Showing 54001 words to 57000 words out of 185789 words

Chapter 19 - Ga-irin-ta-nan-complete by binta umar abale

05 Jul 2024

24177

da kyakykyawan fata."


Ummatu tace."To shikkenan Gwaggo insha Allahu zan cigaba dayi masa addua.

Tace."Bari na tsaya na tafi da kunun tunda naga kin gama damawa." Ummatu tace."Aa Gwaggo kije kawai zan kawo muku." Gwaggo 'kin tafiya tayi har sai da Ummatu ta zuba musu kunun a jug ta zuba musu awara mai yawa a silba Gwaggo ta dinga shi mata albarka kamar basu ta'ba samun sa'bani da juna ba Ummatu ta dinga mamakin al'amarin domin tunda suke da Gwaggon bata ta'ba kwantar mata da kai irin yau ba gashi har da ya sanya mata albarka gaskiya dole al'amarin ya bata mamaki.


'Dakin ta shigo ta same ni na gama shiryawa tace."Sa'ida ga kunu nan da zafin sa ki zauna kisha kafin ki tafi.''


Da mamaki! a tare dani nake kallonta kafin nace."Yau da kanki kika kar'bo kunun."? Tace."Eh gani nayi ta gama damawa shiyasa na tsaya na tawo dashi.

Shuru nayi na samu cup na tsiyayi kad'an a warar ma uku na dauka na zauna ina kur'ba, tace"Ki sake kiran wayar tasa mana.

Ba tare dana ce komai ba na dauki wayar na shiga duba number tashi....Kamar dazu wayar ta katse ta'ki shiga.

Nace."Gwaggo sai dai kiyi hakuri fa domin wayar nan ta'ki shiga.kallona take nace." Dan Allah ki daina wannan kukan Gwaggo mutuwa dai ake Jin tsoro idan Kwanan sa ne ya 'kare Allah ya jikansa.


Tace."Sa'ida amma baki da tausayi da imani yanzu sai kiso Khalid ya mutu a wani guri ai idan ma lokacinsa ne yazo nafi bukatar ya mutu a gabana hankali na sai yafi kwanciya idan naga gawarsa.

Nace."Yanzu ma idan mutuwar yayi kina zaune labari zai same ki kuma za'a kawo miki gawar sa har gida.

Ta dinga kuka tana watsa min harara, dariya na kunshe a gurguje na gama abinda nake nayi mata sallama uffan ba tace min ba har na fita daga gidan.


Sai da gari ya waye tukkuna suka samu damar komawa cikin motar kowa ya zauna a gurin zamansa jikinsu duk yayi sanyi da irin 'barnar da 'yan fashi sukayi musu Khalid baiji takaici sosai ba saboda yasan ya tsira da sim card dinsa da 'yan tufafinsa amma duk guzurin kudin da Sukayi shi da Salmanu 'Yan fashin nan sun hargitsa musu kaya sun kwashe a yanzu ko sun sauka a garin na legos sai Sunyi fafutuka tukkuna.


Motar tayi shuru kowa na sake-sake a cikin ransa yayin da direben ke ta sharara guda akan kwalta, tun kafin su karasa inda matar take kwance a gefen titi Mijin nata yake ihu! da fadin"Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un gatacan a kwance sun kasheta.''


Direban suna karasawa inda take ya fara kokarin parking ko kafin ya 'karasa mutumin ya fit ya fito a take ya gangara k'asan wani rami mai Mugun zurfi! gaske.


Hankalin su Khalid ya tashi mutuka hakika tunda yake bai ta'ba ganin masifa da tashin hankali irin na yau ba wannan mugun ramin da mutumin ya fad'a ciki ai sai dai wani kuma, wasu suka nufi inda matar take kwance wasu kuma Sukayi dafifi! a bakin ramin da mutumin ke ciki sai salati suke suna tunanin ita ina zasu taimakeshi.


Khalid yayi masifar tsorata da ganin matar da babu rai a tare da ita har ta fara kumbura ga jini duk ya bushe a jikinta kud'aje da 'kwarika sai bin jikinta sukeyi.......Yarinyar ta na gani uwarta sai ta tsandara ihu!! ta shiga tsakanin mutanan tana so taje inda take...Khalid yayi gaggawar daukarta yana rarrashin ta hawayen tausayi na nema ya kufce masa..


