Showing 27001 words to 30000 words out of 185789 words
Da alama maganata bata gamsar dake ba."
Da sauri tace."Ta ina kuwa zata gamsar dani bayan nasan karya kake kana fada ne kawai dan ka kareta nan Jamila take sheda mana irin lalatar da takeyi da maza a makarantarsu saboda haka maganar Jamila ba karya bace Sa'ida bata da kintsi da kamun kai."
Jamila 'yar yayan Ummatu ce da suke zaune a cikin gidan Jamila budurwace 'yar kimanin shekara goma sha takwas tana zuwa makarantar da Sa'ida take koyarwa ta *Hajara Buhari* dake goran dutse.
Khalid yace."Jamilan ce tazo tana fad'in wannan maganar."? Baito na kokarin yin magana Ummatu ta karaso gurin da sauri tace."Rabi kinga Khalid daga zuwansa ya soma kalubalantata akan na fadi gaskiya ashe har Sa'ida ta fiki kima da mutumci a gurinsa."
Ummatu ta ajiye butar dake hannunta rai a 'bace tace."Baito aini tuntuni na gama magana wallahi tallahi duk ranar da yaron nan ya sake shiga sabgar Sa'ida to sai yaga abinda zai faru dashi."
Khalid yace."Ummatu dan Allah ki daina wannan maganar aunty Sa'ida 'yar uwata ce bai kamata ki raba zumuncin dake tsakanina da ita ba."
Tace."Ai nima dama ba zumuncin ku nace zan raba ba abinda nake nufi shine ka raba kanka da ita tunda duk wasu alamu ka nuna kana sonta in banda rashin hankali irin naka Khalid me zakayi da wannan yarinyar tsohuwa gata mara daraja da kamun kai kai yanzu ba zakaji kunyar auranta ba."
Yace."Ummatu babu kunya a cikin abinda ya zamanto halas dan aunty Sa'ida ta girme ni hakan ba zai hanani na aureta ba tunda ba haramun bane.''
Baito tace."To ba zaka aureta ba d'in Khalid ba zaka lalata mana zuria ba kaje ka nemo wata ka aura idan baka samu ba kazo gida ka duba gamu nan da 'yan mata kyawawa masu da kyau da duk abinda ake bukata."
Shuru yayi ransa duk a 'bace ya tsani yaga suna nuna k'yamarsu akan auntynsa a ganinsa sam bata cancanci haka a gurinsu ba.
A cunkushe yace."Dama ni nazo ne domin nayi muku sallama idan Allah ya kaimu gobe zan koma makaranta''
Baito tace."Wace makaranta kuma? dama baka gama karatun ba."?
Yace." Akwai sauran kad'an." Tace."To Ubangiji Allah yasa daga ka gama ka samu aiki kaga sai kayi auranka da hujja ni nafi so ma kazo gida ka duba wallahi ina yi maka sha'awar Jamila." tana 'yar dariya ta 'karasa maganar.
Hararar gefan ido yayi mata yana kokarin mi'kewa yace."Baito ni dai Namiji ne babu wanda zai yi min auran dole."
Ummatu tace."Khalid magana kake so ka fad'a mata saboda baka da kunya."?
Girgiza kansa yayi yace."Aa Ummatu kiyi hakuri dan Allah abar maganar amma ni kada a 'kara yi min maganar wata Jamila bana ra'ayinta."
Ummatu ta fusata sosai tace." 'Yar d'an uwan nawa kake k'yamata? meye aibun Jamila yarinya kyakykyawa fara mai kuruciya a jika."
Shuru yayi bai tanka ba yasa takalmansa Baito tace."Ai ni mamaki ma ya hana ni magana 'kiri-'kiri yaron nan yana nuna yafi kaunar dangin Ubansa akan na uwarsa."
Khalid dai baice komai ba ya kama hanya ya fita daga gidan gabad'ayansu suka bishi da kallon mamaki!! bayan fitarsa Baito tace."Rabi hak'ika zama bai ganki ba tilas ki fara neman taimako akan yaron nan idan ba hakaba anan gaba cewa zaiyi ba ke kika haifeshi ba."
