Showing 24001 words to 27000 words out of 185789 words
damuwa.
Baba Iro ne ya shigo dakin da carbi a hannunsa suka gaisa yace."Gwaggo ya kike ganin za'ayi ne."? Tace."Ibrahim ni da kaina zani gidan Alhaji Shamsun dan bana tantama can ta nufa kome suke ji dashi na rantse ni nafi karfinsu Sa'ida ikona ce dan haka tilas ta dawo gabana ta cigaba da zama."
Yace."Gwaggo kada ki fusata komai cikin nutsuwa za'ayi Alhaji Shamsu babban mutum ne mai mutunci bai kamata kije har gidansa gaban iyalinsa kici masa mutunci ba."
"Ibrahim bafa zan zauna nayi lako-lako ba wato ka manta irin d'auki ba dad'in da mukayi dasu a wacan karon ko wane irin abune baiyi ba akan lallai Sai Sa'ida ta zauna a hannunsa to wannan karon ma ko yafi 'kuda naci ba zata zauna a gidansa ba domin bamu gaza dayi mata komai ba."
Baba Iro yayi shuru yana mamakin halin mahaifiyarsa yasan halinta da rashin tsinkaye da hangen nesa zata iya zuwa gidan mutum gaban iyalinsa ta tsinka shi wannan dalilin yasa yayi wani tunani....."Gwaggo ki nutsu ki kwantar da hankalin ki insha Allahu Sa'ida zata dawo gida da kaina nake so naje gidan mu tattauna da Alhajin yana ganin mutuncina sosai itama Sa'idar haka da yardar Allah tare da ita zan dawo gida."
"Aa Iro gwara mu tafi tare ayi komai a gabana wallahi nake fada maka jiya kewarta hana ni rintsawa tayi.'' Yace." Ai bake kad'ai ba Gwaggo ni kaina banyi bacci ba amma insha Allah komai zai zo da sauki kiyi hakuri naje ni kad'ai din."
Shuru tayi alamar bata gamsu da maganarsa ba...Khalid ya shigo dakin suka gaisa da mahaifin nasa tace."Khalid kaje ka aro adaidaita sahun abokin ka kazo ka dauke ni ka kai ni gidan Alhaji Shamsu."
Babu walwala a fuskarsa yace."Me zakije kiyi."? da sauri tace."Zanje na dauko Sa'ida ne." Yace."Gwaggo babu inda zakije aunty Sa'ida zata dawo da kafafunta bayan haka kuma shi wanda zai bani aron adaidaita sahun nasa ya fita aiki da ita saboda haka ki zauna a gida zamuje nida Baba."
Da sauri tace."Zakuwa ku gan ni a gidan domin kuwa Allah ya hore min kudin mota.''
Baba Iro cikin rarrashi yace."Gwaggo abinda nutsuwa bata bayar ba to tashin hankali ma ba zai bayar dashi ba dan Allah ki nutsu kada kizo ki aikata abu daga baya kizo kina jin kunya Alhaji Shamsu bai cancanci tozarci a gurin mu ba yana kuma da ikon ri'ke Sa'ida a hannunsa tunda yana matsayin mijin mahaifiyarta.
Tace."Ai kaji abinda nake gudu dama nasan ko kaje ba wani mataki zaka dauka ba karshe ma ka dawo gida kai kadai ba tare da ita ba to sai naje na fada maka."
Khalid yace."To kije d'in kina shiga gate din zan sa masu gadi su saki karnuka kin san zan iya ko." shuru tayi tana kallonsa, Yace."An fada miki cewa komai a hankali da nutsuwa ake binsa amma kin kasa ganewa." tasa kuka da fad'in "Khalid bana son Sa'ida tayi nesa dani shiyasa kaga duk hankalina ya tashi bana so wannan karon Alhaji Shamsu ya samu galaba akan mu."
Yace."Ba zai samu ba insha Allahu." hawaye ta share tace."Khalid shiyasa nake so ka aureta na dinga ganinku a gabana inaso ku haifa min zuria mai yawa."
Tausayi ta bashi yace."To Allah ya amsa adduarki ina fata dai yanzu kin janye maganarki ta zuwa gidan." Tace."Tunda kunfi karfina na hakura ina zuba ido kuje ku dauko min ita."
