Showing 75001 words to 78000 words out of 185789 words
normal gruop#300...account.. 0542382124...Binta umar gtbank....Idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min magana ta WhatsApp da wannan numbers*
*07084653262*
*08089965176*
*BINTA UMAR ABBALE*
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*
*_Ha'kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.????????_*
*49&50*
Hawayen dake sharara a saman fuskata bai sanya shi ya sassauta matsar da yayi wa wuyana ba, yana wani irin huci da zufa! yace."Ni zaki yi wa haka ko? me yasa kin san an daura miki aure da wani zaki yaudare ni! kin mayar dani shakatafe sabida kina ganin ina sonki ko to wallahi ki rubuta ki ajiye sai na hana ki jin dadin rayuwa yanda kika hautsina min lissafi kema sai na hautsina naki sai na hana ki zaman aure da kowane mahaluki." Yana maganar yana matse ni a jikin bango had'e da bubbuga kaina yanda jikinsa yake rawa sai ka dauka tsumin 'yan bori yasha hannu nasa akan nasa ina k'okarin cire hannunsa ya sake shaqe ni da kyar nace."Kashe ni kake so kayi ko."?
Ido jawur! yace."Meye amfanin mayaudariya kashe ki zanyi dan baki da wani amfani." ya 'karasa maganar yana sake ma'kure ni a jikin bango(Garu) Gwaggo da Ummatu suka shigo dakin hankalinsu a tashe.
Ganin yanda nayi wujiga-wujiga a hannunsa ya tsorata su Ummatu tazo tana janyeshi had'e da bashi baki ya sake ni! kansa ya sunkuyar k'asa tare da sassauta matsar da yayi min amma bai sake ni gabadaya ba.
Gwaggo tazo ta rike hannunsa a sanyaye tace."Haba Jarumi ka zama mai hakuri da yarda da kaddara mana me yasa zaka aikata haka ka duba kaga yanda duk ka galabaitar da ita kayi hakuri ka saketa komai kaga yana faruwa to dama can haka Allah ya shirya."
Ya kalleta da jajayen idanunsa yace."Gwaggo wato har dake za'a hada baki a yaudare ni ko? me yasa kin san tayi aure baki fada min ba bayan kullum muna waya dake."
Kallona tayi tana so tayi magana sai ta kasa nace."Me yasa zakiyi shuru Gwaggo ki fada masa cewa nice na tsara haka in yaso sai ya dauko wuka ya soka min a ma'koshi."
Raina a 'bace nake magana.
Matse wuya na ya sakeyi ya tsira min rikitattun idanunsa, da 'kyar nace."Khalid ka kashe ni mana mai ka tsaya jira ne." Shuru yayi bai ce komai ba ya dai zuba min idanunsa da nake hango ruwan hawaye a cikinsu.
Ummatu tazo ta cire hannunsa daga wuyana ai banyi wata-wata ba na fitar da hannu a zafafe zan kai masa mari!
Hannun ya rike ya murd'e da mugun karfi na saki ihu! ya yarfar min da hannuna yana huci! ya matsa daga gurin.
Tsugunawa nayi a gurin hawaye masu zafi na zubo min hannuna kawai nake dubawa kamar wacce tayi targade sabida zafi.
Gabad'ayansu kansa suka rufu suna bashi baki babu wacce tabi ta kaina. raina ya 'baci sosai na kalli gefe na kwalbar cocar colar da Gwaggo kesa maganin sauro a kai na dauka a fusace na kai masa jifa da ita. cikin zafin nama ya kauce yana kallona.
Murya na rawa nace."Wallahi sai kasan wanda kayi wa wannan iskanci Khalid sai na fad'awa Kawu yayi min tsakani da kai shashasha mara hankali kawai."
Gwaggo a fusace! tace."Wato ba zaki daina zaginsa ba ko.''
Nima a fusace! Nace." Gwaggo abinda yafi zagi zanyi masa mutukar bai fita daga dakin nan ba."
Tace." ba zai fita ba din sai dai ke ki fita dama ai rashin hakurin ki ne yasa mijin naki ya koro ki gida.""
