Showing 174001 words to 177000 words out of 185789 words
na dinga komai cikin rashin kwarin jiki........ tsaf na kammala abin kari na shirya daining din da jikina na zauna zaman jiran shigowarsa............Khalid kuwa na can tare da Yarinyar mutane sai wajigata yake Amina raguwa ce dan tun kafin tafiya tayi nisa take masa kuka da magiya akan ya kyaleta ai kamar kara tunzurashi take ya zage sosai a kanta yana biyan bukatarsa Ya samu gamsuwa amma ba kamar irin wacce yake samu gurin auntynshi ba.
Amina na share hawaye ta lalla'ba ta shiga toilet domin gyara jikinta shi kam yaji dadi sosai da ya samu budurcinta sai ya tuna lokacin daya keta budurcin auntynshi rintse idonsa yayi yana girgiza kanshi sam beso hakan ba yaso ace ta hanyar aure komai ya faru amma kaddara ta riga fata haka Allah ya shirya musu.
Yana gama kimtsa jikinshi ya fice daga dakin ba tare da ya bari ta fito daga bandakin ba hakan yayi mata masifar ciwo a hankali ta zauna gefan gado tana kukan bakin ciki yanda ya jigata ta ya bata wahala ta dauka ai zai tsaya ya rarrasheta amma da yake ba itace a ranshi ba har ya fice ya bar mata dakinta zuciyarta ta sake cika da kishin abokiyar zaman nata.
Khalid kuwa yana fita bai ko kalli Side din Auntyn nasa ba kai tsaye inda motocinsa suke ya nufa Yaron shi Chinedu ya mike da sauri yana mika gaisuwarsa motar ya bude masa ya shiga ya zauna shima da sauri ya shiga gurin zaman shi ya tashi motar kafin su fita daga gidan sai da ya sauke gilashin na motar suka gaisa da Maigadi Khalid bashi da girman kai da wulakanci yanda yake Mu'amula da jama'a abin zai baka sha'awa.
Sai yamma ya dawo gidan kai tsaye gurin Sa'ida ya nufa domin ya dubata.......Kallo daya nayi masa na dauke kaina a nutse ya karaso kusa dani ya tsaya tare da zuba hannuwansa a cikin aljihu.
Babu walwala a tare dani nace." Barka da yamma." ajiyar zuciya ya sauke a hankali yace." Barka dai kinji shuru ban shigo na dubaki ba ko."
Shuru nayi hankalina akan Tv ya cigaba da cewa." Da wurwuri na fita kuma tunda na fita ban samu kaina ba ballantana na kira wayarki ina fatan kin wuni lafiya."
Ajiyar zuciya na sauke ina d'an jin sassauci a cikin raina nace." Lafiya lau na Wuni ina fatan ka leqa gurin Gwaggo."
Yace."Aa banje ba saboda uzirin daya sha kaina mybe sai gobe zan shiga mu gaisa.'' Nace." To Allah ya kaimu."
Zama yayi kusa dani na dan kalleshi sai naga kwarmin idanunsa sun zurma. " Ki bani abinci tun safe babu komai a cikina."
Cike da mamaki nace." Tun safe babu komai a cikin ka? amma kake yawo a haka."
Hannuwansa yasa ya rufe fuskarsa da fad'in."Ke dai ki bari kawai jiya na kwana banyi bacci ba yau kuma na yini da yunwa abubuwan sunyi min yawa."
Maganar ta bani haushi sosai sai kawai na kauda kaina na rabu dashi. Ya kalleni da fad'in." Ko dai ni zan shiga kicin din na dauk'o abincin."?
"Kaje kicin din ko kuma ka tafi gurin matarka tunda a dakinta ka kwana." " Wace irin maganace wannan."?
Shuru nayi masa gabad'aya haushinsa nake ji ko kunya yazo yana fadin ya kwana beyi bacci ba yaron ya gama raina min hankali.
Ganin yanda nayi watsi dashi a gurin yasa ya mi'ke ba tare da ya sake min magana ba ya kama hanya fita, 'karamin tsaki naja tare da bin bayansa da harara.
