Showing 18001 words to 21000 words out of 185789 words
fad'a miki ki daina yarda da surutan mutane akan yarinyar nan shi aure lokaci ne dashi idan lokacinta yayi za tayi aure amma dan Allah ki daina d'ora mata lalura yanzu ina amfanin abinda kikayi Gwaggo da sassafe kin bunka a haya'ki a gida kin firgita yarinya tunda tace bata so ba sai ki k'yaleta ba."
"Kai Ibrahim ba fa zanyi asarar kudina ba dole sai nayi haya'kin nan tunda d'akina ne kuma idan ba aljanun ne da ita ba me yasa take guduwa mu da muke shak'ar haya'kin me yayi mana saboda haka ba zan fasa abinda nayi niyya ba idan tana da inda za taje ta tafi."
Khalid ya fito daga dakin fuska a murtuke yace."Gwaggo ina haya'kin naga irinsa." Kallonsa tayi lokaci guda ta fahimci abinda yake da akwai tace." Babu sauransa kenan nasa a wuta."
Kawu Iro yace."Gwaggo jiya ma fa haka kika ce sai gashi kuma yau da safe kin kuma kunnawa." Kuka ta fashe dashi tace."Yanzu dai kunyi min taron dangi kenan kuna kokarin 'karyata ni ko."?
Kawu Iro hankalinsa ya tashi ya dinga rarrashinta tace."Oh!oh! Ibrahim ai 'yar d'an uwanka ta fini a gurinka tunda gashinan a kanta kana nema ka 'kure ni."
Yace."Aa Gwaggo wallahi ba haka bane ina ni ina 'kure ki nayi laifi ki yafe mun." Ba tare da tace komai ba ta shiga dakinta ta bar mu a tsaye.
Kallonsa nayi naga duk hankalinsa ya tashi nace."Kawu ka kwantar da hankalin ka insha Allahu zan cigaba da hakuri da halinta." Yace."Yawwa Sa'ida dama abinda nake so kenan naji daga gurinki kiyi ta addua kinji ko komai mai wuce wa ne." Cikin dauriya nace."To Kawu nagode." Gurinsu ya nufa ya barmu nida Khalid a tsaye.....Yace."Aunty Sa'ida kada ki damu duk inda ta 'boye haya'kin zan bincika a dakin."
Nace."Khalid kyaleta dakinta ne fa tayi duk abinda take so da abunta." "Eh d'akina ne Sa'ida idan kinyi zuciya kada ki sake shigowa." Tana daga cikin dakin take magana.
Yace."Gwaggo wace irin magana ce wannan."?
"Haba Jarumi ai dole raina ya 'baci akan al'amarin nan ranar da naje 'karbo maganin nan sai da na yini banci ba bansha ba salloli na ma sai had'asu nayi amma saboda wukalancin Sa'ida ta dinga kokarin watsa min 'kasa a ido.
Yace." To wai waye ya saki ne? sai fa da nace dake kada kije okey to zanje har gidan ita Uwalen da take janki yawon gurin masu magani na gargad'eta akan hakan ni idan kinyi min baki ba zai kamani ba tunda dai ni ba Baba Iro ba ne."
Kuka tasa daga cikin dakin take fad'in "Khalid kada kaje kaci mutuncin Uwale bata cancanci hakaba." Ya d'aga labulan d'akin da fad'in."To idan bakya so naje gidan Uwale dauko min haya'kin."
Tace."Shigo ka kar'ba." da sauri ya shiga dakin nima naji wani sanyi a cikin raina.......Wani tsohon magani ta d'auko masa a 'karkashin gadonta a daure a wata tsuhowar leda ta mika masa da fad'in"Gashinan wannan jaraba ta isheni haka."
Kar'ba yayi ba tare da ya tanka mata ba ya fito daga dakin.
Yana fitowa yace." Ki kwantar da hankalinki ga maganin nan a hannuna zan fita dashi na zubar."
Hannunsa na kalla a take na gane ba maganin bane domin wancan a k'ulle yake b'akar leda wannan kuwa ledarsa yaluwa ce.....girgiza kaina kawai nayi na wuce na barshi a gurin, dakin na shiga na sameta tana murd'a redion ta ta dago kanta ta kalleni ta dauke kai tana cigaba da abinda take......gurin dana kwanta na nufa na dauki wayata na nemi gefan gado na zauna wayar na kunna na fara dube dube a ciki.......Ummatu ce ta shigo da jug d'in kunu da mai daidaiciyar silba da 'kosai a ciki.
