Showing 240001 words to 243000 words out of 280244 words

Chapter 81 - AUREN HUCE HAUSHI complete

07 Feb 2026

1099

da abinci.
Bayan magariba kadan Aunty Aishat suka shigo da abincin lokacin Zahra na sama tayi wanka tana shiryawa, wata Riga ash colour ta saka irin ta mutanen Kuwait tayi rolling da veil din sai tayi wani irin kyau Dan yanzu ne kwarjiinin Amarcin yake bayyana a jikinta.
Saman Aishat ta haura tabar su Radeeya a kasa,sau Daya tayi knocking zahra ta bada Umarnin shigowa.
Suna arba da Aishat zahra ta rugo kamar yarinya ta shige jikinta tana fadin " Aunty Aishat nayi fushi idan ke bazaki zo ba ai saiki bada a kawo min Afnan Mana duk kewarta da dameni tana Ina ne dan Allah?".
Kan sofar dake dakin suka zauna Aishat din na fadin
"Afnan sunje Usman Dan fodio teaching Hospital dubiya, Inna Maimuna ce ta goyata kinsanta da son yawo".
"Su Inna kuma,to waye bashi da lafiya?"
"Naji dai suna cewa Mama kinsan ba sanin mutanen nayi ba".

" Ayya! haba shi yasa babu Wanda yazo gurina,Saida na gaji na Kira Aunty Hasana Amma kin fada min tayi sai cewa tayi zasuzo suna da wasu uzururruka ne Ashe Mamace jikin yaki Dadi Allah ya Bata lafiya".
"Allahumma Amin".
Aishat ta fad'a tana kallon zahra, kokonto ne ya darsu a zuciyar Aishat yanda taga zahra na Yan guje guje nan tasan ba'a gamu ba Amma saboda ta tabbatar saita cewa Zahrar.
"Dan Allah dauko min turarenki na gani Yana yi min Dadi sosai".
Tsam ta miqe Ras ta tafi ta dauko Mata su ta kawo Mata Aishat din ta dauka tana Kara shinshinawa tana kwarzanta kanshin su.
Handbag dinta ta dauki ta bude wasu kwalabe ta dauko tana murmushi sai wani kuma Karamin daurin magani a cikin irin ledar da ake zuba tablet a asibiti ta Mika Mata tana fadin "gasu Nan inji mummy Badi'a ta dauko wani turare Mai colour purple tace "Kinga wannna ki shiga toilet ki dan shafa a kirjinki da kasan mararki sai kuma wadannan guda biyun duka jikinki Zaki shafe dasu, wannann kuma ki zuba Madara ki Sha yau da gobe da jibi ya wadatar, Bari na dauko cups na hada Miki".
Zahra duk a kunyace take da Aunty Aishat din, ita mamaki take Bata tamkar ba dangin miji ba ita gani takeyi wallahi Kamar Aunty Hasanarta. Aunty Aishat ce ta tashi ta nufi kofa ta fice.
Bata Jima ba ta kawo cups da ruwa da farm fresh da Hollandis free mik, Aunty Aishat din da kanta ta hadawa zahra maganinta da Holladia ta Bata ta Shanye, Bata kayan tayi tace ta Adana kada ta Bari ko mahmud ya gani turaren na Mata ne kawai.
Kai ta gyada Mata tana Mata godiya, kasa suka sauko tare da Auntyn sai wurin 8:30 mahmud da Sameer suka shigo gidan, Sameer na ganin Hajiyar makwarari yayi turus Yana kallonta cikin madaukakin mamaki.
"Yanzu saboda Allah Baki bi su Rukayya ba Kika koma gida? to ko zaman daki zakiyi musu ne? Oh yau Naga ikon Allah gaskiya ko haihuwa tayi Allah bazan kowaki garin nan ba tunda baki iya cin Dan wake Mai yaji ba sai kin fantsama a ido, gaskiya gara da Allah yasa 'ya'yanki maza basa kusa dake da rawar gaban hantsi zaki Hana su wallahi, kawai kizo ki nemi guri ki zaunawa yarinya kina ganin shige da ficenta dan ki hanata watayawa kawai".
Tafi da sallallami Hajiyar ta dauka tana fad'in. "Yau Naga abinda ya isheni kaida ba gidanka naje ba ballentana kace nayi maka ba dai dai ba, su an fada maka irin kane zalamamme Wanda baya kauda Ido akan matarsa ai ban mance abinda kukayi min ba Ina zaune kuka kwakume juna kuna tsotse-tsotse ba kunya ba tsoron Allah saini na bar muku gurin, Amma kaga su da yake Allah yasa suna da ta Ido ko hannunta kaga ya rike a gaban mu eyeh?" . mahmud ne ya matso kusa da Hajiyar Yana fadin.
"Hajiya barka da dare, Dan Allah rabu da Sameer baya son zaman lafiya ai Nan dai gidana ne idan ma kin amince Zaki zauna har iya rayuwa kiyi zamanki daki ma sai Wanda Kika zaba zaki zauna".
"Allah yayi Albarka ko yanzu ka nuna min Kai cikakken d'ane na halak, Daman Kai nake jira ka mayar Dani yau can gidan ku Zan kwana ba gurin Hajiya Inna ba".
"Ok Bari na shirya sai muje na kaiki Nima ban shiga ba Nan nayo ya fada Yana nufar stairs da sauri yayin da Aishat tabi bayansa da sauri, Saida suka bacewa ganinsu Hajiyar ta kalli Zahra tana tabe Baki "ke Kuma miji ya dawo Kika nemi gurin Zama kamar wata kud'd'a marar wayo, baki ga ita 'yar uwar tasa ta bishi ba? Maza tashi ki bishi kinji ba'a sake da Lamarin miji".
Su Radeeya dai sai dariya suke musu suna daga d'ayan parlourn Dan da alama wannan har tace Hajja Bata iya ba.
"Yo ta Ina zata iya binsa kin kasa kin tsare kin hanata sakewa da mijinta".
Sameer ya fada a kule.
Shiru tayi masa Bata Kara tanka Masa ba.