Yau tsayin kwana ki uku kenan bai sake shigowa inda nake ba, damuwa da kadaici suka dabaibaye ni gabad'aya hankalina ya tashi na rasa abinda yake nufi dayin hakan, kullum ni kenan cikin leqen sa a duk sanda zai fita ina kallonsa ko kallon Gurina ba yayi zai shiga mota dravar sa yaja motar su tafi........Duk yanda nake kokarin daurewa sai da na kasa zama nayi naci kuka na na k'oshi na dinga tunanin hanyar da zanbi gurin shawo kansa.
Ina lissafe Yau kwanansa bakwai a gurin Jamila ya gama mata kwanakinta zai dawo guri na tunda na tashi nake jin annushuwa da farin ciki abinci kala uku nayi masa nayi ado sosai irin wanda zai ja hankalinsa. sai dai me? Daf da magariba ya kira waya ta cike da zumudi da murna na daga wayar.
Ciki-ciki ya amsa gaisuwata yace." Yau girki ya dawo hannunki ko." ? Nace."Eh." Yace." Kiyi hakuri yanzu haka bana gari naje Bauchi tare da abokanan sana'ata zanyi kwana uku sai na dawo." Kafin nace wani abu ya kashe wayarsa.
Jiki a masifar sanyaye na zube a gado kawai naji hawaye masu zafi sun k'wace min. Na riga na gama cin buri nasa rai yau karshen matsala ta dashi zai k'are saboda na gama shirya duk yanda zanyi na sanya shi cikin farin ciki bayan haka kuma a matse nake don ni kadai nasan halin da na shiga tsayin kwanaki bakwai din da yayi a gurin Jamila......Ina jin wani irin d'aci a ma'kogwarona nasa hannu na dinga share hawayen dake zuba a fuskata.
Alhaji Nura cikin shiga ta alfarma yayi parking din motarshi a inda ya saba idan yaje gidan zance fitowa yayi daga motar tashi yana gyara babbar rigar dake jikinsa......Wayarsa ya dauko domin ya sanar mata da zuwansa, Ya kira ya kai sau nawa bata shiga sai ya hakura ya fara neman yaron da zai tura gidan. Kawu ne ya fito daga gidan sai ya ganshi a jingine a jikin motarsa cike da mamaki ya karasa inda yake. Alhaji Nura ya saki fuskarsa cikin mutunci da girmama juna suka gaisa da juna.
Kawu yayi shuru yana so yaji abinda yake tafe dashi. Alhaji Nura ya gyara tsayuwarsa a nutse yace." Kwana biyu bana gari wallahi ban samu na shigo mun gaisa ba jiya na dawo naje india shine yau nace bari na shigo mu gaisa inaso naga Sa'ida domin mu tattauna abin da yake gaban mu."
Kawu yace."Ayya ashe baka garin shiyasa baka da labarin al'amuran da suka gabata." Yace."Kwarai kuwa Kawu inaso yanzu a lamunce min na bada sadakin Sa'ida ranar juma'a mai zuwa a daura aure.''
Kawu ya jima kanshi a kasa kafin yace." Alhaji sai dai kayi hakuri da abinda Allah ya tsara domun dai a yanzu maganar da nake maka yau sati biyu kenan da daurin auran Sa'ida tare da Dan uwanta Khalid."
Alhaji Nura gumi ne ya tsinke masa ya cire hularsa yana firfita da ita kamar mara hankali yace." Ya za'ayi ayi min haka? Yarinyar nan fa ni take so tayi min alkawarin komawa gidana domin ta kula min da 'ya'ya na mai zai sanya ka tilasta mata auran d'anka wannan ai rashin adalci ne."
Kawu ya dinga kallonsa yana mamakin maganarsa........Alhaji Nura ya cigaba da cewa ." Wannan yaron naka mara kunya kwata-kwata bai dace da kamilar mace irin Sa'ida ba saboda haka duk yanda zanyi sai nayi na ruguza auran da kuka daura."
Kawu na 'kokarin magana Muryarsa ta bayyana a gurin ya jima da zuwa gurin basu sani ba......."Kai wane irin wawan mutum ne bagidaje mara hankali da nutsuwa."