Cikin takaici da mugun bakin ciki nace."Haka zaki ce ko."? Da sauri tace."Eh mana ai gaskiya ce ya za'ayi ki yaudari yaro bayan kin san ba auransa za kiyi ba shiyasa lokacin da kika zo da maganar hankalina bai kwanta da ita ba saboda nasan halin Khalid da zafin zuciya.
Nace."A lokacin da nazo da maganar gabad'ayan ku kuna neman hanyar da zaku bi kuga ya dawo gida kun rasa me yasa dana kawo shawarar hakan kuka amince sai yanzu kuma ki goya masa baya to bari kaji da kai da Gwaggo a yanzu koda aurena zai mutu ba zan aureka ba kaje can ka nemi daidai da kai." na 'karashe maganar idona a tsaye a kansa.
Gwaggo tace."To dama me zaiyi dake kuma ai shi sabuwar budurwa zai aura mai jini ajika.
Kallonta nayi zuciyata na ingiza ni akan na tashi na hada kayana na bar gidan wata zuciyar tace ki zauna dai har Kawu ya dawo ya yanke hukunci.
Ummatu tace."Ke Sa'ida magana ta mutu dan kyautawa baki kyauta ba kai kuma Khalid ka shiga hankalinka ka gane samu da rashi duk na Allah ne.
Yace."Ummatu wallahi hakkina ba zai bar wannan mayaudariyar ba ta cuce ni."
Nace."Kai har kana da bakin wata magana akaina ko.''? Gwaggo da sauri tace."Magana dai a barta ni bana son wani tashin tashina."
Girgixa kaina nayi cikin tsantsar takaici na kalleshi nace."Hakki ko."?
Kallona yake babu kiftawa nace."To ina rokon Allah ya gaggauta bi maka hakkinka a kaina idan kuma ni nake da hakki Allah ya gaggauta bi min akanka.''
Ina k'are magana ta na fita tsakar gida na zauna dandaryar 'kasa tunanin mafita kawai nake.
Gwaggo da Ummatu da 'kyar suka rarrasheshi ya tsakuri abinci kadan yace ya koshi! mikewa yayi ya fita ya barsu a dakin suna tattaunawa.
Bayansa nabi da kallo a lokacin da yake kokarin fita daga gidan, daidai bakin kofa ya yanke jiki ya fadi.
Gabana yayi wani irin fad'uwa! "Gwaggo." da karfi na kwala mata kira."
Tare suka fito ita da Ummatu na nuna musu inda yake kwance tamkar mara rai.
Gwaggo salati ta rafka hankali a tashe ta kamfato ruwa ta kuza masa a jikinsa, tsayuwa sukayi kansa suna kuka Gwaggo fadi take "Sa'ida kinga masifar da kika janyo mana ko zaki kasheshi ki huta ai.
Daki na shiga na dauko waya ta hannuna sai rawa yake na marasa wanda zan kira a wayar.
Ummatu ta tsuguna kusa dashi tana masa firfita hade da kiran sunansa.
Idonsa ya bude a jigace yake kokarin tashi zaune kansa na wani irin sarawa hakika al'amarin yayi masifar firgitashi da sashi cikin tashin hankali .
Gwaggo hannunsa ta rike sai sannu take masa tana yi masa firfita da mahuci.
Kawu ne ya shigo gidan hannunsa rike da ledoji ganinsu sun masa rumfa da mafici a hannu yasa ya tsaya yana tambayar abinda ke faruwa.
Gwaggo hawaye ta share tace."Faduwa yayi ya suma bayan ya samu labarin auran Sa'ida yanzu yanzu ya farfado.
Kawu bece komai ba ya tsallakesu ya shige ciki
Kallona yayi cikin kulawa nace."Kawu Sannu da zuwa." yana sake nazari na yace."Sa'ida kiyi hakuri da rayuwa kinji ko." hawaye suka zubo min hannu nasa na goge nace."To Kawu insha Allah. Har yayi nufin wuce wa gurinsu sai ya tsaya da fad'in "Har yanzu dai Alhaji Nura beyi magana ba ni kuma bana so na tunkareshi da maganar sabida kada yaga kamar wani abu dole dai zamu cigaba da sauraransa daga nan zuwa gobe idan beyi magana ba to zan samu Alhaji Shamsu da maganar muji hukuncin da zai yanke.
A raunane nace." To shikkenan Kawu."