Abin mamaki cikin mutuncin Gwaggo ta kar'ba "Sannu 'yar albarka ai Ibrahim yayi sa'ar mata Rabi wallahi ina jin dadin zama dake sabida kina mutunta ni Allah yayi miki albarka."
Ita kanta Ummatu sai da tayi mamaki da yake tasan halin Gwaggo sai tayi dariya kawai ta girgiza kanta ta fita daga dakin....Nima dana san dani take ban tanka mata ba na cigaba da duba text d'in da Alhaji Nura ya turo ina mamakin al'amarin.....Kiran wayarsa ne ya katseni da sauri na d'aga nasa a kunnena.
Yanda ya amsa gaisuwata yasa naji jikina yayi sanyi nace."Alhaji naga text dinka amma kuma ban fahimci abinda kake nufi ba."
A d'an fusace! yace."Sa'ida kada ki mayar dani 'karamin yaro mana, jiya kin turo min text din daya hanani bacci amma yanzu kina wata magana."
A nutse nace."Alhaji kayi hakuri kayi min bayanin da zan fahimta na dai ga text d'inka amma ban mayar maka da replay ba."
Ajiyar zuciya ya sauke yace."Haba Sa'ida kada kiyi wasa da hankalina mana, nifa ba yaro bane ballanatana kizo min da wasa da gaske nake auranki zanyi amma me yasa kin san akwai al'kawarin aure a tsakaninki da yaron nan Khalid kikayi wasa da hankalina."
Jikina yayi sanyi nace."Wace irin magana ce wannan waye kuma Khalid."? Lokacin da nayi maganar tayi daidai da lokacin daya shigo dakin shida Gwaggon suka zuba min ido....na cigaba da cewa."Alhaji ina tambayarka kayi shuru waye Khalid da har kake wata magana akansa yanzu a duniya na rasa mijin aure sai Khalid dan Allah ka daina wannan maganar sannan kuma text d'in daka gani mybe shine ya dauki wayata a bayan idona ya turo maka amma ni da hannuna wallahi ban tura maka wani text ba."
Ajiyar zuciya ya sauke yace."Okey to har naji dadi a cikin zuciyata yanzu a'ina maganarmu ta kwana."? nace."Insha Allahu yau ko gobe zan yanke shawara.'' Yace."Haba Sa'ida wace irin shawara ce wannan da har yanzu ba'ai yanke ba."?
Nace."Alhaji ka 'kara hakuri dan Allah." Yace."Shikkenan tom ina sauraranki." Sallama mukayi na kashe wayata rai a 'bace na kalleshi yana tsaye idonsa ya kad'a yayi jajazur!! sai wani irin kallo yake min.
"Khalid waye ya baka izinin d'aukar min waya."? Kai tsaye yace." Ni ne na bawa kaina izini ko kina da abinda zakiyi ne."? Cike da mamaki! nake kallonsa.
Ya zare min manyan idonsa da suka rine da 'bacin rai da 'bakin kishi yace."Ni kike ciwa fuska ko."? Nace."Meye abin cin fuska sarkin tsaurin ido ina kai ina Alhaji Nura da har zaka dauki wayata ka rubuta masa text kasan dai ya kusa haifarka ko."?
Yana 'kokarin magana Gwaggo tace."To daya kusa haifarsa mai zai nuna masa? namiji yake shima namiji yake sannan duk abinda yake dashi shima yana dashi sai me kuma."?
Kallonta nayi tace."Mara mutunci wacce bata san mai sonta ba, dame Alhaji Nuran yafi Khalid da har zaki dinga ci masa fuska."
Nace."Kinga Gwaggo ki cire kanki daga cikin wannan maganarki babu ruwanki ni babu wanda ya isa yayi min dole a gidan nan wanda nake so zan aura bana auran 'karamin yaro a kyaleni."
Gwaggo ta fashe da kuka had'e da fad'in "Zagi na Zakiyi ne naga kina zaburowa ko kuma dukana zakiyi butulu kawai."
Hawaye suka shararo min nace."Me nayi na butulci kuma? ina zaune a gado na mahaifina ina ciyar da kaina sai me? me nayi na butulci da har kike kirana da kalmar."