Aishat Bata Jima ba ta sauko tana fadin "Sameer Bari mu wuce mukam Saida safe".
Tsam Hajiyar ta Mike muje ki tafi dani kada wannan Mai dacin ran ya kifar Dani a hanya yanda yake cika Yana batsewa baza'a haifi da Mai Ido ba".
Har gurin mota Zahrar ta rakasu tana rike da babbar jakar data hadawa Hajiya nata kayan harda na makotanta ta Bata Wanda take ta Kira ana yiwa zahra Allah Sanya Alkhairi, Saida suka wuce ta dawo.
Tana dosar kofar Sameer da shi suka fito,Sameer din rike da wasu files a hannunsa shi Kuma Dan gogan yana waya da wani yare Wanda Bata San ko wane yare bane. Rab'awa tayi zata wuce yayi ram da hannunta Yana binta da wani mayen kallo, marairaice Masa tayi tana Masa nuni da oga Sameer Amma ya fuske saima k'ok'arin mannata a jikinsa da yakeyi.
Wani killer smile Sameer yayi ya Kara gaba Dan yaga alamar ogan nasa sai a Hankali yau wuni yayi sakarwa kansa ruwa, Saida ya Kare wayar sannan Sameer ya dawo da laptop a hannunsa Mika Masa hannunsa dayan yayi ya saka Masa ita ya juya Yana fadin. "Good night".
Motarsa ya fada Yana sakin murmushi, a fili yace "wallahi ka shiga cikin tsarin dai sai yarinyar Nan ta goge maka hadda tas kazo kana sakin layi a gaban mu, Mata! Mata! Hummm ayi dai mu gani".
Ya figi motar ya fice daga gidan ai Kamar jiran ya fice mahmud yake yi ya wani juyo da ita Yana faman shinshina jikinta wani irin kamshi yakeji Yana fita daga jikinta Wanda yake bijoro Masa da wani irin feeling na tashin Hankali, hannunsa ko Ina yawo yakeyi a jikinta da kyar ya saurara mata suka shige ciki a daddafe sukaci cus-cus da vegetable soup sai wani nama Mai ruwa-ruwa da yaji spices da seasoning sai tashin kamshi yakeyi, kwanukan da suka Bata ta dauke ta shigar dasu kitchen sannna suka haura sama Yana rungume da abarsa suna shiga ya wuce toilet yayi wanka duk da kafin ya tafi sallar magariba Saida yayi wankan, tana zaune ya fito daure da towel fari sol a kugunsa Yana goge jikinsa da karamin Shima fari ne.
Lotion kawai ya shafa ya nufi clothset dinsu ya sako t-shirt Navy blue da trouser milk Mai haske na kamfanin Armani ya nufota Yana zuba kamshinsa na gado, hannu kawai ya Mika Mata ta Kama ta Mike Bai wani Bata lokaci ba ya kashe wutar dakin suka fito ya daddanna wasu numbers suka mufo down stairs. Wani Dan Abu ya Danna Kamar switch din kunna wuta sai gurin ya bude keys ne a gurin masu yawa Daya taga ya dauko har ze kashe wutar kitchen ya juyo motsin mutum sai lokacin suka tuna da yarinyar da Ammi tasa aka kawowa Zahra ita Kuma Aunty zilai su Aishat tabi tace sai an kwana biyu zata dawo duk da haka ta fadawa Ammi bazata ke kwana a can ba.
Ita dai ikon Allah take kallo ta kofar Baya suka fice parking lot ya nufa Yana rike da ita har suka karasa.

