Showing 48001 words to 51000 words out of 185789 words

Chapter 17 - Ga-irin-ta-nan-complete by binta umar abale

05 Jul 2024

24218

na bar garin kano domin mutukar ina zaune a cikinsa hankalina ba zai ta'ba kwanciya ba yanzu nan na kira aunty Sa'ida a waya ta farfad'a min maganar da take so akan wannan mutumin da zata aura Allah Salmanu yanda na tsani Alhaji Nura haka na tsani mutuwa ta idan ina ganinsa zan iya aikata mummunan abu akansa domin sosai nake kishin sa."

Salmanu yace."Dan Allah Khalid ka cire soyayya a cikin ranka kayi abinda yake gabanka wai shin me kake nema ne a gurin aunty Sa'ida bayan ka samu biyan bukatarka duk fa namijin da ya aureta a yanzu sauranka zai samu to meye na damuwa kuma ka cire soyayyarta a ranka ka fuskanci abinda yake gabanka.


"Salmanu bana jin zai ta'ba daina son aunty Sa'ida a cikin jini na yake ko yaya nayi motsi sai na jita a rai na ina yi mata so da kaunar da ban san iya adadinsa ba saboda haka ka daina wannan maganar bana tsammanin zan cire sonta a cikin raina.

Salmanu yace." To ai aure za tayi bai kamata ka cigaba da bibiyarta ba dan Allah tunda dai ka samu abunda kake so a tare da ita to ka rabu da ita ta zauna da mijinta lafiya.

Murmushin takaici yayi yace.''Idan ni ne na auri mace babu budurci wallahi a daran ranar zan saketa to ina fatan hakan ta kasance a kanta Alhaji Nura ya koro ta gida a daran ranar da aka daura musu aure."

A tsorace Salmanu yake kallonsa yace."Khalid wace irin muguwar zuciya gareka wai shin kai baka kaunar zaman lafiya ne kake irin wannan mugwayen kalaman akan 'yar uwarka gaskiya ba sonta kake ba domin duk wanda kake so ba zaka dinga yi masa mummunan fata irin wannan ba."

'Karamin tsaki yaja yace"Salmanu dan Allah maganar nan ta isa haka ni kadai ne nasan abinda yake cikin xuciyata sai kuma wanda ya hallice ni duk da na samu abinda nake so a tare da ita to ba zan daina bibiyar rayuwarta ba."


Salmanu ya dinga girgiza kansa yana mamakin karfin halin abokin nasa.

Yace."Kenan yanzu daka kira wayarta ba hakuri ka bata ba."

Yace."Ganin ina karyar da kaina gurin bata hakuri yasa ta samu damar fad'a min ba'kar magana wannan dalilin ne yasa ka shigo ka tarar dani a burkice Salmanu wai dan Allah dame Alhaji Nura fini da har zata dinga fifitashi a kaina."

Salmanu yace."Watakila kud'insa take so amma bayan haka babu macen da zata dubeka tace bata so Khalid kasan matan yanzu suna so su auri mai kudi ko dan su huta shiyasa kaji nace ka watsar da komai kazo muje mu nemi kudi ko dan mu huce takaici.


"Salmanu bana tsammanin aunty Sa'ida za tayi auran kudi kawai dai nine bata ra'ayi tunda tasha fad'a cewa ita ba zata auri yaro ba sai mai shekaru shin wai wane abu ne take nema da bukata a gurin Alhaji Nura wanda ni bani dashi na zauna nayi tunani sosai na kasa gane mai take hangowa a tattare da mutumin."


Salmanu yace."Son sa take shiyasa take ganin kowane namiji a bayansa yake saboda haka ni dai shawarar da zan baka shine ka tattara lamarinta ka watsa a kwandon shara ka fuskanci a binda yake gabanka.
Murmushin takaici kawai yayi yace."Salmanu duk abinda zan fada maka a yanzu ba zaka gamsu ba saboda kai baka ta'ba soyayya ba sabida haka zanyi kokarin ganin na dauki shawararka amma inaso na sheda maka cewa ba zan ta'ba iya cire son aunty Sa'ida daga zuciyata ba."