Jikinta ne kuma yayi sanyi ganin ina kuka.....Girgiza kansa yayi ya fita daga d'akin zuciyarsa kamar ta babbake saboda 'bacin rai.
Bayan fitarsa na share hawaye mi'kewa nayi na fara had'a kayan wanki, sai naga tana satar kallona cigaba nayi da abinda nake tace."Sa'ida kinga yau 'kosan yayi kyau gashi da zafinsa ki zuba kunun kisha sai kiyi wanki."
Nace."Aa Gwaggo ba zan sha kunu ba kisha kawai.'' Shuru tai tana kallona tsaf na gama had'a wankin na fita dashi can bakin rijiya na zubesu komawa dakin nayi na dauko indomee biyu 'karamin gas d'ina na kunna na d'ora tukunya da ruwa akai na zuba indomee a ciki.....ina zaune a gurin ta dahu na juye a plate kana na kashe gas d'in. Nan tsakar gidan na zauna a nutse naci na fara ci ina Nazarin rayuwa wai ni Gwaggo take kira da Butulu hummm! rayuwa kenan.
*Masoya a taimaka da sharing????*
*IDAN KINA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE.....VIP GRUOP#600 NORMAL GROUP #300 ACCOUNT... 0542382124.....BINTA UMAR GTBANK....IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER*
*07084653262*
*08089965176*
*BINTA UMAR ABBALE*
*GA IRINTA NAN!!!?????¡â?*
_(LOVE STORY??)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE??_
*MANAZARTA WRITES ASSO?????*
*11*
Ina zaune da plate din indomee a gabana ya shigo gidan, kallo guda nayi masa na kauda kaina, gani nayi ya tsaya yana kallon kayan wanki na dana jibge a bakin rijiya, minti biyu ya wuce daga gurin..... mikewa na share tsakar gidan sannan na shiga dakin na harhad'o kayan wanke-wanke na fito dashi bakin rija. d'akin na koma na sameta ta fara kad'in lagwani nace." Gwaggo zan fara wanki inaso na share miki dakin." Tace."Kije kiyi wankin ki idan na tashi na share." Ba tare da nace mata komai ba na fita daga dakin, samun sa nayi zaune a bakin rijiya daga shi sai gajeran wando yana wanke kayan ball d'insa.
Tsigar jikina ta tashi na tsani na ganshi babu suttura a jikinsa nakan ji wani irin yanayi a tare dani, kamar na koma d'aki na zauna idan ya gama abinda yake nazo nayi wankin, sai dai na daure kawai naja bokiti da ruwa a ciki na zuba omo na sunkuya na fara cud'a wankin....Shuru gurin yayi yana ta cud'a kayansa nima ina cud'a nawa.
Sunkuyo na d'an gyara karaf! na kama shi yana satar kallon kirjina. cikin dubara na duba sai naga ashe gurin sunkuyo din wuyan rigata ya zame gabad'aya breast dina ana ganinsu.
Girgiza kaina kawai nayi na mi'ke. kujera 'yar tsuguno naje na dauko na zauna akai na cigaba da abinda nake........ Hannunsa ya mi'ka ya d'auki briziyata yasa a cikin ruwan omon dake gabansa ya fara cud'awa.
Rai a 'bace! na kalleshi da fad'in "Ranka zai 'baci idan baka mi'ko min rigar nan ba."
Uffan bai ce min ba ya cigaba da cud'a breziyar yana gyarata, Nace."Khalid ko bakyaji abinda nace ba."? Babu walwala a tare dashi yace."Naji ashe akwai sauran wani abu da zakiyi min bayan wanda kikayi min d'azu."
A zafafe! Nace."Nayi maka d'in ai kai ka janyo meye ruwanka da wayata ko kuma Alhaji Nuran sa'anka ne wallahi ka nutsu ka shiga hankalinka idan ba hakaba kana tare da 'bacin rai."
Cike da nuna rashin damuwa yace."Mutukar akanki ne a shirye nake da kowane irin 'bacin rai kuma wallahi sai inda karfina ya 'kare zaki gane baki da wayo."