Ummatu ta sunkuyar da kanta ranta idan yayi dubu ya 'baci tace."Baito maganarki gaskiya ce Khalid kwata-kwata baya ganina da mutunci baya jin maganata sai ta kakarsa duk abinda Gwaggo tace shine daidai a gurinsa ni ya raina ni alhalin ni na haifeshi kuma mutukar za'a zagi Sa'ida a gabansa sai ya nuna 'bacin ransa saboda haka dole na nemi taimako a gurin malamai su karkarto da hankalinsa kaina dan na rantse ba zai auri Yarinyar nan ba."
Baito tace."Abinda ya kamata kiyi kenan kada kiyi sanya idan anjima ki shirya sai muje gurin Malam Saminu zai taimaka miki akan lamarin."
_Allah kasa mu dace jama'a wai uwa ce take d'ora 'yarta a hanyar zuwa gurin malami a maimakon tayi wa d'anta kyakykyawar addua sai mugun baki take masa 'karshe ma zata kaishi gurin malami Allah ya kyauta yasa mu gane_
Khalid na daf da fita sukayi karo da Jamila zata shiga gidan washe baki tayi da fadin"Laa Yaya Khalid ina wuni."? Kallon banza yayi mata kafin ya ratseta ya wuce ba tare da ya amsa gaisuwarta ba, haushinta yake ji sosai akan k'azafin da tayi wa auntynsa.....Jamila a sanyaye tabi bayansa da kallo gabanta na faduwa itakam ya zatayi ne Allah ya d'ora mata kaunarsa a cikin ranta...jiki a mace ta shiga cikin gidan.
Gwaggo na zaune a tsakar gida ita kad'ai tayi suguri abin duniya duk ya isheta Sa'ida kawai take tunani idonta akan kofar shigowa gidan daga taji motsi zata zabura ta kalli kofa.....Uwale ta rangad'a sallama cikin gidan.
Gwaggo ta amsa mata tare da gyara mata gefanta ta zauna suka shiga gaisawa....Uwale tace."Dama nazo ne naji inda aka kwana shin ina fatan kuna ganin kyawun maganin nan."?
Gwaggo ta sauke ajiyar zuciya rai a 'bace! tace." Ai Uwale Yarinyar nan ta'ki bani had'in kai wallahi da 'kyar ma ta bari aka turara maganin sau biyu daga nasa turaran a wuta zata dinga masifa ta fita daga dakin ta barni a ciki ina shakar haya'kin ke a takaice ma ta gudu daga gidan tun jiya."
Uwale ta rike ha'ba cikin mamaki tace."Kinji ko ai alamun da akwai iska a tare da ita kenan tunda gashi sun hanata zama a gidan saboda turaran da kikeyi musu."
Gwaggo tace."To hakan zata iya kasancewa amma ni ina tunanin abinda Rabi tai mata ne yasa ta tattara kayanta ta gudu."
Cikin son jin gulma Uwale tace."Oh! me kuma Rabin take mata."? Gwaggo ta shiga bata labarin abinda ya faru...Uwale tace."Ai kinga Rabi ko gado tayi dan mahaifiyarta Baito mara mutunci ce babu irin sharri da kazafin da ba tayi wa kishiyoyinta ba ni dama tuntuni nasan Baito ba mutuniyar kirki bace."
Gwaggo tace.''Kice dai Rabi gadon mugun hali tayi."? Uwale ta 'bantari gora ta mi'ke kafarta a kan tabarmar tace"Wallahi kuwa Sau nawa muna had'uwa da ita a zauran malam ai shiyasa kullum nake fad'a miki cewar sai kin tashi a tsaye akan Rabi domin ita da mahaifiyarta biye-biyen malamai suke."
Gwaggo tayi shuru tana jimanta al'marin.....Uwale ta yunkura da fad'in "Gwaggo ni zan tafi dama unguwa zani nace bari na shigo mu gaisa na kuma tambayeki halin da ake ciki."
Gwaggo tace."To Uwale nagode sosai sai kin dawo nazo gidan naki domin mu yanke shawarar yanda za'ayi domi gaskiya maganar Rabi da mahaifiyarta ya tsaya min a rai."
Uwale tace."To shikkenan ai babu damuwa sai kinzo din." Sallama sukayi da juna...Uwale na kokarin fita daga gidan Khalid ya shigo da kyar ya gaisheta yana dauke kansa ya shige gidan.
Gwaggo na ganinsa shi kadai fuskarsa kuma babu annuri sai tasha jinin jikinta.....Ya zaune kusa da ita yana matse gumin goshinta a sanyaye tace."Jarumi ya ake ciki ne ina Sa'idar.''?
Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke kafin yace."Gwaggo lokacin da muka isa gidan Alhajin ya fita sai na yanke shawarar kiran wayarta Gwaggo nayi nayi ta daga ta'ki haka na hakura na kyaleta.
Tace."Yanzu dai baku samu nasarar daukota ba." Kansa kawai ya daga mata ya lumshe idonsa damuwa ce mai tsanani take damunsa.
Gwaggo shuru tayi na minti biyu kafin tace."Idan anjima da yamma zanje gidan ayi wacce za'ayi."
Idonsa ya bude da sauri yace."Kada kije musu gida ki bari Baba yace zai koma da daddare insha Allahu komai zaizo da sauki amma ni bana so kije gidan kiyi wani abu suji haushinki ko kuma daga baya kiyi nadama kiyi hakuri abi komai a hankali."
Shuru tayi ba dan maganarsa ta gamsar da ita ba, yace." kin san gobe ni zan koma skull ko."? Girgiza kanta tayi tace."Bani da labari aini na dauka ka gama karatun ganin wannan karan ka dade a gida."
Yace."Yajin aiki malamai suka tafi karatu kuma da yardar Allah na kusa kammalawa ki cigaba dayi min addua idan na gama na samu aiki."
Tace."Insha Allahu zan cigaba dayi maka addua."
Mikewa yake kokarin yi tace."Zaka ci abinci ko."? kallonta yayi kafin yace."Idan yanzu kika girka zanci." Tace."Sai dai na dauki taliya d'aya a cikin kayan abincin Sa'ida nayi maka dafaduka da daddawa irin wacce kakeso."
Girgiza kansa yayi yace."Kada ki ta'ba mata kayan abinci bari nai wanka na fita na siyo sai kiyi min." Tace."Khalid kada ka 'batar da kudinka zasuyi maka amfani a makaranta ka bari a d'auka tunda da akwai."
Yace."Gwaggo bana bukata na fad'a miki ki kyaleni naci aljihuna bana fatan wata mace ta ciyar dani." Tace."To shikkenan bari naje na siyo kayan miyar da zanyi maka girkin."
Yace."Ki zauna ki huta duk zan had'o komai da zaki bukata gurin girkin." Shuru tayi tana kallonsa har ya shige gurinsu....Ta sauke ajiyar zuciya cikin ranta take masa fatan alkairi.
Tsaf tayi masa jallop din taliya irin ta mutanan da taji daddawa da manja da kifi sosai yaji dadin abincin ya dinga ci yana santi ita kuma sai dariya take masa dama haka take so ya sake ya cika cikinsa da abinci......Bayan ya kammala cin abincin a nutse ya kalleta da fad'in "Gwaggo ni zan fita nayi sallama da abokaina dan gobe da wuri nake so na tafi."
Tace."To shikkenan Jarumi sai ka dawo." Khalid yasa takalmansa ya fice daga gidan ita kuma ta juye ruwan zafin dake kan wuta ta surka ta shiga bandaki tayi wanka a gurguje ta shirya jikinta cikin atamfa (nicam) riga da zani da mayafi ta daura dankwalin (disco) a kanta pose dinta da dan mukkuli ta dauka ta fito ta kulle dakin takalmanta na dan'ko tasa a 'kafafunta ta fita daga gidan......Bakin titi ta fita tana addua akan Allah yasa kada ta hadu da Khalid din cikin ikon Allah kuwa har ta shiga adaidaita sahu bata ganshi ba.
Har bakin gate din gidan Alhaji Shamsu aka ajiyeta ta fito tana gyara lullu'bin mayafin atamfar dake jikinta, Pose din ta bude ta dauko dari biyu ta mika masa ya kar'ba tare da dauko hamsin ya bata a matsayin canjin ta.. karba tayi da sauri tasa a cikin jakarta tana masa godiya yaja babur dinsa yayi gaba.
Gate din gidan ta nufa ta bubbuga maigadin ya bude ganin kamar yasan fuskarta yasa ya gaisheta tace."Ina fata ka sheda ni ko."? Maigadin yace."Eh na sheda ki Gwaggo bisimillah shigo mana."
Gwaggo ta shiga gidan tana hamdala a cikin zuciyarta...............Gyaran kayan miya mukeyi da Asabe kawai naji sallamarta nai saurin daga kaina ina kallon bakin kofa. Ido muka had'a da ita tace."Babu shakka Sa'ida wato ke kina nan hankalin ki a kwance kin bar mu cikin damuwa ko."?