Baba Iro yace."To Alhamdulillahi bari na kimtsa na fito, yana kokarin fita ta kira sunansa, juyowa yayi yana kallonta tace."Maganar Rabi baka ce min komai ba."
Yace."Tun jiya tana gidansu ai." girgiza kanta tayi tace."To wannan hukuncin daka yanke ni yayi min daidai na kuma ji dadi gobe ma sai ta sake aikatawa amma inaso yau idan Sa'ida ta dawo gida kaje kayo bikon matarka."
Yace."To Gwaggo yanda kika ce hakan za'ayi.'' ya juya da niyar fita sai ya tsaya da fad'in ."Me zaki karya dashi na aika a siyo miki." Tace."Ibrahim ba sai kayi asarar kudin ka ba ina da d'umame gashi can a jibge yanzu zan d'umama kafin ku tafi sai kuci."
Yace."To shikkenan Gwaggo." Bayan fitarsa daga dakin sai ta fara janyo kwanukan abincin tana dubawa doyar babu abinda tayi sannan itama farar shinkafar da Ummatu ta dafa a daran ranar ba tayi komai ba ta mike ta fita da kwanukan abincin a hannunta tana fad'in "Ruwan zafi kawai zan sa na turara shinkafar tunda da abincin ai ba sai anyi hidimar siyan wani abu ba."
Tsaf ta gyara abincin ya dawo tamkar sabo ta dauko ta kawo daki....cikin plate ta zuba masa ta zuba masa miyar nama da yawa.....yace." Gwaggo a'ina kuka samu nama haka."?
Tace."Kasan duk sati Alhaji Nura yakan kawo mana cefane to jiya da ya kawo sai Sa'ida tayi mana miya harda kayan shayi ma watakila ta tafi da abunta."
'Bata fuska yayi yace."Gwaggo nayi sha'awar abinci amma ba zanci ba." tace."Sabida me Khalid."? Hankalinsa nakan wayarsa yace."Saboda ina kishin mutumin na tsaneshi wallahi."
Tace."Khalid ka kwantar da hankalinka kai zaka auri Sa'ida Alhaji Nura kuwa shi yaga zai iya wahalar da kansa mu dai duk abinda ya kawo hannu biyu zamu sa mu 'karba.
Yace."Gwaggo idan kina bukatar farin ciki na to ki daina cin abinda mutumin zai kawo wa aunty Sa'ida wannan shine abinda nake bukata dake."
Shuru tayi tana girgiza kanta bata tsammanin zata daina cin kayan dad'in da Alhaji Nura zai kawo musu amma saboda ta kwantar masa da hankali tace."To shikkenan tunda baka so na daina."
Mikewa yayi zai fita tace."Yanzu Khalid kana kallon abinci da kyau amma kace ba zaka ci ba." Girgiza kansa yayi yana ta'be bakinsa yasa takalmansa ya fita..........Baba Iro ya shiga dakin cikin shiri yace."Ina Khalid din." tana tsotse 'kashin hannunta tace." Wata'kila ya tafi gurin mai shayi.'' da mamaki a tare dashi yace."Wannan abincin fa."?
Tace."Ibrahim kasan Khalid da zuciya da kishin kansa wai ba zai ci ba saboda yana kishi da wanda ya kawo cefanan."
Baba Iro ya zauna kusa da ita yana girgiza kansa mamaki yake sosai akan irin tarangahumar d'an nasa in banda abinsa inashi ina Sa'ida ko da yake Namiji komai 'kan'kantarsa mutukar ya balaga to mace duk girma da shekarunta bata gagararsa.....Gwaggo ta zuba masa abincin tasa masa miya da uban nama akai." Yace."Gwaggo ki rage naman." Tace."Ibrahim kaci ka 'koshi ka barshi.''
Bisimillah yayi ya fara cin abincin. dakin yayi shuru na tsayin minti biyar yace."Gwaggo ya kamata mu samu zama da mutumin nan idan da gaske yake akan yarinyar nan ya fito ayi abinda za'ayi."
Da sauri tace."Ko da gaske yake ba zamu bashi Sa'ida ba tunda Khalid ya nuna yana so hausawa na cewa gida bai koshi ba ba za'a kai dawa ba."
Yace."Gwaggo duk da Sa'ida budurwa ce to bai cancanci ayi mata dole ba shin da bakinta kinji ta furta tana san auran Khalid."?