Gabadaya suka juya da sauri suna kallonsa.
Rai a masifar 'bace yace." Ka jima kana kira na da mara tarbiya shin kai d'in menene sunanka? Kana gadara da dukiya ko? to inaso na sanar maka da cewa a yanzu idan nayi Ra'ayi ba zaka koma gidan ka ba zan sa a daure min kai har karshen rayuwarka."
Kawu ya daga masa hannu da fadin."Ya isa haka kowa ya bawa zuciyarsa hakuri.'' Khalid shuru yayi sai wani irin huci yake yana jin kamar ya shaqe wuyan Alhaji Nuran ya had'a masa jini da majina bai ta'ba ganin mutum mai mugun naci kamarsa ba.
Kawu ya kalleshi da fadin." Alhaji idan rai ya 'baci ba'a sauran yanke hukunci ya kamata kayi mana uziri sannan kuma ka dauki kaddara komai kaga ka samu a duniya dama rabonka ne idan kaga baka samu abu ba to dama baka da rabo saboda haka sai kayi hakuri ka barwa Allah al'amarinsa.
Gumin goshinsa ya goge rai a bace yasa hularsa ya bude motarsa da karfi yaja Kawu yayi saurin matsawa yana kallon ikon Allah sai da ya bar gurin ya juyo yana kallon yaron nasa yana tsaye bakin kishi ya cika masa rai idanuwansa sunyi jajawur.
Yace." Yau shigowar dare kayi kenan."? ajiyar zuciya ya sauke yace."Eh kasa hakuri nayi sai da safe ina so naga Gwaggo ne." Yace." To babu laifi nima yanzu nan na fito daga gurin nata. Yana kokarin shiga kofar yace."Bari a gurguje na shiga mu gaisa Allah yasa ba tayi bacci ba." Kawu yace." Bana tsammanin hakan."
Gwaggo na gyangyad'i ya shiga ya sameta, kamshin turaransa taji da sauri ta bude idonta tana kiran sunansa.
Kusa da ita ya zauna yana gaisheta ta amsa cikin kulawa tace."Kwana uku ina lissafe baka zo inda muke ba."
Yace."Nayi tafiya ne Kuyi hakuri yanzu dawowata kenan na kasa hakuri na shigo na duba ku." Tace."Jarumi za kayi tafiya amma babu labari ko baka bukatar adduarmu."?
Yace." Gwaggo kuyi hakuri nayi laifi tafiyarce babu tsammani ina fatan na sameku lafiya." Tace."Lafiya kalau alhamdulillhi Ya iyalin naka."?
Yace." Duk suna nan kalau." Tace." To masha Allah sai ka tashi ka tafi gurinsu su ganka kada ka shiga hakkinsu."
Yace." Tom ki bani abinci naci." Girgiza kanta tayi tace."Aa babu ruwana ba zan baka abinci ba mai girki taji haushina.
Yar dariya yayi yace." Gwaggo bana sha'awar komai sai abincin ki kawai ki bani idan da akwai."
Jim tayi tana nazari tace." Bari na baka kadan idan kaje gida sai ka 'kara wani."
Yace." To ki had'a min bari na shiga gurin Ummatu mu gaisa na fito." Tace." Tom shikkenan sai ki fito.
Da 'Kyar Gwaggo ta kore shi ya tafi dan bayan ya gama cin abincin kwanciya yayi kusa da ita tana bashi labarai sai dariya yake kyalkyalawa ganin dare yayi beda niyyar tafiya gida yasa tace ita kwanciya za tayi ya tashi ya tafi gurin iyalinsa da kyar ya tashi ya tafi cike da 'kaunarta a cikin ransa.
Sai da ya fara duba Jamila tukkuna ya nufi Gurin ta.
Duk da nasan yau zai dawo gida Ban yi tsammanin zai shigo inda nake ba wannan dalilin yasa ban zauna zaman jiransa ba na shige daki nayi kwanciyata.