Salmanu yace."To Allah yayi maka magani abokina." ya amsa da ameeen yana goge fuskarsa da hankici Salmanu abincin ya zuba musu a plate cikin ikon Allah aka kawo wuta dama zafi ya ishesu sai kawai suka kunna fanka suka fara cin abincin suna tattauna yanda tafiyar tasu zata kasance.


Ina komawa gida na kunna waya ta saboda nasan Alhaji Nura zai iya kirana a cikin ko wane lokaci.....sai da nayi wanka tukkuna na zauna domin cin abinci Gwaggo tace."Sa'ida yau ma sai hakuri domin dai tun safe Rabi tasa kafa ta fita daga gidan nan bayan fitar mijinta.

Nace."Ba ayi abinci ba kenan."? Tace."Sauran taliyar ki na dauka na dafa gatanan a cikin fulas sai dai babu yaji dan nayi ta neman yaro ya siyo min barkono ban samu ba duk suna makaranta.

Nace."Gwaggo taliya da man gyada ina laifin da manja.'' Tace."To nima dai har yanzu ban ci ba dan na tsani taliya ina jiran yara su dawo daga makaranta a siyo min d'an wake a gidansu Mamu."

Nace."Yau kuma d'an wake kike sha'awa."'? Tana cigaba da kad'i tace.Aikam kin san rai da marmari." Girgiza kaina kawai nayi cikin zuciyata nace."Gwaggo sar'ka kenan mai rikicin gangan.

Mikewa nayi zan fita tace."Ina kuma zakije da ina so muyi wata magana mai muhimmanci.

Nace."Zan duba almajiri ne ya siyo min kayan miya nayi miya dan ba zanci farar taliya da mai ulcer zata tayar min.

Tace."Yawwa to tunda hakane nima na fasa siyan d'anwaken Allah yasa a samu almajirin."

Ameen nace na fita daga dakin....daga cikin soron na tsaya ina le'kawa can na hango almajirai su uku hannu na daga musu gabad'ayansu suka 'karaso inda nake na mikawa daya daga cikinsu dari biyu da fad'in "Dan Allah kayan miya zaku siyo min na duka.''

Da sauri suka ce to suka tafi ni kuma na koma cikin gidan


Tana zaune a inda take na nemi guri na zauna ina kallonta da fad'in " Wace magana za muyi."

Ta dago a nutse tace."Ya jikin naki ina fatan gurin ya daina ciwo.'' nace."Eh alhamdulillahi." Tace."Masha Allah haka ake so."

Dakin yayi shuru na minti biyar kafin tace." Dazu bayan tafiyar ki makaranta Ina sauraran shirin *TAMBAYA MABUDIN ILIMI* wanda Malam *AMINU DAURAWA* yake gabatarwa a tashar freedom redio naji yana amsa wata tambaya da akayi masa akan budurwar da akayi mata fyad'e ko kuma karuwar da ta tuba ta dawo gida domin tayi tsarkakken aure shine yake cewa ba kai tsaye za'a daura aure ba sai mace tayi tsarki uku an tabbatar da cewa babu ciki a tare da ita sai a d'aura auran wannan shine daidai da abinda addinin musulunci ya tanada sai duk jikina yayi sanyi Sa'ida ina so kiyi tsarkakken aure gashi yau saura kwana biyar daurin auranki yanzu ya kike ganin za'ayi me zamu cewa da Alhaji Nura nasan dai shi yanzu ya gama shirye-shiryensa lokaci kawai yake jira yanzu ya kike ganin za'ayi."?

Cikin wani irin yanayi nace."Gwaggo wallahi nima ban san ya za'ayi ba gabad'aya na mance da hakan kinga Amfanin sauraran redio kenan da tuni an daura aure akan kwamacala."

Tace." To Sa'ida ai ita redio tamkar makaranta take domin babu abinda basa koyawa mutane wallahi sauraran redio yafi mutum ya kalli akwatin talabijin mutukar ba tashoshin addinin musulunci mutum zai kalla ba."

Nace."Hakane maganarki Gwaggo yanzu wace shawara za 'a yanke."? Tace." Bari Babanki Iro ya dawo mu tattauna shima nasan hankalinsa ne ya dauke baiyi tunanin hakan ba nasan idan ya dawo yaji abinda yake da akwai dole a nemo mafita."

