Showing 57001 words to 60000 words out of 185789 words

Chapter 20 - Ga-irin-ta-nan-complete by binta umar abale

05 Jul 2024

24238

dai Alhaji Nura yayi alias a run zuwa gurin Kawu su tattauna maganar haka din ne ya kasance domin Kawu a daran ranar ya kira wayar Alhaji Shamsu mijin mahaifiyata ya sheda masa dukkanin abinda yake da akwai Alhaji Shamsu yace babu damuwa insha Allahu zai fito da wuri ayi zaman dashi.

Sun tattauna abinda ya dace a tsakaninsu tinda dukkaninsu ba yara bane sun san harkokin kasuwanci mussaman Alhaji Shamsu shi ya 'kara karfafawa Alhaji Nura gwiwa akan tafiyar tasa amma kuma sai yace mai zai hana kawai a daura auran idan yaso in ya dawo sai ayi maganar tarewa.

Lokacin da yayi wannan maganar Kawu Iro hankalinsa ne ya tashi yayi shuru yana sauraran yaji amsar da zai bashi Alhaji Nuran yace yafi so ayi komai a lokacin da yake nan." Alhaji Shamsun yace to shikkenan babu damuwa Allah yasa hakan shi yafi alkairi."

Dukkaninsu suka amsa da ameen ya Allah ." suka rabu cikin mutumci da girmama junansu.


****
*Bayan sati biyu*
Khalid da Salmanu mota suka bi da kayansu da kuma guzirin su domin zuwa Lego's dan su nemi aikin yi su kuma cigaba da gudanar da harkokinsu na buga kwallo a cewarsu duk inda ta fad'i sha ne, Salmanu lafiya lau suka rabu da mahaifiyarsa da da sauran 'yan uwansa shi kuwa Khalid babu sa albarka uwa da uba ya d'auki irin wannan tafiya aikuwa cikin dare suna tsakiyar titi motarsu na sharara gudu *da'u fataken dare!* ('Yan fashi) suka tare musu mota yana ganin haka yayi saurin bude wayarsa ya cire sim card dinsa yasa a bakinsa ya danne a kasan harshen sa......'Yan fashin suka dinga sakin harbi! ta ko'ina suka sanya dik wa'inda suke motar mata da maza suka fito suka kwanta a tsakiyar titi duk motar da ta karaso gurin sai sun tsayar da ita sun fito da mutanan ciki.....Daya bayan d'aya suka dinga binsu suna kar'be musu wayoyinsu wa'inda sukayi gardama a cikinsu suyi musu dukan mutuwa ganin haka yasa mutane suka tsorata domin tsira da ransu da lafiyarsu suka dinga mika musu wayoyinsu da jakkunan kayansu da guzurinsu.

Sai da suka kwace musu komai suka loda cikin motocinsu sannan suka dawo gurin da suke kwance suna haskasu.........Babban cikinsu ya tsuguna kusa da wata mata ta rungume d'anta sai kuka take ta hada uban gumi jikinta sai karkawa yake.

Fuskarta ya haska sosai yake 'karewa jikinta kallo ya sauke ajiyar zuciya ganin akwai mamora a jikinta yasa ya kira daya daga cikin 'yan uwansa ya nuna masa ita da fad'in "Zamuje da ita mu biya bukatarmu."

Matar ta fashe da kuka tana waiwayen bayanta mijinta take nema can ta hangoshi ya rarrafo gurin cikin fitar hayyaci yace."Oga dan Allah kada kuyi mata wani mummunan abu ni ne mijinta tunda dai kun samu abunda kuke bukata shikkenan."

Wani wawan mari ya kwad'a masa a take hancinsa ya fashe da Jini yasa kan bindigar dake hannunsa ya dinga dukan kansa da mugun karfi har sai da yaga galabaitar dashi tukkuna ya kyaleshi ya fad'i a gurin jina jina dashi! matarsa da 'yarsa sai kuka suke a kansa.........Fizgo hannunta yayi ya hau janta a k'asa ta dinga ihu tana fad'in "Ku taimaka min kada ku bari ayi zina dani." 'Kwakkwaran motsi babu wanda yayi a gurin mijin nata ya rarrafa ya mike domin ceton matarsa dan fashin ya kai masa wawan duka ya fadi a gurin a sume.