AUREN HUCE HAUSHI_*

AISHAT ISAH MUSAH

(Maman Fateemah)

09061432330

08055362975



Page 86.

........... Da kyar ya lallabata sukayi sallah sai kananun koke-koke take masa, cak ya daukota ya Dora a gadon Yana cire mata hijab din daya saka mata, cikin jikinsa ya sakata yana Dan shafa bayanta a hankali tana ta sauke ajiyar zuciya, duk ta dagula masa lissafi Dan shi kansa dauriya ce kawai kada ayi haihuwar guzuma 'ya kwance uwa kwance, dan zazzabin jikinsa Shima k'aruwa yakeyi, sunanta ya Kira very softly,Bata amsa ba sai Kara shiga jikinsa da tayi tana Dan rawar sanyi tare da rik'e hannunsa tana cije lips dinta na kasa
"Pls... precious forgive me,you make me lose my control, iam so lucky to have you... Precious you're special, i love every part of you, every time with you is specia I love you.. Ilove you with all my heart..
Kiran Daya shigo wayarsa shiya dakatar dashi daga abinda yayi niyyar fada.
"Kizo Dan Allah Ina mabera sabon parta din Nan, da fatan Kinga text message dina?".
"Eh na gani gamu munzo da doctor zainab din Saida na biya na daukota motarta ce taqi tashi".

"Ok, ku shigo kawai kofar a bude take".
Rigar jikinta ya gyara Mata, sannan ya tattare gashin ya saka masa band ya hade shi a tsakiya ya sakeshi baya. Kalamansa sun tsaya Mata a zuciyarta, mamakinsa ya girmama a gurinta idan ta kalleshi sai taga Kamar bashi bane totally ya canza mata, wani sabon Mahmud take gani ba ainishin wanda ta sani ba.
Suna daf da karasawa kofar da zata sada ka da babban parlourn suka tsinkayo muryar Hajiya Inna tana fadin. "Kai su wanene haka da asubar fari suka shigo min gida babu sanarwa? me zakuyi a Nan? to babu kowa a cikinsa da kuka nufa kuna ta sauri Kamar masu amsa Kiran fada, ai Ina Jin karan shigowar mota na leko Naga kun nufo Nan yasa na fito bansan mahalukin Daya bude min kofar bama" .ta karasa fada tana kusanto su Aishat din.
Dr zainab ce ta gaisheta, sai lokacin ta gane doctor din tunda itace family doctor dinsu.
"A'a likita lafiya Kika zo Mana da sanyin asuba nan Ina ga kinyi makuwa kuwa ai Nan babu kowa kinibibin ne yasa aka gina shi kawai Dan fariya, yo inba fariya ba yaushe za'a kashe irin wanan dukiya a banza".
Aishat ce ta matso tana fadin.
"Dan Allah Inna ki koma ki kwanta mune ba wasu baqin Ido ba, zamu shigo gurinki yanzu wani uziri ne ya kawo mu, doctor Bismillah".
Tsaye Hajiya innar tayi tana kallon Aishar tana ayyana wani Abu a cikin ranta.
"Shatu, waye babu lafiya a gidan nawa Wanda ni ban sani ba saike da kike wata unguwar Kika sani?".
"Dan Allah ki barta muje daga baya nayi Miki bayani".
Ta nufi kofar doctor zainab na biye da ita da sauri, ai itama hajiya Bata tsaya neman wata maganar ba ta rufa musu baya tana fadin. "Muje Naga ikon Allah, tunda abun ya Zama na Qumbiya-Qumbiya Kuma".
Suna shiga dukkansu Saida suka girgiza da ganin yanda aka qawata part din ba qananun kudi aka narkar ba a cikinsa, cikin corridor din ta nufa Kamar yanda ya fada Mata a hankali tayi knocking daga ciki ya Basu Umarnin shigowa.
"Masha Allah!!"
Abinda bakinsu furta kenan lokacin da suka shiga da sallama, saboda babu Qarya ko Mai hassadar mutum saiya yaba bedroom din Nan, suna Kan gadon tana jikinsa, da sauri Hajiya Inna ta natso tana fadin "me Zan gani Mahmudu? Daman Baku tafi ba a nan kuka kwana? Ikon Allah meya sameta Naga lfy-lfy mukayi sallama daku".
Dan dafe kansa yayi Wanda ke Sara Masa, ya dago idanunsa Yana kallon Aishat da alamar tuhuma a cikinsu.
Basarwa tayi tasan dai maganar Daya ce meyasa ta tado Hajiya Inna, ita Kuma tasan karambaninta ne yasa ta fito Kuma tasan ba komawa zatayi ba shi yasa ta rabu da ita kawai.
Doctor ce ta matsa suna gaisawa da Mahmud Wanda har lokacin kanzil Bai cewa Hajiya Inna ba.
"Lfy kalau doctor".
Ya amsa gaisuwar,Zahra kuwa lif tayi ta rufe idanunta Kamar me barci Dan ji tayi bazata iya hada Ido da Hajiyar ba.
'Yallabai ku dan bamu guri na dubata ko".
Kanta ya zame daga kan cinyarsa ya mike Yana fadin "ok doctor Dan Allah a dubata sosai jikinta yayi zafi da yawa, muje ki fada min meya fito dake yanzu da sanyin asubar nan?".
Ya riko hannaun Hajiya ji tayi Shima nasa jikin yayi mugun zafi.
"Yo ai kaima ba lafiyar gareka ba, yau Naga abinda ya isheni,Ina cikin gida Amma ka kasa fada mini meye amfanina kenan? Maza lalubo min Babanka ya turo likita ya duba min Kai yaushe za'a zauna da ciwo a jiki".