Gurinsu ya shige ba tare daya waiwayi su Gwaggo ba haushin Khalid din ya shafe su ya lura wani lokacin mahaifiyar tasa ce take d'aurewa yaron gindi yake iskancin da yake so.
Nima mi'kewa nayi na shiga daki na bar su a gurfane a gabansa suna rarrashinsa mussaman Gwaggo da duk ta fita daga hayyacinta, shima abinda ya gani kenan yasa ya sassautawa zuciyarsa ya daure ya mike tsaye, Gwaggo tace ka shiga dakinka ka kwanta ka huta kaji ko Khalid dan Allah dan Annabi ka cire Sa'ida daga cikin ranka idan ka mutu mune mukayi asara ba wani ba.
Kansa kawai ya daga mata ya bar gurin kallo suka bishi dashi suna jimanta abinda ya faru.
To sai da na bari Kawu ya ci abinci ya nutsu tukkuna na shiga gurin na same shi a kashingid'e akan dadduma yana hutawa.
Gaishe shi na sakeyi ya amsa cike da kulawa da fadin "Sa'ida akwai magana a tare dake ko."?
Nace." Eh Kawu nazo ne akan inaso kayi min tsakani da Khalid ya fita daga harkata tunda dai ni ba sa'arsa bace Kawu wai kamar ni Khalid zai shaqewa ma'kogwaro kuma su Gwaggo suna gani sun kasa daukar mataki."
Kawu Iro ya mike zaune ransa a bace yace."Wato Khalid din daga zuwan sa da abinda ya fara kenan me kikayi masa da zaiyi yun'kurin kasheki.
Hawaye na share nace."Sabida kawai anyi masa dubara akan idan ya dawo gida za'a daura mana aure shi ne daya samu labarin aurena da Alhaji Nura ya yanke min wannan hukuncin."
Kawu na kokarin yayi magana ya fito daga dakinsa, a kaina ya tsaya kamar zai mangare ni yace."Ni yaro ne da zakiyi mun dubara mai yasa baki fada min gaskiya ba kika yaudare ni shin kin san halin da nake ciki a yanzu."?
Kawu ya buga masa tsawa da fad'in "Yanzu daka tsaya a kanta dukan ta za kayi kome."?
Sunkuyar da kansa yayi ya nemi gefe ya tsuguna yana watsa min harara! al'amarin ya dinga bani mamaki da tsoro yanzu gabad'aya tsoronsa nake ji sabida dazu nayi masifar galabaita a hannunsa.
Kawu ya kalleshi rai a 'bace murya a kausashe yace." Khalid wallahi ka fita daga idona na rufe kabar ganin duk abinda kayi Gwaggo tana daure maka gindi wallahi ka guji fushi na wato har ka manta laifinka ko ka dawo zaka yi rashin mutunci da rashin arziki ko? Yanzu Sa'ida sa'arka ce da zaka dinga dukan ta."?
Yace."Kawu ka gafarce ni dan Allah ni wallahi 'karya take min ban doke taba."
Kallonsa nayi ina mamakin maganarsa wai yau yaron dana sharewa majina shine yake 'karyata ni."
Kawu ya cigaba da cewa." Kayi yun'kurin kasheta ta hanyar matse mata ma'kogwaro kana nufin idan ka kasheta za'a saurara maka."? shuru yayi Kawun ya cigaba da cewa''Yarinya tace bata sonka bata sonka amma saboda naci ka nace sai ta aureka waye ya fada maka a nai wa so dole ne."?
Khalid ya dinga jin wani maqaqin bakin ciki a cikin ranshi! Kawu Iro ya cigaba da watsa masa 'bakar magana iya yanda ransa yake so tas yayi masa wankin babban bargo dama haushinsa yake ji! Khalid ya rasa inda zai sanya kasa sabida bakin ciki da takaici babu shakka da yasan wannan bakin cikin zai zo ya tarar to da yayi zamansa a inda yake.
Kawu Iro ya cigaba da cewa"To wannan ce maganata da kai ta 'karshe Khalid nayi maka tsakani da Sa'ida babu kai babu ita babu kuma maganar so Sa'ida ta girme maka a yanzu tunda tanada aure sabida haka kada na 'kara jin ka furta mata kalmar so gaisuwar mutunci ce a tsakaninku.