Bagarar da maganarta nayi nace."Gwaggo sannu da zuwa ki shigo mana." Tace."Ai ko baki fad'a ba." Asabe na murmushi ta gaisheta ta amsa tana bin gurin da kallo sai ta'be baki take.
Sanin halinta yasa nayi saurin mi'kewa da fad'in "Shigo mana." Ba tare da tace komai ba ta biyo bayana...Ummah kawai sai ganin mu tayi a tare.
Da sauri tace."Gwaggo kece kike tafe da yamma haka."?
Tana kokarin cire takalmanta domin shiga falon tace."Aikuwa dai nice nake tafe ko dai ba'a maraba dani."?
Ummah Habiba tace."Aa Gwaggo ana maraba dake shigo ga guri ki zauna." Ta shiga ta zauna kan kujera tana gyara yafan mayafinta.
Cikin mutunci da girmawa Ummah ta gaisheta ta amsa babu cikakkiyar walwala a tare da ita.
Nace."Gwaggo sannu da hanya." tayi saurin fad'in "Ai bazan amsa gaisuwarki ba Sa'ida tunda kin nuna mana iyakarmu."
Nace."Gwaggo wace irin magana ce wannan."? Fashawa tayi da kuka tace."Wato Sa'ida saboda Ibrahim bashi da kudi baya baki shayi da biredi baya siyo kayan miya da nama shine kika tattaro kayan ki kika gudo gidan mijin mahaifiyarki to komai talaucin mu mune gatanki sabida haka 'kafata k'afarki zamu koma gida dan ba zan zauna ayi min 'karfa-'karfa ba."
Cikin aljabi da mamaki nake kallonta lallai Gwaggo ta iya sauya lamari wato tanan ta 'bullo kenan."
Umma Habiba tace."Haba Gwaggo banji dad'in wannan magana ba wallahi Sa'ida bata da gata sai ku kuma duk rashi da taulacin Kawunta bai gaza da ita ba yana iyakacin bakin kokarinsa akanta to me zai sanya kiyi wannan maganar."
Shuru tayi bata tanka ba.Umma Habiba ta cigaba da cewa" Sa'ida tazo gidan nan jiya da daddare cikin damuwa da tashin hankali ta sheda min irin cin mutuncin da Ummatu take mata wannan dalilin yasa nace ta zauna ta huta idan ta samu nutsuwa sai ta koma."
Gwaggo tace."Eh hakane abinda tazo ta fad'a miki Ummatu taci mutuncin ta amma kuma Kawunta Ibrahim ya dauki mataki dan yanzu zancan da nake miki Rabi tana gidansu kuma yace ba zata dawo ba sai Sa'ida ta dawo saboda haka idan ke 'yar halak ce sai ki had'a kayanki mu tafi gida idan kuma kikayi sanadiyar raba auran Ibrahim da matarsa to zaki shiga bakin duniya."
Sa'ida da mahaifiyarta jikinsu yayi sanyi! Gwaggo ganin duk jikinsu ya mutu sai taji dadin hakan ta cigaba da zuzuta al'amarin.....Ummah Habiba tace."To shikkenan Gwaggo magana ta 'kare Sa'ida zata biki amma sai mun jira Maigidan ya dawo."
Gwaggo wani irin kallo ta watsa mata a fusace tace.....
*Masoya a taimaka da sharing??????*
*IDAN KINA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE.....VIP GRUOP#600 NORMAL GRUOP#300....ACCOUNT.0542382124....BINTA UMAR GTBANK.....IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER*
*07084653262*
*08089965176*
*BINTA UMAR ABBALE*
*GA IRINTA NAN!!!?????¡â?*
_(LOVE STORY??)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE??_
*MANAZARTA WRITES ASSO?????*
*MUTANAN NIJAR IDAN KUNA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA NUMBER DA ZAKU NEMA......22790899076*
*SADAUKAWA NE GA IYAYE BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*
_*Hakika ina alfahari dadu Iyayena??????*_
*16&17*
*'KARSHEN FREE PEGE*
"Wane irin sai maigidan ya dawo kuma Habiba kina nufin zanyi ta zama a gidan nan har sai mijinki ya dawo ya bada umarni."? ta'karashe maganar tana hararar ta.