Khalid yayi shahada ya mike da saurin gaske yace."Kai bawan Allah kaji tsoron Allah kuji tsoron ranar had'uwa dashi shin wai baka san matar aure ce ba kada kuyi zina da ita da nauyin aure a kanta Allah ba zai barku ba.

A sukwane! sukayo kansa dukkaninsu! Salmanu ya shiga tsananin tashin hankali ya dinga jan hannun Khalid din wai ya tsuguna ya basu hakuri Khalid ko gezau beyi ba yana tsaye suka karaso gurin babban cikinsu ya daga hannunsa zai kwada masa mari Khalid da sauri ya rike hannun.......Cike da mamaki jama'ar gurin suke kallonsa. Kafin kiftawar ido yaji saukar wani mugun duka a tsakiyar kansa...ihu! ya kurma yayin da lokaci guda yaji wani dummmm! a kunnesa tangad'i ya farayi Salmanu ya mike a zabure! yayi nufin rikeshi Danfashin da yake bayansa ya bangajeshi ya fad'i! 'katon dutsen dake hannunsa ya sake bugawa Khalid a kansa a take ya fad'i a gurin ya suma gefen kansa ya fashe sai zubar da jini yake........Fitilolinsu suka kashe gurin yayi duhu! dumd'um! suka ja matar nan tana kurma ihu! suka sanyata a motarsu suka tafi da ita.....




*Littafin na kudi ne....Kada ki siya ki fita dashi...idan kika ganshi a gruops kada kiyi sharing......Idan kika karanta baki biya ba na biki bashi.....Idan kina so ki biya kudin littafin ga yanda abin yake... Vip gruop#600 normal gruop#300...account.. 0542382124...Binta umar gtbank....Idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min magana ta WhatsApp da wannan numbers*
*07084653262*
*08089965176*
*BINTA UMAR ABBALE*
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA GUDA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*

_*Ina kaunar ku iyayena ina kuma alfahari da irin kaunar da kuke nuna min????*_


*37&38*
Khalid da Salmanu sun sha matukar wahala kafin wani bayerabe ya tausaya musu ya basu gurin kwana a jikin gidansa, tunda suka sauka a garin suke buge-buge a kasuwanni domin su samu abinda zasu ci idan dare yayi su shiga 'kar'kashin gada su kwanta asuba nayi suke futowa daga karkashin gadar suyi sallah su shiga buge-buge kamar yanda suka saba Akande beyerabe ne kullum yana ganinsu a kasuwa suna bulayi da daukar dako sai ya tausaya musu ya dinga jansu a jikinsa yana nuna musu gurin da zasu shiga su samu aiki cikin ikon Allah kuwa suka kutsa cikin kasuwar su shiga cikin kanikawa masu gyaran abubuwan hawa suka fara taimaka musu da yake duk yawanci masu aiki a gurin 'yan jahar kano ne shiyasa suka saki jikinsu dasu suka basu gurin zama suna nuna musu yanda zasuyi sati hudu sun zama 'yan gari domin gyaran mota kona babur babu wanda basu iya ba.
Idan sun tashi daga aiki sai su nufi shagon da suke kwana wanda yake jikin gidan Akande, watansu biyu a legos suka siyi waya Khalid yasa Sim card dinsa a wayar shi kuwa Salmanu sai da ya siyi wani akai masa rigistar Allah yasa yana da number wayar mahaifiyarsa saboda haka kai tsaye ita ya fara kira.

Khalid kuwa babu wanda yayi tunanin kira sai aunty shi domin kullum da ita yake kwana a cikin ransa zuciyarsa na fada masa cewa ta riga tayi auranta fa sai dai ka hakura duk sanda zuciyarsa tayi masa wannan tunin yini yake cikin damuwa da bakin kishi.



Muna tare da Hauwwa a gidanta mai lalle nayi min na biki kiran wayar tashi ya shigo waya ta a lokacin da naga sunansa yana yawo a fuskar waya ta sai da na zabura! mai lallen tayi saurin rike kafata nace."Dan saurara na amsa waya.

Kafata ta saki na kalli Hauwwa a sanyaye nace."Khalid ne."? Baki ta bude da sauri tace."Ikon Allah dama yana raye a duniya.?