Kaji ko ba kaji ba.?
Cikin Jin mugun ciwon kai yace." Naji Kawu." Ya kalleni da fad'in "Ki tashi kije ki kwanta ki huta insha Allah itama Gwaggon gobe zan zauna da ita akan wannan matsalar.'' Cikin jin dadin abinda yayi wa Khalid din nayi masa sallama na tafi zuciyata fes nasan tunda mahaifinsa yaja masa kunne dole ya fita daga harkata.
*Littafin na kudi ne....Kada ki siya ki fita dashi...idan kika ganshi a gruops kada kiyi sharing......Idan kika karanta baki biya ba na biki bashi.....Idan kina so ki biya kudin littafin ga yanda abin yake... Vip gruop#600 normal gruop#300...account.. 0542382124...Binta umar gtbank....Idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min magana ta WhatsApp da wannan numbers*
*07084653262*
*08089965176*
*BINTA UMAR ABBALE*
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*
*_Ha'kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.????????_*
*52&53*
"Mijin naki ne yazo ne."? Gwaggo ce ke magana tana zaune akan dadduma da carbi a hannunta. A nutse nace." Eh shine yazo yanzu." shuru tayi ba ta sake tankawa ba har na gama abinda nake na fita daga dakin.
Yana tsaye a soro kamshin turaransa duk ya game gurun. babu walwala a tare dani na gaishe shi. sai naga ya saki fuskarsa yana amsawa sai kallona yake yana murmushi.
Shuru gurin yayi na 'yan mintina kafin yace."Sa'ida ina fatan kinyi hakuri akan abinda ya faru tsakanina dake sharrin shed'an ne kuma bana fatan wani sa'bani mai muni ya sake had'a mu."
Murmushin takaici nayi nace." To naji dadin maganarka kuma ina fata har cikin zuciyarka kake maganar domin ni tuntuni na dawo daga rakiyar ka."
D'an murmushi yayi yana kallona yace."Kada ki damu Sa'ida wannan magana har cikin raina nakeyi miki insha Allahu zan gyara kuskure na."
Ajiyar zuciya na sauke ina jin sassauci a cikin zuciyata nace."To ya maganar aikin nawa."
Shuru yayi kansa a kasa yace."Sa'ida ki ajiye batun aiki a gefe kwata-kwata bana ra'ayin matata ta dinga yawo a gari inada kishi mai tsanani."
Na bude baki kenan zanyi magana Kawu ya shigo soron ganinmu a tsaye yasa ya tsaya babu yabo babu fallasa suka gaisa a tsakaninsu.
Kawu yace."Alhaji ai tun shekaran jiya muke tsammanin zuwanka shuru babu kai babu labarinka."
Cikin jin nauyi yace."Malam Ibrahim a gafarce ni wallahi uzirurru ne sukayi yawa."
Kawu yace."To babu laifi ai Allah ya taimaka." ya amsa da ameeen ya Allah"
Kawu yace." Sa'ida tazo mana da magana tana kuka wannan dalilin yasa nace tayi hakuri a saurari zuwanka domin kaima muji ta bakinka.
Yace."Malam Ibrahim d'an sa'bani ne muka samu ni da ita wanda ya sanya ta yanke hukuncin zuwa gida a gaskiya al'amarin beyi min dadi ba ko kadan."
Kawu yace."Yanzu kana nufin dama ba kai kace tazo gida ba." ? Ko kunyata beji ba yace."Kwarai kuwa ni dai bance tazo gida ba nayi mata fada da nasiha akan abinda tayi min na rashin kyautawa."
Kawu ya juyo da sauri yana kallona a lokacin da nake mamakin 'karyar da mutumin nan ya shirga da girmansa da komai amma baya jin kunyar karya.
Kawu yace "Sa'ida ina gargadi akan duk irin sa'banin da zaki samu da mijinki kada ki sake cewa zaki dawo gida ki zauna ki bashi hakuri ku fuskanci juna aiki kuma tunda yace baya so sai ki hakura."A sanyaye nace." To shikkenan Kawu duk abinda kace haka za'ayi.
Ya juya yana kallonsa da fadin"Alhaji a kara hakuri da lamarin mata dan Allah ku zauna lafiya da iyalanka."