Da yake sun shiga cikin gari yasa basu sha wata wahala ba mazauna gurin suka kawo musu dauki 'yan agaji suka shiga cikin ramin suka fito da mutumin a mace duk ya karkarye, da yawa daga cikin mutanan gurin sai da suka tsorata da wannan tashin hankali masu rauni a ciki suka dinga faduwa suna suma wasu kuwa gefe suke nema su zauna suyi ta share hawaye suna kad'aita Allah shi d'aya.


Khalid wata irin nadama mai tsanani ta rufe shi ya dinga jin kamar ya juya ya koma gida ya nemi gafarar iyayensa da wacce ya zalin ta yanzu idan da 'karar kwana da tuni shima ya zama tarihi ya mutu da fushin iyaye a tare dashi.



Jakar mutumin aka duba akayi sa'ar samun wallet dinsa nan Suka shiga binkicen in da yake a jikin IDcard d'insa aka samu cikakken address dinsa da inda yake aiki. Mutumin dai dan kano ne kuma yana aiki asibitin Koroda dake karkashin gomnati. ba tare da 'bata lokaci ba jami'an tsaron dake gurin suka shiga aikinsu Gawarwakin aka d'aure suka sa a mota suka dauki hanya Khalid ya dinga jin kamar ya tsayar dasu ya bisu ya koma gida suna tsaye a gurin har motar Police din ta 'bacewa ganinsu kafin su koma cikin motar ko wanne da mataccan jiki motar tayi tsit! shima direban duk da ya saba ganin tashin hankali irin wannan amma gaskiya wannan karon ya firgita mutuka jiki a mace ya shiga ya zauna ya kunna motar suka bar gurin...





*Littafin na kudi ne....Kada ki siya ki fita dashi...idan kika ganshi a gruops kada kiyi sharing......Idan kika karanta baki biya ba na biki bashi.....Idan kina so ki biya kudin littafin ga yanda abin yake... Vip gruop#600 normal gruop#300...account.. 0542382124...Binta umar gtbank....Idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min magana ta WhatsApp da wannan numbers*
*07084653262*
*08089965176*
*BINTA UMAR ABBALE*
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha'kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.????????_*




*33&34*
Ummatu da sauri ta d'aga kaskon dake cike da wutar ta gyarashi haya'kin ya cigaba da tashi a gurin tana me cigaba da kiran sunan Khalid a bayyane .........Gwaggo ta tsorata sosai da sauri ta bar gurin tana toshe hancinta dakin ta dawo ta same ni da tissue ina goge hanci gabad'aya majina ta tsinke min wannan wace irin jaraba ce...Hannuna ta kamo muka fito daga dakin har yanzu Ummatu na tsaye akan maganin tana aiki ita kanta sauri take ta gama kiran sunan Khalid din iya adadin da aka gindaya mata .

Kofar gida muka fita muka tsaitsaya muna mayar da numfashi..Gwaggo ta kalli cikin soron gidan tasa gefen hijabinta ta goge hawayen dake sauka a fuskarta tace."Sa'ida kinga yanda haya'kin nan yake fitowa kuwa."

Soron na le'ke na gani nace."Gwaggo matsa daga gurin ki bashi hanya ya fice idan gidan ya sarara sai mu koma.

Kusa dani ta tsaya tana zazzare ido kafin tace."Sa'ida kiga jaraba mutum da gidansa an koro shi waje kai gaskiya Rabi shaid'aniya ce wallahi tana azabtar damu."

Nace."Gwaggo addua zakiyi mata Allah ya shiryeta." tace."Sa'ida idan da Rabi zata shiryu da tuntuni ta shiryu kullum fa a tafe take to daga yau ta daina fita daga gida domin zan sa Ibrahim ya gindaya mata sharad'ai."

Tana rufe bakinta Kawun ya karyo kwana nace"Alhamdulillahi gashinan ma.'' Ajiyar zuciya ta sauke dukkaninmu muka tsira masa ido har ya karaso gurin.


Hankali a tashe yace."Gwaggo lafiya na ganku da magariba a tsaye a waje."

Da sauri tace."Ibrahim ai gidan yafi karfin mu le'ka kaga abinda yake fitowa daga cikin gidan.