Ajiyar zuciya na sauke nace"Gwaggo Allah yayi mana maganin masifa.'' ta amsa da "ameen 'yan nan."

To kusan awa guda kenan da aiken da nayi wa almajirai shuru basu dawo ba, Nace"Gwaggo kinga awa guda almajiran nan basu kawo kayan miyan ba.

Tace."Sa'ida Ai almajiran unguwar nan su zama abinda suka zama Allah yasa dai basu gudu da kudin ba domin sau nawa suka gudar min da kudi shiyasa kika ina zuwa nayi uzirina da kaina.

Girgiza kaina nayi nace." Allah ya kyauta to.'' tace"Sai dai fa kiyi hakuri ki bada wani kudin a siyo kayan miyan." Nace."Bani dasu tunda kin san yanzu dai a karshen wata muke ki siyo ai nasan kina da kudi.

Tace."To bari na 'karasa abinda nake sai naje na siyo." Tana rufe baki naji alamar shigowar text wayata daukar wayar nayi ina dubawa, Khalid ne wai dan Allah yana so yayi magana da Gwaggo yanzu zai kira sai na bata wayar. takaici ya sani na kashe wayar gabadaya na ajiyeta.

'Bangaransa kuwa hankalinsa ne ya tashi sosai lokacin daya kira wayar yaji ta a kashe ya kalli Salmanu a raunane yace."Kaga ta kashe wayar gabadaya.'' Salmanu yace."Ka kira ta mahaifinka mana." shiru yayi yana tunani kafin ya yanke hukuncin kiran mahaifin nasa.


Baba Iro yana kasuwa yaga kiran D'an nasa 'kin daga wayar yayi har ta karaci ringing d'inta ta katse. Khalid sai da ya kira sau kusan biyar Kawu Ibrahim bai daga ba. sai ya yanke shawarar kiran ta mahaifiyarsa a lokacin ta dawo daga zauran Malam Sammani suna tattaunawa da mahaifiyarta Baito ganin Khalid din ke kiranta a waya sai farin ciki ya isheta hakika babu abinda za tace da malam sammani gashi tun kafin aje ko'ina aiki yayi kyau Khalid din ya kira wayarta.


Hannu na rawa ta dauki wayar tasa a kunnenta tana kiran sunansa.

Ajiyar zuciya ya sauke yace."Ummatu ku gafarce ni." sai kawai ta fashe da kuka da fadin."Khalid kana ina ne? me yasa ka gudu bayan baka ka aikata ba nasan ni yaro na kamili ne ba zai aikata abinda ake zarginsa ba.


Yace."Ummatu ni na aikata ba wani mahaluki ba wallahi nine." sai hawaye suka 'kwace mata tana rawar baki tace."Khalid kaine fa kace."

Yace."Eh Ummatu tsautsayi da qaddara ne ku gafarce ni." hannu tasa ta sharce gumin fuskarta tace."To yanzu kana ina."?

Yace."Ummatu ina gidansu abokina a halin yanzu domin ina jin kunyar sake hada ido da gwaggo da Babana naci amanarsu na tozartasu a idon duniya dalilin da yasa kenan na yanke shawarar barin gari gabadaya.

Gabanta ne ya fad'i da sauri tace."Khalid ba'a kan ka aka fara ba kuma ba za'a 'kare a kanka ba saboda haka ka dawo gida shine kwanciyar hankalina.


"Ummatu kiyi hakuri ki gafarce ni ba zan dawo gida na zauna cikin takaici da damuwa ba ki yafe min kuma kiyi min fatan alkairi a duk inda nake."
Yana gama maganar ya kashe wayar kansa na wani irin sarawa

Ummatu baki a sake take kallon mahaifiyarta Baito tace."Wai me yake faruwa ne."?


Bude baki tayi za tayi magana sai kuma kuka ya kufce mata!


baito hankali a tashe ta dinga tambayarta abunda ya faru Ummatu sai da taci kukunta ta koshi ta fada mata yanda sukayi da Khalid din.

Baito tace."Amma nayi mamakin hakan saboda nasan aikin malam Sammanin kamar yankan wuka haka yake to me yasa wannan karon aikin yayi gardama."