Girgiza kanta tayi tace."Aa bata furta ba asali ma kullum cikin fad'a da juna suke sam basa jituwa dalilin ma kenan da yasa naje na kar'bo taimaiko gurin mai magani Ibrahim yarinyar nan Sa'ida na tare da iskokai kaga kuwa idan ba na gida ne ya aureta ba to babu shakka akwai matsala shiyasa kaga sam! bana sha'awar wani na waje ya aure ta."
Baba Iro shuru kawai yayi ya cigaba da cin abincinsa, shi kam ba zai iya da rigimar mahaifiyarsa ba mutukar shine madaurin auran Sa'ida to ba zai daura mata aure da wanda bata so ba.
To Cikin nutsuwar zuciya na wayi gari a gidan mahaifiyata, sai da nayi wanka tsaf na shirya jikina sannan ta shigo dakin fuska a sake tace."Sa'ida kinji shuru ko." Murmushi kawai nayi nace."Umma ai nasan inda kike ina fata kin tashi lafiya."?
Tace."Lafiya kalau alhamdulillahi Jiya duk na shedawa Alhaji abinda yake faruwa shima al'amarin bai masa dadi ba ko kad'an dan haka ya yanke hukuncin kan cewa ko zaki koma can gidan sai kin kwana biyu anan kin samu nutsuwa tukkuna."
Ajiyar zuciya na sauke cikin zuciyata ina jin dadin hukuncin da ya yanke. tace."Ki tashi kije ku gaisa dan fita zaiyi bayan kin fito daga dakin nasa sai ki shiga dakin matan gidan ku gaisa.''
Nace."To shikkenan Umma." hanyar fita ta nufa da fad'in "Bari na shiga kicin na taimakawa Asabe da aiki kada ya yara su makara a makaranta." Nace."Umma ai yau Lahadi babu skull.'' tace."Ai yaran gidan nan suna zuwa islamiyya tahafiz in suka tafi sai yamma suke dawowa."
Bayanta nabi da fad'in "To bari nima nazo ayi aikin dani." Mirmushi tayi ba tare data ce komai ba ta nufi hanyar babban kicin din nasu dake tsakar gidan.
A nutse nayi sallama cikin dakin nasa......Ya amsa min tare da kiran sunana." Na karasa cikin dakin sosai ina amsawa har 'kasa na tsuguna na gaishe shi. Ya amsa cikin sakin fuska da kulawa ya d'ora da fad'in "Sa'ida jiya mahaifiyarki duk tayi min bayanin abinda ke faruwa da rayuwarki naji rashin dad'i sosai kuma raina ya 'baci dalilin da yasa ma kenan na yanke hukuncin kan cewa ko zaki koma can gidan to ba yanzu ba sai kin samu nutsuwa saboda haka ina so ki kwantar da hankalinki ki cire duk wata damuwa dake ranki insha Allahu Allah zai kawo miki miji nagari ki aure."
Cikin rauni gami da tausayin kaina nace"Nagode Alhaji insha Allahu kuma zan cire al'amarin daga cikin raina."
Yace."To Alhamdulillahi ya aikin ki ina fatan komai lafiya."? nace."Alhamdulillahi komai lafiya Alhaji."' Yace."To masha Allah Allah ya taimaka." Na amsa da ameeen tare da kokarin mikewa yace."Kyace ina kiran mahaifiyar taki." Nace."Tom zan fada mata yanzu.
Ina fita na nufi kicin din na sheda mata kiran da yake mata, cikin sakin fuska muka gaisa da mai aikinsu Asabe har tana tambayata yaushe nazo. nace "Shigowar dare nayi shiyasa ba kowane yasan da zuwana ba."
Sai bayan mun kammala aikin ne na samu nutsuwar shiga d'akunan abokan zaman nata muka gaisa dasu cikin mutunci da girmamawa Famliy d'in Alhaji Shamsu suna da kirki sosai Mussaman Babban d'ansa Mai suna Aminu mun saba dashi sosai yana da kirki da saukin kai kud'in sa sam bai rufe masa ido ba babbar matsalar Yaya Aminu rashin aure anyi anyi dashi yayi aure ya'ki ga uban kudi da yake samu dan kasuwa ta nayi dashi sosai yake fita 'kasashe ya shigo da kaya amma duk kudinsa da tsayin shekarunsa bashi da mace... mahaifiyarsa har magunguna take 'karbo masa cikin dubara take bashi a ganinta ko bashi da lafiya shiyasa baya sha'awar auran shi kuwa ba tare da yasan maganin menene ba zai kar'ba yasha tunda yasan mahaifiyarsa ce ba zata cutar dashi ba.