Ya amsa da ameen insha Allahu zanyi kokarin ganin na kawo daidaito da zaman lafiya a gidana.
Cikin farin ciki Kawu yace."Yanzu zaku tafi kenan.
Yace."Eh kwarai kuwa." ya kalleni da fadin "Kiyi maza kije kuyi sallama da mutan gidan yana tsaye yana jiranki."
Amsawa nayi da to Kawu da sauri na shiga gidan domin dauko jakar kayana
Yana dogare a bakin kofar dakin Gwaggo suna magana na shiga gidan har na karasa bakin kofar bai kauce min hanya ba sai da nayi masa magana tukkuna ya dan matsa hanyar na duba naga ba tada da spece gurin wuce wa jikinmu zai iya had'uwa.
Kallonsa nayi yana duba wayarsa ya wani murtuke fuska nace."Khalid ko ba kaji ne ka matsa ka bani hanya na wuce." Gwaggo da sauri tace."Ke kam Sa'ida kin fiye neman fituna wace hanya zai baki bayan wacce ya matsa miki.
Nace."Gwaggo duba da kyau ki gani a bakin kofa ya tsaya hanyar ba zata isheni ba.
Gurin take kalla kafin tace."Jarumi bata guri ta wuce kada tayi maka wani sharrin.'' Ba tare da yace uffan ba ya shiga dakin ya zauna a kusa da ita suka cigaba da magana.
Kallonta nayi da jakar kayana a hannuna nace."Gwaggo ni zan koma." baki a bude tace."Ke kadai zaki koma dakin naki babu dan rakiya kuma saboda ke ki ke iko da kanki ba zaki tsaya Kawunki ya dawo su tattauna magana ba.
Nace."Gwaggo yanzu haka Kawu da Alhaji suna tare kuma sun tattauna dik maganar data cancanta."
Shuru tayi tana kallona kafin tace."Ashe ni ban isa ya shigo ya gaishe ni ba kenan.'' Tunda tafadi wannan maganar nasan neman magana take sai kawai na kama hanyar fita ba tare da nace mata komai ba.
Tace."Ai shikkenan Allah ya sa'ba halaye sai ki cigaba da hakuri tunda ke ki kaga zaki iya." shuru nayi mata nasa takalmana gurin Ummatu na nufa nayi mata sallama na fito.
Khalid kuwa kasa sukuni yayi ya rasa abinda ke damunsa kishi mai zafi ya dinga taso masa Gwaggo data fuskanci yana cikin damuwa sai ta dinga rarrashinsa tana tausar zuciyarsa jinta kawai yake da kunnensa amma sam baya fahimtar abinda take fada.
Tun a mota yake jana da hira ni dai jinsa kawai nake da kunne dan na kasa sakin jikina dashi kafin mu shiga gidan sai da ya tsaya ya sayi kaji da yoghot masu sanyin gaske.
Aunty Murja ita da yaran suna zaune a falo suna kallo muka shiga muka samesu.
Babu yabo babu fallasa ta amsa gaisuwata gabadaya ta rage walwala komeye dalili oho.
Nima ban wani zauna a falon ba na mike da jakar kayana na bude dakina na shiga......to har nayi shirin kwanciya bai shigo ba raina ya 'baci sosai dan koda ya shigo dakin sai da ya fahimci hakan sai ya shiga bani hakuri yana inda-inda nace."Alhaji wallahi idan ba kayi da gaske ba aunty Murja zata kai ka wuta gabadaya na lura tsoronta kake ji shin wai itace take auranka ko kaine kake auranta."?
'Bata rai yayi yace."Sa'ida kada ki fada min maganar banza mana ni akwai wata mace data isa naji tsoronta."
Kallonsa nayi ina mamakinsa. ya cigaba da bambami yana kumfar baki. cikin zuciyata nace"Ni ka raina ai shiyasa ka zauna kana min masifa ita aunty Murjan da yake kana tsoronta ai ladabi kake mata. Ajiyar zuciya na sauke nace."Kayi hakuri dan Allah fadan ya isa haka na amince kai tsayayyan namiji ne a gidanka.
Shuru yayi yana kokarin cire rigar shaddar jikinsa. kallonsa nake wani irin feelings na taso min ya mike ya nufi toilet nace yau