Le'ka kansa yayi soron ya hango haya'ki da sauri yace."Subahanallahi Gwaggo ba dai wuta ce ta tashi a gidan ba.'' Yana kokarin kutsa kansa gidan yake magana.

Gwaggo ta hana shi shiga da fadin"Oh o! ko d'aya Rabi ce take haya'ki a gidan ko na barkono ne oho! dan a jigace muka fito daga gidan.

Kawu ransa ya 'baci sosai shi kam Allah ya jarrabeshi da fitinanniyar mata kafin Gwaggo tayi aune ya fad'a cikin gidan.


Lokacin da ya shiga gidan Ummatu ta gama aikin tana sunkuye gaban kaskon wutar tana karkad'eshi duk tayi wujiga wujiga fuskarta tayi jawur! d'ago kan da za tayi sai taga mijin nata a tsaye a kanta shima hawayen haya'kin na zuba a fuskarsa Kawu Iro bai damu ba saboda yasan dole yayi hawaye saboda zafin maganin da yake fitar da haya'kin.


A sanyaye take kallonsa tana share fuska yace."Rabi wane irin haya'ki ne wannan kika turni'ke gida dashi saboda tsabar iskanci da wulakanci na dawo na tarar da mahaifiyata a waje a tsaye Rabi wai me yasa bakya ganin girman Gwaggo ne me tayi miki kika raina ta."


Ummatu kuka ta fashe dashi tace."Wallahi ni bance su fita daga gida ba da kansu suka fita dama nasan dole a k'ulla min sharri a gurinka.

Mari ya kwada mata yace."Rabi kina nufin mahaifiyata ce za tayi miki sharri.'' hannu da dafe da kumatu tace "Aa ni ba haka nake nufi ba. Yace." To wannan azababben haya'kin na magani da menene.'' ?

Tana kuka tace."Kiranye Malam ya sani nayi wa Khalid saboda d'azu da Rana Ya kira ni a waya yake sheda min cewa shida gida har abadah. shine Baito tace na tashi muje ayi mana taimako akan al'amarin shine wani malami ya had'a min wannan maganin yace nasa a wuta na tsaya a kai na kira sunan Khalid in sau dari ba d'aya."

Fuskarsa ta sanja da yanayi na 'bacin rai yace."Rabi yanzu akan yaron nan Khalid kike nema ki kauce hanya wane irin mushirikin malami ne wannan kikeje gurinsa da ya baki irin wannan hayakin."?

Tana hawaye tace." Kandala 'Kawar Baito ce ta kaimu gurinsa a can cikin k'yauyen Janguza."


A karaf a kunne gwaggo a lokacin da suke kokarin shiga gidan ita da Sa'ida.


Tace."Umhum! kaji maganar Uwale ta fito ko Ibrahim."? da sauri ya juya yana kallonta ta cigaba da cewa." Ibrahim ba zan ta'ba mantawa ba kafin ka auri Rabi babu irin abinda ba a fada maka ba a kanta da mahaifiyarta amma ka rufe ido to yanzu ai sai ka gazgata maganar mutane tunda gashinan da bakinta tana fada maka cewa ita da mahaifiyarta sukeje Janguza gurin malami.

Kawu Iro jikinsa yayi sanyi tabbas hakane babu irin shawarwarin da ba'a bashi ba akan ya hakura da Rabi ya nemi wata ya rufe idonsa a lokacin saboda masifar son da yake mata ya aureta gashinan tana azbatar masa da mahaifiyarsa.

Yace."Gwaggo dan Allah kiyi hakuri wallahi tuntuni na gazgata maganar mutane akan Rabi ba mutuniyar kirki bace."


Tace."Ai ni tuntuni magana ta wuce a gurina amma inaso na sanar da kai cewa Yau tsayin kwana biyar kenan Kullum matarka bata yini a gida haka take fita tana barin mu da yunwa ga kayan abincin Sa'ida ya kare muyi ta kame-kame! to sabida haka nake umartaka cewa ka hana ta zuwa ko'ina idan kuma ta'ki to ka gindaya mata sharadi cewa duk sanda ta sake fita a bakin auranta.


Ido jawur yake kallon Ummatu da tayi muzu-muzu a tsaye sabida tsabar zurga-zurga har ta rame yace."Rabi ina kike zuwa babu izini na sannan kuma ina kike kai kudin cefanan da nake baki a kullum."