To Alhaji Shamsu na fita da kamar minti ashirin su Khalid suka isa gidan.....su gaisa da maigadi cikin mutunci Baba Iro yace "Munzo gurin maigidan ne." Maigadi yace."Ayya wallahi kun doki gurbi Alhajin bai jima da fita ba sai dai idan kasuwa zaku bishi."
Gabad'ayansu jikinsu yayi sanyi....Baba Iro yace."Babu damuwa insha Allahu zamu dawo da daddare ko kuma gobe da safe idan yaso idan ya dawo sai ka sheda masa zuwanmu."
Maigadi yace."To shikkenan babu damuwa wane suna za'a fad'a masa."? Yace."Kace masa Ibrahim ne Kawun Sa'ida daga Mandawari."
Yace."To shikkenan za'a fada masa insha Allah."
Sallama sukayi da juna Maigadin ya rufe gate din....Khalid a sanyaye yace."Baba mai zai hana mu bishi kasuwar.''? Baba Iro ya girgiza kansa da Fad'in "Khalid al'amarin yana bukatar sirri bai kamata mu bishi gurin sana'arsa ba tunda dai maigadinsa yasan da zuwanmu nasan idan ya dawo zai fada masa."
Jiki a mace yace."Hakane." Adaidaita sahu suka shiga Baba iro yace."Ni Kasuwa zan wuce yanzu yana da kyau kazo muje ." Jim! yayi yana nazari kafin yace."Baba kasan gobe zan koma skull so inaso na koma gida nayi shirye-shirye." Yace."To shikkenan Khalid idan ka koma gida ka taushi zuciyar Gwaggo nasan dai yau akwai rigima a gidan amma kai tunda taku tazo da d'aya ka rarrasheta kafin na dawo."
Yace."To shikkenan Baba." Direban yace." Ina zan kaiku ne naga kamar tafiyar taku ta bambamta." Khalid yace." Kasuwar sabon gari zaka kaishi ni kuma Mandawari." Direban yace."Ai hanyar ta baud'e ni yanzu kai tsaye Sabon gari na nufa."
Yace."Okey to sauke ni na samu wata." ya tsayar da babur din ya fito hannu yasa a aljihu ya dauko kudi ya mik'a masa......Baba Iro yace."Kana da kudi wadatacce a jikinka ne."?
Yace."Eh baba kada ka damu Kuje kawai Allah ya kiyaye." Direban yayi saurin sa kudin cikin d'an bankin dake gaban babur din yaja da sauri suka bar gurin.
Ajiyar zuciya ya sauke bayan barin su a gurin ya tari wani babur din gidan Alhaji Shamsun zai koma.
Maigadi ya bude karamar kofa yana tambayar waye ganin Khalid yasa yace ''Ka dawo kenan."? Khalid yace."Inaso zanyi magana ne da Auntyna Sa'ida."
Jim! yayi kafin yace."Khalid kayi hakuri da abinda zan fada maka Alhaji ya hana kowane namiji shiga cikin gidansa ko masu yi musu hidima iyakar su bakin gate saboda haka nake baka shawarar kiranta a waya ita sai ta fito ku gaisa."
Yace."Okey to bude min na zauna a gurin zamanka sai na kira wayar tata." Maigadin ya bude masa ya shiga ya zauna kan kujerarsa shi kuma ya mayar da gate din ya rufe...
*Masoya a taimaka da Sharing??????*
*IDAN KINA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE......VIP GRUOP#600....NORMAL GRUOP#300.....ACCOUNT.....0542382124.....BINTA UMAR GTBANK.....IDAN KATI ZAKI TURO...#400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHASAP DA WANNAN NUMBER*
*07084653262*
*08089965176*
*BINTA UMAR ABBALE*
*GA IRINTA NAN!!!?????¡â?*
_(LOVE STORY??)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE??_
*MANAZARTA WRITES ASSO?????*
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA GUDA BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
_*Ina kaunar ku iyayena ina kuma alfahari da irin kaunar da kuke nuna min????*_
*14&15*
Wayarsa ya d'auko daga aljihun shart din dake jikinsa sai ya nemo number ta ya shiga kira.
lokacin ni kadaice zaune a falon Ummah ina karyawa, jin kira ya shigo wayata dake gefena a ajiye yasa da sauri na kai hannuna kan wayar kwata-kwata ban kawo shi bane sai da na duba naga number sa akan wayar. tsaki naja na mayar da ita na ajiye a nutse na cigaba da abinda nake.
