Showing 234001 words to 237000 words out of 280244 words

Chapter 79 - AUREN HUCE HAUSHI complete

07 Feb 2026

1029

wani sabon mahmud take gani ba Wanda ta sani ba.

Ya tambaya Yana kokarin zare Mata Alkyabbar gaba Daya daga jikinta wani fitinan kamshin ya mamaye shi, ga wani mahaukacin feeling da yaji Yana fusgarsa zuwa gareta, kankameta ya karayi a jikinsa da gaske ya shiga wani yanayi,ba Karamin yak'i yayi da zuciyarsa kafin ya sassauta Mata rikon da yayi mata Yana maida numfashi.

Alkyabbar ya aje gefen gadon ya Zama daga ita sai wata rigar atamfa wadda akayiwa wani fitinannan dinki Wanda ya fito Mata da ikahirin halittarta ta kirji zahiri, yabi shafaffen cikinta abinda ya Kara fallasa asirin kirjin nata kenan da suke a cike tsan-tsan, ai baisan lokacin Daya Kara mannata a jikinsa ba Yana fadin "Ashe wannan abar ba Karamin sitirtamin kayana tayi ba" Yana Kai hannunsa gurin.
Dan zabura tayi ta rike hannunsa ta shagwab'e Masa fuska tare da juya Masa sexy eyes dinta
"Please meu amorrr.....ba kyaufa ka Bari Dan Allah".

Saitin kunnenta yayi magana a hankali..