Maganarsa kawai naji a kaina, da sauri na bude idona ina kallonsa, ganin fuskarsa a murtuke yasa gabana faduwa ni kam Allah yana jarrabata da masifaffun maza.
Zaune na mike a sanyaye nace." Khalid ka dawo ashe."? a dakile yace." Na dawo ina fatan kuna lafiya."? Nace." Lafiya kalau Ya hanya."? shuru yayi min kawai ya zuba min ido." Nace." Kana bukatar wanka na had'a maka ruwa."?
"A'a idan ina bukata zan shiga na had'a da kaina yanzu inaso nayi magana dake ne." Yanda yake magana a harzu'ke yasa na gane cewa lallai da tashin hankali ya shigo gidan.
*Kika karanta baki biya ina bin ki bashi.....Vip group #600...Normal...#400 Account... 0542382124....Binta umar gtbank.....Idan kati zaki turo sai kiyi min magana ta WhatsApp da wannan number.*
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE**103*
A nutse nace."To Allah yasa alkairi ne ina sauraranka." Cikin sigar tuhuma yace."Har yanzu akwai sauran alaqa a tsakanin ki da Alhaji Nura ko."? Gabana yayi wani irin fad'uwa! Ido na tsira masa raina idan yayi dubu ya 'baci nace."Khalid wace irin magana ce wannan."?
Hannu ya d'aga min "Kinga tambayarki nayi yana da kyau ki bani amsa ba ki tambaye ni ba." Ajiyar zuciya na sauke tare da bawa zuciyata hakuri nace."Tunda nayi aure alaqa ta yanke a tsakanimu.''
"To mai yasa yake bibiyarki har yanzu."? Kallonsa nayi duk ya tsareni da ido Nace." A'ina zan ganshi da har zai bini."
Tsaki yaja cikin tsananin kishi yace."Yau yaje can Mandawari ya samu Kawu yana cin mutuncinsa har da fad'in ba ayi masa adalci ba kin san Allah wannan mutumin yana cin darajar abu guda ne da ba don haka ba da tuni na dauki mataki mai tsauri a kansa sabida haka ki fad'a masa cewa komai maitar sa dole ya hakura dake idan kuma yaqi zai k'are rayuwarsa a prison."
"Ka daina wannan maganar Khalid yanzu ni a ina zan sameshi har na fad'a masa sa'kon ka a kansa don Allah ka rage kishi ba abune mai kyau ba.''
" Wannan abun da nake ba kishi bane gyara ne na lura dake dashi baku da Ilimin addini ba kusan menene hakkin aure ba shiyasa kuke abinda kuka ga dama to ke d'in ma tsatstsauran mataki zan dauka a kanki mutukar baki daidaita sahun ki ba."
"Khalid ni kake kira da suna jahila har kana fadin ban san hakkin aure ba har yaushe aka haife ka? yaushe kazo duniyar da zaka dinga yi wa mutune rashin kunya ko ka manta cewa a gabana aka haife k..........Kafin ta 'kara maganar ya kifa mata lafiyayyan mari! yana wani irin huci yace." Kada ki kuskura kice zaki min wannan haukan! ranki ne zai 'baci wallahi ina ruwana da wani shekarun ki duk girman ki a k'arkashina kike dole kibi umarnina idan ba haka ba ki fuskanci bacin raina."
Yana gama maganar ya bar gurin yana numfarfashi na bacin rai.
Hannu dafe da fuska na bishi da kallo har ya bude kofar toilet din ya shige.
Wasu hawaye masu tsananin zafi ne suka tsinke min wai yau yaron nan ni yake mari ikon Allah! wani abu mai nauyi ne yazo ya tsaya min a makogwaro shin wai menene mafita? ta yaya zan daidaita alaka ta dashi wai shin gabad'aya haka halin maza yake? babu shakka idan duk haka halinsu yake dole aure ya dinga saurin mutuwa babu uziri a cikin al'amuransu duk mazan data aura hakan suke da irin wannan halin.