Hannu na daga mata nasa wayar a kunnena.

sanyayyar ajiyar zuciyarsa naji a kunnena kafin naji sautin muryarsa yana kiran sunana.

Na amsa a nutse da fad'in "Khalid tsayin wattanin hudu kana ina ne? shin kasan halin damuwar ka jefe iyayen ka a ciki kuwa? Uwa uba Gwaggo na nan ta'ki lafiya kullum sai tayi kuka kafin ta kwanta bacci tana ganin kamar baka raye a duniya dan Allah ka dawo gida ni idan saboda ni ka tafi to ka dawo na yafe maka.''

A sanyaye yace." Aunty Sa'ida idan na dawo gida zaki aure ni."? Gabana ya fad'i nace."Khalid ashe har yau baka daina wannan tatsuniyar ba."?

Ransa ya 'baci yace."Ki daina kiran soyayyata da ta tsuniya insha Allahu sai ta zama gaske."

Nace."Okey to naji yanzu dai yaushe zaka dawo gida."? Yace."Kina so na dawo ne."? Nace."Eh ka dawo ka nemi afuwar iyayenka ni kuma na yafe maka."

Yace."Aunt Sa'ida idan na dawo gida zan takura miki fa." Nace."Khalid na amince zan aureka ka dawo gida."

Da sauri yace."Da gaske kike.''? Ajiyar zuciya na sauke cikin yaudara nace "Eh da gaske nake kana dawowa za'a daura aure."

Yana dariyar farin ciki yace."Okey ki bani Gwaggo mu gaisa insha Allahu zan dawo gida a satin nan.

Nace."To yanzu dai bana gida ina gidan 'kawata Hauwwa insha Allahu idan na koma gida zan kira ka sai ku gaisa."

Yace."Nagode auntyna insha Allahu zakiyi alfaharin aurena zan jiyar dake dadin duniya auntyna zan kula dake zan zama bawanki zan kwanta ki taka ni zan zama d'an aiken ki zan......Katse shi nayi nace."To duk naji na kuma gamsu da maganarka Ka bari idan ka dawo sai ka 'karasa.

Yar dariya yayi yace."Okey to shikkenan zan kira anjima idan kin koma gida." Ina kokarin kashe wayar nace"babu damuwa.

Hauwwa ta zuba min ido tana kallona tace."Sa'ida babu kyau yaudara fa ban so kikayi masa haka ba ya za'ayi kice zaki aureshi bayan kin san gobe daurin auranki."?

A sanyaye nace."Hauwwa ni nasan halin Khalid idan ba haka nai masa ba wallahi ba zai dawo ba ga Gwaggo taki kwantar da hankalinta dan har fargaba nake na tafi na barta cikin halin damuwa kullum da daddare sai na lalla'bata take bacci.'

Hauwwa tace."To yanzu idan yazo ya tarar kinyi aure fa wane hali kike so ya shiga."?

Kai tsaye nace."Sai yayi hakuri ya kaddara cewa ni d'in ba matarsa bace."

Hauwwa tace." A gaskiya da kamar wuya ya iya wannan hakurin dan yaron yana miki mahaukacin so." Nace."To hauwwa idan ba zai yi hakuri ba sai yayi abinda zaiyi." ta bini da kallon mamaki! na Kalli mai kunshin nace."Baiwar Allah ki cigaba." Ta kama kafata da sauri ta cigaba da akinta.

Khalid cike da farin ciki yake shedawa abokinsa Salmanu abinda ke faruwa. Salmanu na washe baki yace."Kai amma naji dadi wallahi to yanzu ya za'ayi naji kace a cikin wannan satin zaka tafi kuma gashi zamu fara buga wasa a Club kasan kana da mutukar mahimmanci a 'kungiyar nan ko zaka bari mu gama wasan in yaso wani satin sai ka tafi."

Girgixa kansa yayi yace."Salmanu hankalina gabadaya yayi gida wallahi kafin na tafi zan nemi shugaban kungiyar na fada masa uziri na idan za'a d'aga wasan nan da sati uku sai ayi min uziri idan kuma yana ganin da akwai wanda zai kawo a madadi na sai ya kawo dan gaskiya babu abinda zai hana ni tafiya gida.