Suna ficewa Aishat ta karaso kusa da Zahra ta zauna wadda har lokacin idanunta a rufe suke.
"Sannu zahra, ki tashi nasan idonki biyu ga doctor tazo ta dubaki kinji".
Rinannun idanunta ta bude ta kalli Auntyn Nan da Nan taji idanunta sun kicciko.
"Aunty Aishat Dan Allah kirawo min Aunty Hasana".
Sai hawaye sharrrr... Suka biyo kumatunta.
Hannunta farare sol Aunty Aishat ta rike tana girgiza Mata Kai.
"Pls ki daina kuka gashi Nan za'a dubaki".
Kanta kawai ta iya gyada Mata.
Tashi Aishat din tayi tana fadin "doctor Bari Naga bros".
Tayi waje tare da ja musu kofar tana Jin tausayin zahra da gani Bai saurara Mata ta ko kadan.
"Sannu Daughter kinji Bari na duba na gani sai asan abinda za'ayi Miki, hands glove ta saka ta umarci zahrar ta gyara ta dubata.
Jikinta tsima ya Kama da kyar ta Bari doctor zainab din ta dubata cikin ikon Allah Bata karu ba sai dai gurin Kam sai a hankali, dan Allah ya taimaketa jikinta irin roba din Nan ne Wanda ko haihuwa masu irin jikin sukayi Basu fiye budewa ba, jikin ba gautsi, a cikin Mata dari da wuya ka fitar da goma masu irin wannan halittar.
Ruwan zafi ta shiga ta hada Mata da kanta ta sakata tana hawaye tana komai, Saida ya canza Mata sau uku cikin ikon Allah sai taji jikin Yayi Mata Dadi fitowa doctor din tayi zahrar tayi wanka ta fito simple Riga ta Bata ta saka sannan ta leka ya fad'awa Aishat ta hado Mata tea Kofi daya ta koma a kitchen din bangaren ta hado saboda babu abinda babu a ciki.
Tea me kauri sosai ta hado Mata a gefen gado ta Samu zahrar tana Zaune yayin da doctor ke hada wasu allurai.
Hajiya Inna ce keta fada akan Mahmud yaki Kira Mata Abbie dinsa ya Kuma Hana Aishat ta kirawo Mata shi.
"Dan Allah ki tashi ki koma Zan Sha magani kawai, nifa lafiya ta kalau kawai dai bana Jin Dadi ne".
Cikin hukuncin Allah saiga kira ya shigo wayarta alamar mota data gani tasan Mustapha ne da sauri ta dauka Kota Kan sallamar da yake Mata Bata bi ba ballentana ta Sami zarafin amsawa.
"Kanaji na Mustapha maza ka taho da likita gidana tunda Aliyu baya gari ya duba min Dan biyu gashi Nan Zazzabi Yayi Masa rigijib ko daga Kai baya iyawa" .
Ta kashe wayar, Baki bude Mahmud yabi Hajiya Inna da kallon mamaki Wai ko Kai baya iya dagawa "ikon Allah".
Can Kuma uncle Mustapha suna tare da Abbie tun bayan da aka fito masallaci suke Zaune a harabar masallacin suna hirar zumunci shine uncle Mustapha ya Kira Hajiya ta tambayeta ko akwai abinda ze taho Mata dashi Dan daga Nan can gidanta ya nufa.
Yayansa ya kalla Wanda shima shi yake kallon domin wayar a speaker take.
"Ikon Allah meya Kai Mahmud kuma gidanta shida ga gidansa can, ko Kuma da yaji ciwon ne ya tafi can kasan shida ita tasu Bata baci".
Uncle Mustapha ya fada.
"To waya sani ka Kira doctor Anka sai ku hadu a can ya duba shi".
Sallama sukayi Abbie ya nufi cikin gidan Yana kokarin Kiran Ammi, yayin da uncle shima ya nufi motarsa ya shiga Yana kokarin lalubo number doctor Anka din.
Allurai kusan Kashi uku ta yiwa zahra wadda Saida Aunty Aishat ta riketa akayi Mata sannan ta Bata Analgesic table ta Sha ta bawa Zahra wani tube na cream tace ta shafa a can da Kuma Kan breast dinta inda shima ya dade, ta Kuma jaddada Mata shiga ruwan zafi Kamar sau biyu kafin dare Dan yanda gurin yayi sai a hankali kawai Dan ma dai Tana cikin Wanda ubangiji Yayi musu special gift da labarin ba wannan akeyi ba.
Tare da Aishat suka fito suna Nan second parlour shida Hajiya innar sallama tayi musu tana fadin "yallabai in ganka mana".
"A'a babu inda zaya shima ba lafiyar ce dashi ba,ko meye Fadi Masa a gabana ai ba kunyata yakeji ba tunda ya tsallake gidansa yazo gidana ya taki matarsa ai shikenan Daman ya fada min".
'kai! Hajiya you have a lot problem wallahi, doctor muje gaskiya kina da damuwa wallahi".

