoon ya fara cin abincin, suna gama wa su Aaimah suka gyara wurin yayin da  su Mom suka koma kan sofa, suma suna gamawa wurin su Mom ɗin  suka dawo,  firar walimar da za'ayi masu su ka shiga yi,  basu  tashi ba sai da lokacin sallar asr yayi sannan su abie suka wuce masallaci, suma daki suka shiga domin gabatar da tasu..

mom  ce ta fito daga bedroom ɗinta  jikinta sanye da atamfa ɗinkin  riga da zani da mayafi sai jaka a hannun ta,  ɗakin  su Aaimah ta nufa  samun su tayi duk sun sha abaya black color  sunyi rolling da gyelenta sai side bag da ko waccen su ta rataya sai glass irin na gayu ɗinnan,  shirin fita suke daga ɗakin  sai ga Mom ta shigo "yawwa kun shirya  kenan to ku fito mu wuce abie dinku da yayan ku na waje mu ka dai su ke jira" Aaimah tace
"Mom ba ki ce munyi kyau ba" yan yatsu kawai Mom ta haɗa  al'amar komai yayi,  ficewa su ka yi zuwa compound din gidan in da anan suka samu abie da ya abdallah,   shiga su kayi cikin motar ya abdallah  ke driving yayin da abie ke kusa da shi, su kuma suna baya su da Mom,a dawo lafiya su mudi su ka yi masu yayin da abdallah  ya fice da motar suka hau kan titi, wani ƙaton  shopping mall ya nufa dasu, parking su kayi a parking lot dake wurin wanda aka tanada domin masu siyayya, sai da ya gama daidai ta parking din motar,  fitowa  suka yi,  cikin  mall din suka nufa,  barka da zuwa waiters  su kayi masu,inda ake ajiye cart suka nufa,guda biyu suka ɗauka,  Aaimah na tura daya tana biye da abie da ya abdallah ,  yayin da Aairah ke tura daya tana biye da Mom,siyayya suka yi sosai,sun jima  a shopping mall sai da suka tabbatar sun tanadi abun da suka san zasu buƙata  sannan suka nufi wurin biyan kudi, Abdallah ya biya duk abun da suka siya  ma'aikatan wurin suka ɗaukar  masu kayan zuwa booth, 
wurin da ake sai da snacks suka wuce pizza  da shawarma sai ice cream ya Abdallah ya sai masu  daga nan suka wuce  gidan dadi, suna isa bakin gate din gidan ya abdallah  yayi horn, mai gadin ne ya leƙo,  ganin motar  abdallah  yasa shi  komawa ciki da sauri hadi da bude masu gate, ciki ya shiga da motar parking lot dake compound din gidan ya nufa  hadi da yin parking,  sannan suka fito,booth abdallah ya buɗe, snacks ɗin da suka siya ya ɗauko haɗi da miƙama   su Aairah,cikin gidan suka nufa,  parlor ne dan dai dai matsakaici yasha royal sofas masu kyan gaske , wata yar tsohuwa ce (dadi kenan)  zaune ita da wata mata aƙalla  zatayi kima nin shekara 38 zuwa 40 ( Aunty Rabi kenan, ƙanwar abie ce,  zaune take  da dadi tun lokacin da Allah yayi ma mijinta rasuwa,  kuma gashi Allah bai bata haihuwa ba shiyyasa ta dawo kusa da mahaifiyar ta tana kula da ita)  sallama su kayi, aunty rabi   ce ta amsa masu sallamar  hadi da cewa "wannan  shi ake kira  tafi da gidan ka, wannan ziyarar bazata haka yaya"
dariya abie yayi hadi da cewa "ke dai bari kawai rabi, munje siyayya ne saboda walimar su Aairah, shine muka biyu ta nan" nan suka shiga gaisawa, wurin  dadi  suka matsa itama suna gaishe da ita amsa masu tayi cikin kulawa hadi da taya su Aairah murnar kammala makaranta da hadda nan suka shiga fira "Muhammad  yaushe ne walimar su yan biyu" dadi  ta tambaya,  amsa abie ya bata  da "jibi ne In sha Allah"
"to Allah ya kaimu" da  ameen suka amsa , miƙama aunty rabi snakcs ɗin dake hannun su suka yi, amsa tayi tana ma abie godiya,   Aairah  tace "amma dai dadi  zaki zo koh"
"In sha Allahu kuwa, ai audu zai zo ya ɗauke  ni da kansa, koh audu" ta fada tana shafa kan Abdallah  dake kusa da ita, ɓata rai yayi yana cewa, "wai dan Allah dadi bazaki daina ce man audunnan ba,  nifa sunana Abdallah , ba audu ba" dariya su ka kwashe da ita su duka ban da Abdallah  dake zabga ma su Aairah harara saboda dariyar da suke  mashi "ai inba kishiya kayi man ba, bazan daina cemaka haka ba, shima abun da zaisa na daina kawai dan karta raina min ango ne,  amma da bazan bari ba"
"to shikenan ashe baki ba cin kaza kuwa,  tunda haka ki kace" dariya suka sake kwashewa da ita, dama duk Abdallah da dadi suka haɗu wuri daya tofa zaka sha dariya , mai aikin dadi ce ta fito daga kitchen wurin su ta nufo tana gaishe da su abie,mom   tace "uwani ashe kina nan, ya kwana biyu"
"Alhmdllh" wace aka kira da uwani tace,  su Aairah ma gaishe da ita suka yi, amsa masu tayi da lafiya lau"an kammala girkin " uwani ta faɗa , aunty Rabi  tace "to shikenan, Aairah ku ɗauki wannan snack's  kuje da shi kitchen sai  ku taya  ta jera abincin  kan dinning" da to suka amsa mata,  tashi suka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login