Ina jin motsin fitowarsa nayi saurin Kwanciya ido na rintse ina nanata kalmar innalillahi wa'ina ilahi raji'un a cikin zuciyata.......Ina jinsa ya gama shirye-shiryen sa yazo ya kwanta gefe na amma ko da wasa baiyi kuskuran ta'ba wani sashe na jiki na ba......Cikin mintinan da basu wuce goma ba naji saukar numfashinsa bacci har ya daukeshi, ajiyar zuciya na sauke a hankali na lalla'ba na sauka daga gadon toilet na nufa domin daura alwala Nafila zanyi domin na kaiwa Allah kuka na.''
Alhaji Nura kuwa tsabar tension ya sanya sitiyarin mota ya k'wace daga hannunsa a take motar ta dinga walagigi a kan titi abinka da daran sanyi sahun mutane ya dauke sai jefi-jefi Cikin tashin hankali ya dinga kokarin kashe motar domin ta tsaya abun yaci tura sai kawai ya shiga kalmar shahada Mussaman daya hango wata katuwar akori kura cike da katako tayo kansa. hannu na karkarwa ya fara kokarin bude motar domun ya fita daga ciki sai kawai yaji motar ta hantsila dashi 'kasa......"Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un." A take motar tashi ta fara hayaki wuta na kokarin tashi, hayaniyar jama'a ya dinga ji sama-sama a kunnenshi ya dinga kiran sunan Allah yana kalmar shahada wutar ce ta tashi a daidai lokacin da jama'a ke kokarin taimakon sa ganin haka yasa kowa ya watse daga gurin wuta ta tashi a motarsa da motar katakon da suka had'u. da kyar 'yan a gaji suka samu nasarar kashe wutar gurin ya turnuke da haya'ki Alhaji Nura k'urmus aka fito dashi duk wani mai imani idan ya ganshi sai ya zubar da hawaye Allah sarki duniya ashe dama Alhaji Nura daf yake da barin duniya babu wanda ya san gaibu sai Allah....Labarin mutuwarsa ya zagaye garin Kano saboda shi din sanannan mutum wanda duk mutumin da yake shiga kasuwar Kwari ya san da zaman shi Abokan kasuwancin sa suka shiga alhini da damuwa.
Gwaggo kuwa kuka ta dinga yi tana fad'in "Allah Sarki Alhaji Nura Allah ya jikan ka mutumin arziki babu kai babu shiga wutar jahannama Allah ya jikan ka ya kar'bi shahadar ka." Rigima tasa akan lallai sai Kawu ya shirya ya kaita gidan mutuwar domin ayi jana'iza da ita.
Kawu da yake shima a cikin alhini yake bai mata gardama ba ta shirya ya d'auketa a motarsa domin zuwa gidan jana'izar DUNIYA KENAN ALLAH KASA MU CIKA DA KYAU DA IMANI.
Koda Khalid yazo gidan Ummatu ke sheda masa mutuwar jikinsa ne yayi sanyi damuwa da nadama suka baibayeshi ashe ma dik wannan hargitsin mutumin saura kad'an ya mutu kai gaskiya al'amarin ya girgiza shi mutuka, adduar samun rahamar Allah yayi masa yayi mata sallama domin tafiya harkokinsa.
To koda ya dawo da daddara kasa fad'a mata mutuwar yayi ya dai sassauta fuskarsa Sa'i da lokaci kuma yana satar kallonta da tunanin yanda zaiyi ya fad'a mata mutuwar mutumin.
Washe gari da safe yana shiryawa na shiga dakin cikin rashin kuzari nace." Amma Zaka tsaya kayi break fast ko."? Ya kalleta da fadin." Ba zanci abu mai nauyi ba don bana so jikina ya mutu za muyi wasa da abokaina sai dai idan na dawo.
Nace."Ai ko tea kasha ka gasa cikin ka ko." Yace." To shikkenan muje ki had'a min.'' Gaba nayi ya biyo bayana, tea din na had'a masa ya dauka yana sha yana kallona ni kam gabad'aya jikina a mace yake na rasa abinda yake damuna.
"Kina da labarin mutuwar.....Kasa 'karasawa yayi kawai ya zuba min ido.
Cikin fad'uwar gaba nace." Mutuwa waye ya mutu."?
Sunkuyar da kansa yayi