"Meye ba kyau din fada min abinda nayi Daya sabawa shari'a? Ina son Jin tempareture din jikinki ne naji kamar tayi high".
"A'a...ni lafiya ta qalau".
"Ok, to bari nazo".
Ya fada Yana gyara Mata zip din rigar, fuskarta ya dan shafa kadan tare da Bata wani light kiss a gefen wuyanta Wanda yasa tadan fitar da wani Karamin sound da yaso ya Hana shi fitar.
Babbar rigar ya cire ya aje a kusa da ita Yana nufar kofa ya fice, Dan kwanciya tayi a gefen gadon tana Jin wani Abu Yana circulating a cikin jinin jikinta.
Bai Jima ba ya dawo dauka da Leda Mai tambarin na Maru suya spots, da plates da sauran tarkacen su knife da cups da su forks, a kan Karamin Conner table ya Dara idanunsa na Kan Zahra wadda ta lumshe Ido tana sauke numfashi a hankali,wani special smile ya saki yana godewa sarki buwayi gagara misali da yayi Masa irin wannan kyautar, Saida ya aje komai sannan ya nufeta ya tsuguna dai dai saitin fuskarta Yana dan shafawa a hankali narkakkun idanunta ta bude tana kallonsa.
"Oya tashi kici abinci".
Ta lumshe idanun tayi. "I am ok fa, bana Jin yunwa barci nakeji".
Bai saurareta ba ya saka hannu ya dagota daga kwancen Yana fadin "Ni nagano yunwar a tare dake".
Nama ne Wanda ita dai bazata ce ga yanda aka sarrafa shi ba, ya gyara hannun rigarsa ya Fara Bata tana mitar ita ta koshi Amma Bai barta ba Saida ya tabbatar da ta koshi sannan ya dauko Mata mutuniyar farm fresh ta strawberry ya cika cup ya kafa Mata a Baki ta Sha rabi ta kawar da Kai kamar yanda yaran goye sukeyi idan suka koshi da Abu.
"Pls precious ki shanye mana farm fresh ce fa, ko kin daina yayinta ne? Naga tunda mukazo kabi nema ba alhalin an cika Miki store da ita".
A shagwab'e ta dago sexy eyes din ta tana Masa wani kallon Daya nemi jefa shi a wata nahiyar.
"Nifa na koshi kamar na cikin mafa ze dawo nakeji".
"Ok. Shike Nan Bari na dauke kayan sai ki shiga kiyo Alwala kafin na dawo".
Har ya kai kofa ya tsinkayo maganarta tana fadar "pls naga zaka mayar Kai bakaci komai ba".
Kafeta yayi da Ido Yana nazarinta "Da kina son naci ai da kin bani, amma Baki bani ba tunda na dauke kuma sai wani jikon Wanda kikaci shikenan is enough for us, koba haka ba?".
Ya dage Mata gira ya fice.
Tsam tayi da ranta tana hasaso mezeje yazo, ita fa duk lamuransa sun tsaya Mata a Rai yanda ya downgrade din kansa a Azare da yanda ya ringa mu'amalantar Almajiran malam, a yayin zamansa a can, ita fa gani take wallahi yanzu yafi karfin ajinta nesa ba kusa ba duk da tasan itama yes ba karya Ubangiji ya Gama Mata gata ya dauke Mata iyaye Amma cikin Rahamaniyya tasa saiya saukake Mata duk wani tsananin rayiwa, duk da Tasha badaqala a baya sai gashi ya zama tariihi.
Allah be Bata ikon tashi ba har ya dawo, ruwan dake hannunsa na laimar alwala ya Dan yarfa Mata sai tayi figigit tana sauke ajiyar zuciya.
Gaba yayi ya nufi kofar da take tunanin toilet ne, ta Mike a hankali tabi bayansa hanya ya matsa ya Bata tare da fadin "shiga kiyo Alwala Ina jiranki".
Ya juya ya fice daga dakin, brush ta bude sabo ya wanke bakinta sannan tayi alwalar gurin mirror ta nufa ta karewa kanta kallo, wallahi tausayin kanta da kanta takeyi tasan sai yanda hali yayi Dan ita kadai tasan me take hangowa a cikin idanunsa.
Tana tsaya taji alamun za'a bude kofar tayi saurin barin gurin, Yana budewa tana zuwa bakin kofar jallabiya ce sabuwa fara Kar a jikinsa sai Zuba kamshinsa nan nasa na musamman yakeyi, hannu ya Miko Mata yana sakin murmushi Yana fadin "inye 'yan matan gidan mahmud Dange, yarinyar Nan kina yanda kike so da Dan malam din Nan wallahi sai cika kike kina batsewa irin kada a kawo Miki wargi din nan ko?".
Kauda Kai tayi tana sakin murmushin ta Mai shagaltar dashi "Ni wallahi ka Bari idan wani yaji saiya dauka haka ne fa".
Hannu ya rike ta fito daga toilet din.
"To da karya na fada ba cikar kike kina batsewa ba kawai Dan ki Sara min allo ki hanani rawar gaban hantsi ni da halaliyata za'a hanani dama daddawata da moda".
Ya fada Yana kafeta da tsumammun idanunsa, sadda kanta tayi kasa Dan abinda take gani a can baya ta gani yau muraran a idanun nasa ta rasa wane irin abu ne da yake sakata a rudu haka.
"Muje muyi sallar".
Hijab taga ya dauko Mata fari sol dashi Mai laushi irin na mutanen Indonesia din nan ya zura Mata,Yana janye da hannunta suka nufi wani guri kamar space din da ake saka dining table suna zuwa taga an yi gurin ne domin ibada kawai ba Bata lokaci ya shige gaba yaja musu sallah, raka'a biyu yayi musu yayi sallama ya Jima Yana musu Addu'oi da harshen larabci Wanda har Saida zahra ta dago da kanta ta Zuba Masa idanu tamkar shine Dan mun gada din, a hankali ya matso inda take saune ya dafa kanta ya ringa kwararo Addu'a, Nan da Nan jikinta ya hau tsuma sai kuka Dan Allah ji tayi tamkar tafi kowace mace sa'ar samun miji Mai addini Dan Bata taba tunanin iliminsa ya Kai haka ba tun a wancen lokacin bare kuma yanzu da taga ra'ayal ainiy.
Sai da ya Gama Mata Addu'oin sannan ya daukota cak ya rungume abarsa Yana fadin " pls precious kinsan bana son kukan naki ko? Ki daina kuka babu abinda Zan Miki ki saki jikinki Dani kinji, Nima na gaji sosai babu abinda nakeso sai nayi barci na huta ai kin gane".
Kai ta gyada masa tana Kara lafewa a jikinsa tamkar mage, ya yarda yayi amanna itace weakness din da gaske Dan ji yake baze iya matsamata ba gurin sex Dan ya fuskanci tana zulumin abin ba kadan ze da raka da ita ta Kara sakewa yasan duk runtsi ba za'a dauki lokacin da sukayi a baya ba.