Ummatu tace."Ni babban tashin hankalina ma katifa ta dana siyar gashi yaron nan yana tabbatar min da cewa ba zai dawo gida a wannan lokacin ba


Baito tace"Share hawayen ki ki daina kuka akwai malamai a gari saboda haka yanzu sauran kudin da suka rage a hannunki dasu zamuyi amfani zaki tashi yanzu muje mu nemi inda za'ayi aiki mai zafi akan yaron nan."

Ummatu a sanyaye tace."To shikkenan Baito Allah yasa a dace." Baito ta amsa da cewa "Za'a dace da yardar Allah bari na shirya mu tafi."
Mikewa tayi ta hau shiryawa suna sake tattauna maganar.



Sai daf da magariba suka gama yawace yawacen gurin malaman tun a hanya suka rabu da juna....Ummatu ana kiran sallah ta shigo gidan lokacin Gwaggo na zaune a kan kujera tana alwala sallama tayi Gwaggo ta kalleta kafafunta sunyi fururu! duk tayi firgai-firgai da ita! Gwaggo ta amsa sallamar da fad'in "Rabi daga ina kike haka kinyi fururu dake kamar an haqo ki daga rami."

Ummatu shuru tayi bata tanka mata ba ta bude kofarta ta shige...Gwaggo ta bita da kallo tana girgiza kanta.

Ummatu abubuwan hannunta ta ajiye da sauri ta fito ta shiga kicin ta hura wuta ta dora tukunya ta fito a gurguje tayi alwala azahur la'asar magriba ta had'a a lokaci guda tana idar da sallar ta mike ta dauko kaskon wuta kicin ta shiga ta d'ebo garwashi da yawa tazo ta bude ledojin data shigo dasu wani magani ta dauko daure a leda ta kwance ai kafin kice kwabo ta rikice da atishawa maganin jajawur dashi kamar barkono tana zabga atishawar ta zuba maganin cikin wutar ta mike da saurin gaske ta fito babban tsakar gidan tasa a tsakiya ta tsaya kan maganin tana kiran sunan Khalid.

Gwaggo dake sallah atishawa da majina suka cika mata hanci hawaye kawai take a jigace! ta idar da sallar ni kuwa tunda na leqa tsakar gidan naga Ummatu a tsaye gaban kaskon sai kace soja na koma dakin na kwanta tare da toshe hancina daya cika da majina tsinkakkiya.....Tana idar da sallar ta hau sababi da fad'in "Wace irin jaraba kuma aka shigo mana da ita gida." Zaune na mike ina kokarin hana ta fita ta fizge hannunta da fad'in "Ke sakar min hannu na fita naga jarabar da matar nan take." Fita tayi daga dakin tana surutai....har yanzu Ummatu na tsaye a tsakiyar tsakar gidan da kaskon wuta a gabanta yana hayaki tana kiran sunan Khalid fuskarta tayi gaja-gaja da majina da gumi da hawaye sai nishi take tana sakin atishawa.....Gwaggo da sauri ta 'karasa gurin tasa kafa tayi wurgi da kaskon wutar da fad'in "Rabi wane irin surkulle ne wannan........!




*Littafin na kudi ne....kada ki siya ki fita dashi. idan kika ganshi a gruops kada kiyi sharing idan kika karanta baki biya ba ina binki bashi....idan kina so ki biya to ga yanda abin yake....Vip gruop #600 normal gruop#300....account... 0542382124...Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min magana ta whasp da wannan number.*
*07084653262*
*08089965176*
*BINTA UMAR ABBALE*
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA GUDA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*

_*Ina kaunar ku iyayena ina kuma alfahari da irin kaunar da kuke nuna min????*_



*28&29*
Tun a cikin adaidaita sahu Gwaggo ke tambayata nace ta kwantar da hankalinta babu matsala, ajiyar zuciya ta sauke tana godewa Allah....har kofar gida nace da direban ya kai mu sai cewa tayi ita ya sauke ta a bakin hanya domin tana so ta shiga gidan Uwale su gaisa.