Umma Habiba taji rashin dadin maganar Gwaggon amma sai ta daure ko a fuska bata nuna ba tace."Gwaggo abinda nake nufi kenan a bari ya dawo a bashi hakkinsa a matsayinsa na mijina tunda tamkar uba yake a gurinta saboda haka dan Allah kiyi hakuri kada ki dauki maganata da wata manufa ta daban."
Ta'be bakinta tayi tace."Saboda kawai nice sarkin zargi sai na dauki maganarki da wata manufa shikkenan ai tunda kince haka sai na zauna na jira shi ya dawo na dai fad'a miki 'kafata 'kafar Sa'ida dan ba zan yarda da raina da lafiyata jinina yayi agolanci a wani guri ba."
Cikin takaici nace."Wai Gwaggo wace irin magana ce wannan kike yi dan Allah kiyi shuru haka ki daina d'aga mirya da tada jijiyar wuya magana ta 'kare zan koma gidan ko dan saboda Ummatu ta dawo d'akinta."
Shuru tayi min ba tanka ba. Umma ta sauke ajiyar zuciya da fad'in "Ai maigidan ma yana kan hanya shida na yamma suke dawowa daga kasuwa."
Tace."To Allah ya kawo su lafiya." Umma Habiba ta amsa da "ameen tare da mi'kewa domin fita daga falon Gwaggo ta dakatar da ita, da fadin " Nace ko kina da goro ki bani wallahi garin sauri na manta nawa a gida." Tace."Gwaggo ni bana cin goro amma bari na tambayar miki Hajia Hansatu.'' tana nufin uwargidansu. tace."To nagode Habiba ina jira wallahi sha'awar cinsa ce ta taso min a yanzu idan ma babu a gurinta ga kudina a siyo min."
Umma Habiba tace."Ba za'a rasa ba insha Allahu bari na tambayar miki ita." Fita tayi daga dakin da sauri.
Nace."Gwaggo ba zaki daina cin goro ba ko."? Kallona tayi cikin kulawa tace."Sa'ida ai ina jin sai ranar da numfashi ya bar gangar jikina zan hakura da goro ya zame min masifa ni kaina so nake na daina amma na kasa."
Nace."Abu ne da kuka sanyawa ranku wanda kuke ganin idan baku ci ba wata matsalar zata iya faruwa daku kuma ba haka bane da zaku yi sati guda baku ci ba babu abinda zai same ku sai ma lafiya da kuzari da zakuyi amma dan jaraba kuyi ta cin abinda zai cutar daku."
Shuru tayi bata ce komai ba. nasan duk surutan da zanyi akan al'amarin ba zata d'auka ba cin goro ya zame mata jinin jikinta.
"Gwaggo zan koma gida amma da akwai sharad'i." Da sauri ta kalleni, na sha kunu da fad'in "Kiyi min tsakani da Khalid babu ni babu shi yaron bai da kirki da tarbiya akwai abubuwan da suka faru a tsakaninmu wanda idan na fito na fad'a miki hankalinki zai tashi ko kuma ma kice nai masa sharri to wannan dalilin yasa nayi shuru da bakina inaso ki zauna dashi kija masa kunne sosai ya fita daga sabgata maganar yana sona ya ajiyeta a gefe guda dan na rantse ba zan aureshi ba koda kuwa zan rasa mijin aure keda kike goya masa baya akan lamarin ki cire kanki domin ke zakiji kunya. abu na biyu kuma kina d'ora min lalurar aljanu ni lafiyata kalau kamar yanda nasha fada miki aure lokaci ne sabida haka Uwale ta daina janki gurin masu magani kina asarar kud'in ki bayan haka kuma idan kin san akwai ragowar wannan turaran da kike turnuk'awa a daki to da mun koma ki zubar dashi dan wallahi duk ranar da kika sake kunnawa zan bar gidan kuma komai abinki ba zan dawo ba guduwa ma zanyi ku rasa inda na nake.
Gwaggo gabanta ya fad'i! ta tsira min ido nace." Wallahi Gwaggo wannan maganar da nake miki har cikin zuciyata nake miki ita Khalid ba tsaran aure na bane ki daina tatsuniya ba zan aureshi ba sannan ni lafiyata kalau aure kuma lokaci ne insha Allah cikin satin nan Alhaji Nura zai turo da magabatansa.
"Sa'ida meye aibun Khalid da zaki dinga gudunsa ko dan bashi da kudi ne."? A sanyaye take