Da sauri nace." Ni kake fad'awa wannan maganar."? Shiru yayi ya cigaba da abinda yake a fusace! na kai hannu zan fuzge rigar ya murd'e min hannu har sai da yayi 'kas! cike da mamaki nake kallonsa! Yace."Ki kyaleni na cigaba da wankewa hakan na rage min rad'ad'i!
Gabana ya fad'i! wanke breziyya har wani jin dad'i ne lallai Khalid fitinanne ne........Kallona yayi da wani munafikin murmushi a fuskarsa yace."Naga kamar ma tayi miki kad'an idan na tashi had'a miki lefe wacce ta fita girma zan sa miki."
Naji wani irin takaici ya rufe ni wai ni ya zanyi da yaron nan ne? shamtarsa nayi na zubar da ruwan oman dake gabansa.
Sai yayi murmushi ya cire breziyar a cikin bokitin kawai naga yana marmatsa 'ko'konta kamar yana ta'ba nono sai lumshe ido yake yana cizar lips d'insa....Ruwan Oman dake gabana na d'aga na kwara masa a jikinsa, hakan yayi daidai da fitowar Ummatu daga gurinta, ya mi'ke tsaye da breziyyar a hannunsa.....Ganin mahaifiyarsa yasa yayi saurin mayar da fuskarsa ta salihai "Aunty Sa'ida me nai miki kika watsa min ruwan wanki."
Shuru nayi jikina yayi sanyi da irin kallon banzan da mahaifiyarsa keyi min....ta kalleshi rai a 'bace tace."Khalid meye wannan a hannunka."? da sauri ya kalli hannunsa sai kuma ya jefo min breziyyar da fad'in."Ummatu ban san na rike ba mybe a cikin ruwan wanki data watsa min ta had'o da ita."
Ta kalleni da rai a 'bace "Sa'ida wane tsabar rashin mutunci ne wannan? me yayi miki dan wulakanci zaki watsa masa ruwan wanki a jiki."
Shuru nai mata ba wai dan bani da amsar da zan bata ba sai dan sanin da nayi cewa duk abinda zan fad'a mata yayi min ba yarda za tayi ba.
Gwaggo ta fito daga dakin tana fad'in "Me kuma yake faruwa nake jin hayaniya."? Ummatu da sauri tace." Gwaggo duba jikin Khalid ki gani sabida tsabar ita ta cika ishashshiya ta dauki ruwan wankinta ta watsa masa a jikinsa.
Gwaggo da sauri ta kalli Khalid jikinsa jagab! da ruwan daud'a! cike da mamaki! tace."Jarumi me ya had'a ku nasan dai ruwa baya tsami banza."?
Girgiza kansa yayi yace.''Gwaggo daka kawai zan taimaka mata da wanki shine tayi min wannan wulakancin.''
Tace."Haba Sa'ida me yasa kika aikata haka."? Rai a 'bace na d'ago ina kallonsu nace." Lokacib dana fito da wanki na bance kowa ya taimaka min ba akan me zai zo yasa min hannu sai kace sa'arsa dan wulakaci ya d'auki breziyata yace zai wanke."
Gwaggo ta ri'ke bakinta tana yi masa wani irin kallo mai kama da harara.....Ummatu tace"Ke Sa'ida kada kiyi masa sharri yaushe ya dauki rigar nonan naki bayan ke kika watsa masa ruwan daud'a da ita a ciki."
Nace."Ummatu kenan ba sharri nai masa ba da idonki fa kin gani amma zaki ce nai masa sharri."
Gwaggo tace."To duk dai magana ta wuce kada a 'kara tayar da ita kai kuma Khalid babu ruwanka da ita." Yace."Yanzu ke Gwaggo kin yarda zan aikata hakan? okey idan ma breziyar ta na d'auka domin na wanke mata meye a ciki? ai ba k'irjinta na ta'ba ba ballantana tayi min sharri ." Gwaggo tace."Aikuwa dai babu laifi a ciki tunda tace bata so sai ka kyaleta.
Tsaki yaja ya bar gurin yana fad'in "Daga Abin alkairi sharri ya biyo baya wataran ma cewa zakiyi na turmushe ki." Ummatu tayi saurin fad'in "Allah ya kiyaye." Bayansa tabi tana surutai itama Gwaggo dakinta ta koma ta cigaba da abinda take.