Nace."Gwaggo me zakiji kiyi a gidan Uwale da rana gatse-gatse haka." d'an 'bata fuska tayi tace."Zanje ne mu tattauna al'amuran da suka shafe mu Sa'ida kin san abokin kuka shi ake fad'awa mutuwa."

Idanuwa na suka kawo ruwa nace."Wallahi Gwaggo kika kuskura kika fad'awa Uwale abinda yake faruwa kin kashe kanki domin dai ni nasan Uwale ba zata ta'ba barin maganar nan a cikin ranta ba sai ta fad'awa wani kinga daga haka shikkenan labarin abinda ya faru ya bazu a duniya ko ya sani."

Shuru tayi tana nazari tace."Sa'ida Uwale tana da amana kuma mun jima muna aminta nasan zata ri'ke min amanata.

Nace."Ni dai dan Allah dan Annabi kada kije gidan matar nan wallahi bata da kirki ko kad'an yanda take kawo miki gulmar mutane haka kema zata kai gulmarki gurin wasu.


Tace."To naji dan Allah maganar ta isa haka na fasa zuwa shikkenan ko."

Na kalli direban da fad'in "Shiga damu cikin layin ka ajiye mu a kofar gida.
Da sauri yace." To hajiya.


Koda muka shiga gidan shuru babu motsin kowa kofar gurin Ummatu a rufe da kwado Gwaggo tace."Sarkin yawo kenan wato har ta kulle kofa ta fita."

Nace."Kika sani ko wani uzirin ne ya fita da ita." tace."babu wani uziri ta tafi yawon malamai ne."

Ashe hakane Ummatu bayan fitarsu gwaggo daga gidan itama sai ta shirya a gurguje ta tafi gurin malamin da suke zuwa gurinsa yana musu duba tana kuka duk ta sheda masa abinda yake faruwa.


Malam Sammani ya jima yana zane-zane kafin ya dago kansa ya kalleta da fadin"Rabi yaron nan naki abinda ya aikata gaskiya ne ba sharri akayi masa ba kamar yanda kike zargi! kuma na duba na gani cewa lallai akwai ibtila'in da zai sameshi a cikin 'yan kwanakin nan amma kuma akwai wani tauraro da yake haska shi watakila nan gaba akwai wata daukaka da zai samu sannan maganar surukar ki sai dai kiyi hakuri domin 'kwan'kwaman! da suke kanta sunfi karfin ki itama sunfi 'karfin ta iyayen aljanu ne a jikinta dole kiyi hakuri da duk abinda za tayi miki sai dai akwai wani taimako da zanyi miki akanta zan gwada daure mata baki mu gani idan zai yuwu."


Ummatu ta sharce gumin goshinta hankali a tashe tace."Malam Sammani dan Allah ka taimaka min akan yaron nan hankalina ya tashi da jin abinda kace yayi nisa da gari bayan haka kuma ga ibtila'in da zai hadu dashi ka taimaka min kayi aikin da zai sanya ya dawo gida babu shiri.


Malam Sammani yayi zane-zane a karo na biyu ya duba yaga abinda Allah ya haska masa tabbas duk abinda ya gani a dubansa zai faru amma bari kawai ya sanja mata magana domun ya kar'bi kud'inta ya biya bukatarsa.


"Shikkenan Rabi za'ayi miki kokari akan bukatarki amma kema zaki bayar da sadaka mai auki.''

Tace." To kamar nawa ne abin sadakar."? yace."Dubu bakwai zaki bayar ya isa." jim tayi tana nazari kafin tace."Malam a yanzu dai wallahi bani da dubu bakwai bani da dalilinta amma ina da kayan kudi a gida insha Allahu gobe zanzo maka da kudin sai ka fara gudanar da aikin."


Yace."To babu damuwa insha Allahu zan ajiye aikin kowa na durfafi naki sabida ni kaina al'amarin ya firgita ni amma babu komai za dage da addua muyi masa kiranye ya dawo gida babu shiri itama surukar taki aiki mai kyau zanyi akanta.


Ummatu ta dinga zabga masa godiya kafin tayi masa sallama ta tafi gida .

*Shashashar Uwa kawai a maimakon ta gyara kuskuranta ta sake tafka wani*


Kafin ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login