Murya na rawa tace."Wai shin ya za'ayi na zauna a gida na kwantar da hankalina rayuwar yaro na na cikin garari ai dole naje inda za'a taimaka min."


Gwaggo tace."Shiyasa kika dauki katifar dake shimfid'e a gadon ki kika siyar saboda kiyi yawon malamai."

Da sauri Kawu Iro ya kalleta dan shi bai da labarin siyar da katifa tunda a dakinsa yake kwana sai da Ummatun ta kai kanta gurinsa.


Gwaggo tace."Eh Ibrahim maganata gaskiya ce Kwana hudu da suka wuce Rabi ta siyarwa da Lantana katifar ta.....Kawu Iro kamar yayi kuka yace."Rabi me na gaza dayi a gidana yunwa ko ishirwa."? shuru tayi tana dauke kanta

Yace." To bari kiji Rabi bani kika tozarta ba kanki kika tozarta kuma shi yaron da kike kashe kudi a kansa ko ya dawo ba zai zauna mana a gida ba sai dai ya nemi gurin zama yawon bin malamai kuma kada ki fasa kece a wahale sannan maganata ta karshe dake ita wallahi tallahi duk sanda kika sake fita daga gidan nan bada sani na ba a bakin auranki dan na gaji da wannan munanan d'abi'un naki."

Ummatu tana kuka na fitar hankali ta shige gurin....Ya juyo cikin tausasawa yake rarrashin mahaifiyartasa Gwaggo tace."Ibrahim kada ka damu kaji ko kaje kayi sallah nayi abinci kazo kaci mu tattauna muhimmiyar magana."

Yace."To shikkenan Gwaggo bari na shiga na daura alwala." tace"To babu laifi." Kawu Iro ya bude kofar gurinsu ya shiga ita kuma ta shigo dakin ta sameni a zaune a bakin tabarmar ta.

Zama tayi tana fad'in "Haba jama'a mata duk ta zame mana annoba a gida wallahi Sa'ida da Ibrahim yana da iko aure zan sa shi yayi domin kuwa sam bai dace da mace ta gari ba."


Nace."Gwaggo kema fa da laifinki kina shiga abin da babu ruwanki a gaskiyar magana Ummatu tana hakuri dake da halin ki shiyasa wani lokacin idan tana mayar miki da magana bana jin haushi sabida nasan ke kika janyo."

Tace."Sa'ida nifa ba zan ga ba daidai ba nayi shuru haka halina yake tunda can bana shuru kawai na zuba ido akan mutum yana abinda yake so ban gyara masa kuskuransa ba."


Nace."To Gwaggo kada dai kisa Kawu yayi wani aure a yanzu dan Allah ki kyaleshi yaji da d'aya idan ya 'karo aure gidan nan sansanin ya'ki zai zama gaki ke kuma a gefe kina 'kara ruru wutar al'amarin sabida haka ki kyautata zamanki da surukar ki shima Kawu Ibrahim sai yaji dadin tafiya neman sa."

Tace."To ai shikkenan Sa'ida tunda laifi na kike gani a kan na Rabi." Nace."Aa Gwaggo bance ke kadai kike da laifi kowa yana dashi."

Shuru tayi bata tanka ba ta dauki redio tana murdawa. Kawu ya shigo dakin na gaisheshi a nutse ya amsa Gwaggo ta ajiye redion a kusa da ita bayan ta kama tashar da take so.

Abincin ta zuba masa tasa masa da yawa, yaci ya koshi yasha ruwa. tace."Ka gani sai Rabi taci kayanta idan ta dafa dan Allah Ibrahim ko tayi maka tayi kada kaci ka nuna mata kuskuranta.".......kallonta nayi ina mamakin 'karfin halinta ko waye ya fad'a mata ana shiga tsakanin miji da mata oho.

Zamansa ya gyara da fad'in"Gwaggo kada ki damu ai sai na sake nuna mata kuskuranta idan na shiga gurin." Tace."Yauwa to ka tauna mata tsakuwa sosai." yace."Insha Allah Gwaggo ke nake saurare akan maganar da zamu tattauna.