Tana zaune a d'an tsakar gidanta ya fito daga dakinsa cikin shirin fita yayi gayu cikin 'kananun kaya sai kamshin turare yake, Khalid akwai tsabta da kwalisa kayansa kullum a goge gashi bai yarda da fesa turare me arha ba.
"Khalid zo nan ina so nai magana da kai." A nutse yaje ya samu gefanta ya zauna. tace." Kana jina ko."? yace."Eh Umma ina jinki." Tace."Ni ba zan raba ka da 'yar uwarka Sa'ida ba amma inaso kayi nesa da ita dan gabad'aya ni yarinyar bata kwanta min a raina ba ina jin tsoro taje tayi lalata a waje ta laqaba maka sharri ka daina shiga sabgarta."
A sanyaye yace."Ummatu me yasa kike mata irin wannan zargin." ? Tace."Kai Khalid yaro ne kai baka san me duniya take ciki ba gabad'aya jama'ar gari kallon lalatacciya suke mata dan ni akwai wacce ta kawo min magana kancewa babu irin lalatar da ba tayi da maza a gurin aikinta wannan dalilin yasa nace kayi nesa da ita bana so taje tayo cikin shege ta d'ora maka."
Cike da mamaki! yake kallonta kafin yace."Ummatu amma banji dadin wannan magana ba dan Allah ki daina yarda da surutan mutane bana tsammanin Aunty Sa'ida zata zubar da martabar gidan nan."
Tace."Oho! dai Sa'ida tana bin maza bata bin maza ni dai nace ka rabu da ita dan naga kaima tana so taja hankali ka gashinan baka san laifinta.''
Shuru yayi yana girgiza kansa! Tace."Yaushe ne zaku koma makaranta."? Yace."Ai kin san da tuni mun koma wannan yajin aikin da aka tafi ne ya janyo amma naji gwamnati tayi magana cewa kowane dalibi ya koma makaranta ranar mondy."
Tace."Jibi kenan zaka tafi."? Yace."Eh insha Allahu." Tace."To shikkenan kafin ka tafi kaje can babban gida ka gaishe su." Yana kokarin mi'kewa yace "To insha Allahu zanje."
'Kamshin turaransa ne yasa nayi saurin juyowa muka had'a ido dashi, saurin dauke kaina nayi ina mamakin a'inda ya samu kudi ya siyi turare mai tsada irin wannan nafi jin 'kamshinsa a jikin Alhaji Nura. Cigaba da shanya kayana nayi har ya fice daga gidan sai kawai na tsinci kaina da bin bayansa da kallo gaskiya dressing din yayi masa kyau sosai. kawar da tunaninsa nayi daga cikin raina na cigaba da abinda yake gabana.
Ina tsaka da share inda nayi wanki yaro ya shigo."Wai Salisu mai kanti yace a bashi lagwanin." Nace."Shiga dakin ka fad'a mata. muryarta naji tana fad'in "Bama sai ya shigo ba naji bari na kawo maka ka kai masa."
Yaron yace."To gwaggo." ta fito hannunta rike da leda viva ta mika masa da fadin"Kace dan Allah yayi hakuri banyi masa akan lokaci ba." Yace."To Gwaggo zan fada masa."
Fita yaron yayi ta kalleni da fadin"Sa'ida yau sha'awar sakwara nake ko zakiyi mana da ragowar doyar can." Nace."Banda kudi da zan sarrafa.''
Tace." 'Dari biyu zata isa ayi miyar."? Kaina na girgiza mata alamun ba zata isa ba, tace."Aikuwa dari biyu zan iya bayarwa ayi cefane." tafada tana kokarin shiga daki sallamar Almajirin gidan Alhaji Nura ta dakatar da ita.
Washe bakinta tayi tana kallonsa ya 'karaso inda nake hannunsa ri'ke da ledoji yace."Aunty Sa'ida ina wuni."? na amsa ina kokarin wanke hannuna yace."Daga kasuwa nake Alhaji yace na kawo miki wannan." Hannu nasa na kar'bi ledojin da fadin."To Rabi'u kace masa nagode sosai." Ya amsa da ameen tare da juyawa Gwaggo tace." Rabi'u babu gaisuwa ka shigo kawai ka wuce gurin uwar dakinka."Murmushi yayi yana kallonta yace."Gwaggo Dan Allah kiyi hakuri wallahi hankalina ne yayi gaba ina