Salmanu jikinsa yayi sanyi sam baya so abokin nasa ya tafi yana ganin kamar damar da suka samu zata iya kufcewa gashi ogan nasu kullum sukaje training yakan fad'a musu cewa yana so su mayar da hankali sosai domin a wannan karon ne yake so ya za'bi za'kwa'kurai a cikinsu da zasuje america su buga wasa to
wannan dalilin yasa gabad'aya Salmanu baya so a bokin nasa ya tafi domin jikinsa na bashi kamar zasu samu nasara.

Khalid yace."Tashi ma muje chamber d'in Allah yasa mu sameshi." Salmanu ya mike yana kokarin cire kayan jikinsa ya sanja wasu.


Sun ci sa'a sun sameshi yana horar da wasu suka samu kujeru suka zauna bayan sun gaisa....Oga Labaran yace."Khalid me yasa yau baku shigo da wuri ba."?


Yace."Wallahi oga mun je gurin aiki ne kasan dama sai da mukayi maka bayani cewa asabar da lahadi ba zamu dinga zuwa da wuri ba saboda muna zuwa gurin aiki da wuri.

Oga Labaran yace."Eh hakane na manta da wannan bayanin dama inaso kuzo mu tattauna ina fata dai kuna cigaba da shirye-shirye kamar dai yanda na fada muku cewa Mr William zai zo a ranar da zamu buga wasa na k'arshe kuma a ranar za'a za'bi muzakkarai a cikinku domin kuje ku fatata da 'yan wasan dake can america.

Khalid yace."Oga sai da ni ayi min uziri wallahi cikin satin nan nake so naje ganin gida."

Oga Labaran da sauri ya kalleshi cikin yanayi na damuwa yace."Khalid me yasa zakayi mana haka? kana fa d'aya daga cikin 'yan wasan da nake alfahari dasu, ka iya buga 'kwallo sosai shiyasa nake so kai ka zama zakaran gwajin dafi nasan ko munje america ba zaka bani kunya ba sai kuma kazo min da wannan maganar.""


Yace."Oga wallahi uziri babba ne zai kai ni gida ayi min alfarma." Oga Labaran ya girgixa kansa da fad'in "Khalid dole fa kayi hakuri domin ba zaka sa nayi asara ba ka bari muyi wasan nan mu gama lafiya a za'bi wanda suka dace ayi dasu in yaso sai ka tafi kafin lokacin tafiya american ya tashi."

Khalid yayi shuru tare da sunkuyar da kansa tunani yake akan lamarin.....Yana son aunty Sa'ida baya so ta kufce masa gefe guda kuma ga wata babbar dama ta same shi wacce yake saka ran samun nasara wai shin ya zaiyi ne?

Oga Labaran ya kalleshi da fad'in "Khalid kayi shuru kada fa ka bani kunya khalid."

Ya dago kansa da fad'in "Oga zanyi nazari akan al'amarin insha Allahu kafin lokacin zan yanke shawara." Yace."To shikkenan Allah yasa naji alkairi."


Har sun miqe da niyyar tafiya ya hana su yace su sanya kaya suyi wasa. ba tare da 'bata lokaci ba suka bi umarninsa suka shiga d'akin da suke shiryawa suka sako kayan kwallo suka fito kai tsaye filin wasa suka nufa su shiga shiga cikin 'yan uwansu Oga Labaran ya mike yana zagaye gurin tare da addua akan Allah ya daukaka 'kungiyarsa ta Kano pillas.


****
Ina komawa gida na fad'awa Gwaggo cewa Khalid ya kira waya sai ta kwantar da hankalinta yana raye bai mutu ba, ba tare da tace min komai ba naga ta mike ta dauki buta ta fita, alwala ta dauro ta dawo dakin ta gyara dadduma ta tayar da sallah, ina zaune ina kallonta tayi raka biyu ta jima a sujjadar karshe tana addua kafin ta dago....ko bayan da tayi sallama ma sai da ta daga hannu sama ta dinga godewa Allah tana share hawaye.....na cika da d'umbin mamakin irin kaunar da takewa yaron


Mi'kewa tayi ta fita daga dakin minti uku suka dawo tare da Ummatu tana washe min baki tace."Sa'ida ashe Khalid ya kira ki a waya ko."? Nace."Eh wallahi d'azu da rana mun jima muna waya har yace yana so yayi magana daku nace ya bari na koma gida.