Gyara zama tayi ta fuskance shi sosai tace."Ibrahim akwai wani bayani dana saurara daga Malam Aminu Daurawa inda yake cewa................Bayani tayi masa sosai kamar a gabanta malam din yayi tambihin...Kawu Iro ya dago kansa a hankali yace."Gwaggo wallahi ni kaina na sha'afa da wannan al'amari nasan tabbas hakane gaskiya malam ya fad'a akan wannan al'amarin kuma dole ne a dakata da daurin aure tukkuna aga abinda ubangiji ya lullube amma ni yanzu tunanin ta inda zan tunkari Alhaji Nura da maganar nake."

Gwaggo tace."Muma dai tun dazu muke wannan nazarin mutumin nan fa ya riga ya gama duk wani shirye-shiyen sa lokaci kawai yake jira idan anje masa da wata magana dole yayi zargin wani abu.

Kafin Kawu yace wani abu kira ya shigo waya ta Alhajin ne da sauri na fita daga dakin da wayar a kunnena.

Soro na tsaya muka gaisa kamar ko da yaushe kafin yace."Sa'ida wasu harkoki ne na kasuwanci suka taso min a yanzu dama kuma tun watanni uku da suka wuce nake tsammanin gudanar da harkokin sai yanzu Allah ya bani iko sabida haka nake baki hakuri akan abinda zakiji na fada miki a yanzu." a sanyaye nace."Haba Alhaji ai babu komai ina sauraranka.''

Yace."Yauwa 'yar albarka inaso za'a d'aga daurin auran mu sai nan da wata uku ko hudu saboda a cikin satin nan nake so na tafi chana domin company da muke harkokin mu a tare suna bukatata a kusa wannan dalilin yasa nace bari na kira ki a waya na fada miki kafin nazo.'' Ajiyar zuciya na sauke ina godewa Allah a raina babu shakka dukkanin abinda yake faruwa da ikon Allah ne.


Nace."To babu komai Alhaji kada ka damu ai kamar yau ne kaje ka dawo insha Allahu ina zaman jiranka kuma inayi maka fatan alkairi da nasara a rayuwarka."

cikin jin dadi ya amsa da ameeen Sa'ida insha Allahu a satin dana dawo za'a daura auran ki tare a dakin ki.'' mirmushi nayi nace"To Alhaji Allah ya nuna mana lafiya." Ya amsa da ameeen Gimbiya bari na barki ki huta ko insha Allahu gobe zan shigo da wuri muyi sallama."

Nace."To shikkenan sai kazo din a gaishe min da yarana." ya amsa da fadin"Zasuji da kyau insha Allah." sallama mukayi da juna na kashe wayar na koma cikin gidan.

Cikin nutsuwa na nemi guri na zauna ina kallonsu duk sun shiga yanayi na damuwa nace."Gwaggo ku kwantar da hankalin ku Allah ya kawo mana mafita domin kuwa yanzu muka gama waya da Alhaji Nuran yake sheda min cewa tafiya ta taso masa zuwa chana sabida haka za'a daga daurin aure sai bayan ya dawo wata uku zaiyi a can ko hud'u insha Allahu yace cikin satin da ya dawo sai a daura auran.

Gwaggo tace."Kai alhamdulilahi amma naji dadin wannan magana wallahi dama bayan fitar ki muna ta tararrabin yanda za'ayi a tunkareshi da maganar sai gashi cikin sauki Allah ya kawo mana mafita."

Kawu yace."amma kuma kamata yayi yazo ya same ni mu tattauna maganar a tsakaninmu.

Nace."Eh hakan yace insha Allahu gobe zai zo kuyi maganar." Gwaggo tace."To kaga shikkenan sai ka jira zuwansa kada ka fita kuma kuyi sa'bani."

Yace."Insha Allahu zan zauna nayi jiran zuwan nasa. Mi'kewa yayi da fad'in zai fita ya sha iska a waje." Gwaggo tace."Haba ai zafin ya isa muma yau kwanciyar tsakar gida zamuyi ai." Kawu yana kokarin saka takalmansa yace."Hakan yayi gwaggo ke Sa'ida sai ki fito ki dan gyara muku inda zaku kwanta din." Nace."To shikkenan." mikewa nayi na fito tsakar gidan domin na gyara mana inda zamu kwanta.


To kamar yanda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login