Yayi gaba ya nufi parlourn farko.
"Yo saika Hana na fada ba haka ka fada min ba?".
Ita dai Aishat Bata tanka musu ba, tasan sunfi kusa koka shiga kaji kunya bare ita da ba inuwa daya suke Sha ba.
Godiya sosai Mahmud ya yiwa doctor zainab din a Nan take fada Masa ya Dan d'agawa zahrar kafa zuwa two to three days haka Dan ma Allah yasa babu ciwo masu yawa.
Key din mota ya mikawa Aishat ta Bata tana parking lot sannan yace ta bawa Aishat account number.
Godiya take Masa Kamar zata zube masa a Qasa yi take tana karawa Kamar zata Ari baki, itama Aishat din ta tayata yi Masa godiyar, komawa Yayi ciki kawai shi baiga wani abun yiwa irin wannan godiyar ba.
A sabuwar motarta doctor zainab ta koma murna kamar me Dan tasan wata Rahama ce ubangiji Yayi Mata, motarta tafi kwanan wata biyu tana fama da ita yanzu haka tana Kan cinikin wata motar jira kawai take a Bata adashenta ta Saida tata ta hada kudin ta tura musu a kawo Mata motar Sai gashi cikin hukuncin Allah da sanyin safiya tayi Gam da katar da motar da Nan kusa Bata tab'a tunanin mallakar mota irinta ba ta millions of naira.
Direct bedroom din ya wuce ji yake kamar ya cire mata ciwon daga jikinta, lokaci bayan lokaci Yana sakin smile shi kadai, mamaki yake yi Wai Daman haka lamarin yake ya tsaya Yana cutar da kansa a banza ai da yasan haka ne da gara yayi tun tuni yayi kaffarar rantsuwar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login