Gwaggo tace"Dan Allah ki kirasa 'yar albarka so nake naji miryarsa.

Nace."Gwaggo babu kudi a waya ta bari a samu yaro ya siyo kati.'' Da sauri Ummatu tace"Ga dari biyu a siyo katin." kokarin kwance bakin zaninta take nace"Haba dai bari ba sai kin bada kudi ba bari na duba yaro." Gwaggo tace."Sa'ida na dauka gurin siyar da katin babu nisa inace gurin Auwala ne." Nace."Eh tace."To bani na siyo da kaina." kallonta nayi naga duk ta tashi hankalinta na koma na zauna bakin gado ina gwada siyan kati ta banki babu network ko kad'an na mika mata kudin ta yafa mayafi da sauri ta fita.

Ummatu kuwa tsayawa tayi tana jana da hira na dinga mamakin matar ta saki jikinta dani a yanzu ta daina jin haushina kullum kuma na gaisheta da sauri take amsawa komeye dalili oho.

Gwaggo ta dawo gidan da katin mtn a hannunta da sauri na kar'ba nasa a wayar.......Muryar wani mutum naji a kunne na. nace."Dan Allah Khalid fa."? Yace."A yanzu dai suna filin wasa sai dai idan sun fito." ko kafin nace komai ya kashe wayar.

Gwaggo a sanyaye tace."Ya akayi."? Nace."Wani mutum ne ya dauki wayar yake cewa wai khalid din yana filin wasa.

Gwaggo da Ummatu suka had'a baki gurin fad'in "Ina ne kuma filin wasa."? Nace"Watakila gurin ball yake nufi kun san dama Khalid akwai naci ball a lokacin da yake gida.

Gwaggo tace."Eh hakane kuwa to an jima sai a sake kiran wayar. shuru nayi ina duba waya ta Ummatu tace." To bari naje na karasa ayyukana."Gwaggo tace."To shikkenan daga zarar wayar ta shiga zan fito na fada miki." Ummatu tace to shikkenan a yayin da take kokarin barin gurin.


Kallonta nayi a nutse nace."Gwaggo a yau da daddare nake so naje gidan Ummana nayi sallama da ita." Gwaggo tace."Ba zaki bari ba gobe idan za'a kai ki dakin ki sai na raka ki." Nace."Aa Gwaggo gwara naje yau din." Tace."To shikkenan Sa'ida ai ni ban ta'ba ganin biki irin naki ba sam baiyi farin jini ba.

Nace"Saboda me kike ce haka."? Tace."Ai gani nayi gidan nan yaki cika da mutane makota ne kawai suke shigowa a tsaitsaye suyi Allah ya sanya alkairi su fita."

Nace."Gwaggo wannan kuma kanki zaki tuhuma ina dangin suke."? Tace." Sa'ida kenan ai ni dangina duk sun mutu saura qalilan dama bamu da yawan zuria ko baki gani bane."?

Nace."Hakane amma ai Ummana tana taro a gidanta ita da 'yan uwanta'' Tace."Aikuwa mu dai sai gobe idan an daura aure zamuyi namu taron."

Shuru nayi tace."Dan Allah ki zauna a dakin mijinki lafiya tunda dai Allah ya had'aki da kishiya mai mutunci to ki 'ki ji ki 'ki gani babu ruwanki da 'yan bani na iya kada 'kawar data zugaki ki dauka.

Nace."Insha Allahu Gwaggo zan bawa mara d'a kunya." Tace."Allah ya sanya alkairi Ya bada zuria dayyu'ba." a zuciya na amsa da ameeen.

Dakin yayi shuru na minti biyu kafin tace."Sa'ida Alhaji Shamsu mutumin kirki ne kwarai duk hidimar kayan daki ya dauke ya hana Ibrahim siyan komai duk abinda kika gani a dakin ki to Alhaji Shamsu ne ya siya miki saboda haka ki rike shi da kyau kinji ko."

Nace."To Gwaggo insha Allahu.....Ta dauki goro ta gutsira tana taunawa tace."Oh! yau dai zanji muryar Khalid a kunnena wallahi ni kadai nasan halin damuwar da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login