Ya kira kusan sau hudu bata dauka ba jikinsa yayi sanyi sosai kuma ransa ya 'baci da abinda tai masa yanke shawarar tura mata text yayi kamar haka."
_*Aunty Sa'ida ina fatan kin tashi lafiya na kira wayarki babu adadi sabida wulakanci kin'ki dauka kin tafi kin bar baya da kura a gida saboda ke Baba ya kori Ummatu gidansu bayan haka kuma Gwaggo tana nan cikin damuwa ko abinci ta kasa ci kiyi hakuri ki dawo gida idan ni nake takura miki to ina mai tabbatar miki da cewa gobe i yanzu ina skull saboda haka ki dawo gida saboda farin cikin masu kaunarki.*_
Text din na duba jikina yayi sanyi jin cewar Ummatu na gidansu me yayi zafi da Kawu Iro zai yanke irin wannan hukuncin sai duk naji banji dadin al'amarin ba.
Dakin ta shigo ta sameni a zaune ga kayan break din a gabana na kasa ci tace."Lafiya kika zabga tagumi haka."?
A sanyaye nace."Umma wai kinji Ummatu tana gidansu saboda abinda tayi min Kawu Iro ya yanke mata wannan hukuncin."
Cikin rashin jin dadi tace."Ikon Allah me yayi zafi shi kuwa da zai yanke irin wannan hukuncin a gaskiya ban Ji dadi ba wallahi."
Nace."Nima gabadaya jikina ya mutu wallahi a cewarsa wai ba zata dawo ba har sai na koma gidan.''
Umma shuru tayi tana girgiza kanta kafin tace."A gaskiya Ibrahim ya yanke hukuncin da bai da dace ba ai bai kamata da girmanta da komai yayi mata haka ba."A sanyaye nace." Nima dai haka na gani." tana kokarin bud'e wardrobe d'inta tace."To Allah ya shiga cikin al'amarin ya sasanta tsakaninsu." na amsa da "ameeen ya Allah."
Khalid kai tsaye can babban gida ya nufa gidansu mahaifiyar tasa dake unguwar dala gidan yawa ne irin na gado duk wanda ya tashi a gidan yake aure ya zauna kafin Allah yayi masa nasa shiyasa gidan kullum yake a cike da yara kowanne da nasa .
Kai tsaye bangaran su Mahaifiyarsa ya nufa ya same su suna karyawa da koko da awara zama yayi kusa da kakarsa mai suna Baito yana tsokanarta ganin yanda ta tasa bokitin koko a gabanta tana sha. Tace."Kai ma idan kana sha sai na zuba maka badan halin Ubanka ba."
Yace."Aa bana shan koko kashe min jiki yake." shuru tayi ta cigaba da kur'bar kokonta yace."Baito naga kamar haushina kike ji."
A fusace! tace" Ba dole naji haushi ba Khalid jiya da bakin cikin kakarka da babanka na kwana saboda tsabar rashin mutunci su koro min yarinya cikin dare mai tayi musu da zafi da har zasu yanke mata wannan hukuncin."?
Yace."Baito dan Allah ki samu nutsuwa muyi magana ta fahimta yanzu ina Ummatu take."?
Tace."Tana Bandaki." shuru yayi na minti biyu kafin yace." Baito Ummatu bata fad'a miki laifinta ba ko."?
Tace."Ta fad'a min akan wannan lalatacciyar yarinyar ubanka ya koro ta.''
Khalid yaji kamar ta soka masa wu'ka a ma'koshi yace."Baito bai kamata ba abinda kukeyi kuma fa kun haifa kina da 'ya'ya da jikoki bai kamata ki dinga aibata d'an wani ba yau ko gaskiya ne zargin da kukewa auntyn Sa'ida bai kamata ku dinga zaginta kuna la'antar ta ba kamata yayi kuyi mata adduar shiriya.''
"Allahu akbar! Khalid ka gama nasihar ko baka gama ba."? Tafad'a tana masa wani kallo. yace."