*****Kuka take tamkar wadda akayi mata babban rashi irin na iyaye,duk iya ban baki Salbiyya babbar hadimar Fulani tayi Mata Amma kamar tana Kara tunzira ta, dan tayi masifar kwallafa ranta a Kan mahmud, guyn yayi Mata karshe taci burirrika masu yawa a Kansa,tun bayan dasu Ammi suka dan tattauna a kan yuwuwar hadasu aure bayan samun matsalar data kusan rusa farin cikin da yawa daga family din nasu mahmud.
Tashi Salbiyyar tayi tana fadin "Bari na Kira Giwar Mai martaba tazo taga halin da kike ciki kada ciwonki ya tashi mu shiga uku"
Ta dauko wayar ta tana kokarin Kiran Fulani, da sauri Insiyya ta rik'e hannunta tana girgiza Mata kai saboda kukan da yaci karfinta.
Fasa Kiran tayi itama barazana ce saboda lokacin kusan Daya da minti goma, daren ya Fara nisa bazaso ta daga Hankalin uwar gijiyar tata ba.
"To ya kike son naji Miki ranki shi dade? sai Abu Daya kikeyi tun dawowar mu daga gidan Amaryar Nan Kika birkice min kink'i ki fada min damuwarki ko ina da abinda Zan taimaka Miki dashi".
Wasu zafafan hawaye ne suka zubowa Haura'ul insiyya bata damu data gogesu ba.
"Ina sonsa,son da bansan ta Yaya na Fara shi ba,batun yanzu nake jinsa a Raina ba sai dai Ganin babu fuska yasa na hakura , sai kuma Mama ta fada min sunyi magana da Ammi zasu had'amu aure tun bayan da aka samu matsalar da tasa yabar gida aka rasa Ina ya shiga a cikin duniya, na gansu a India Shida wannan matar tasa, tun a lokacin naji Ina masifar kishinta, saboda Ina Ganin indai tana gabansa babu wata mace da ze daga Ido ya kalla Wallahi".
Ta fada tana share wasu sabbin hawayen da suka ciko Mata idanu.
"Haba ranki shi dade har kina tunanin akwai namijin da zece baya sonki? Ai sai dai Idan ba'a bashi ba, ki gafarceni abunda Zan fada, ni bana Miki fatan ki shiga gidan Aurenki a mace ta biyu, fatana ki shimfida rayuwar ki keda mijinki da 'ya'yanki ki juya abinki yanda kikeso, Ina shi yaron da kuke karatu dashi a can Rasha din Dan nan Nigeria Wanda iyayensa sukazo suka gana da takawa ba naji ance Shima jinin sarauta bane? Kinsan dai da wuya Mai martaba yayi magana biyu ki yiwa kanki Qiyamul laili ki Zubar da wannan batun Kinga dai yanda baiji kunyar kowa ba a gurin dinner game da matarsa, haka naji wasu na fada har suna cewa ai a can gurin wayonsa ya samota, to kinga ko kin shiga ba wata daraja zakiyi ba tunda ba shine yace Yana sonki ba, mazan yanzu sun ganki sunce suna so ma Yaya aka k'are ballentana kin Zama matar shige? Babu abunda Zaki tsinta a gidan sai zaman hakuri, ki cire ranki daga Kansa kiyi ta addu'a idan shi Alkhairi ne a cikin rayuwarki Allah ze kawo sanadin haduwarku ya Kuma saka soyayyarki a zuciyarsa kinji, ki share hawayen ki wane gata ne Allah baiyi Miki ba? Da har Zaki Bata hawayenki a banza idan so cuta ne ai hakuri magani ne".
Duk Jikin Insiyya Sai yayi sanyi tasan duk abinda salbiyyar ta fada Mata gaskiya ne gara tayi addu'ar idan da Alkhairi Ubangiji ya fita sanin ta inda connection din ze hadu.
Salbiyya ta Jima tana kwantarwa da Insiyya hankali, tare da kawo Mata misalai na yanayin rayuwa da zamantakewar aure da irin qalubalen da ake fuskanta a irin auren da take kokarin saka kanta a cikinsa, kafin su kwanta da yake ita ke hidimtawa Insiyyar a Nan.


Karfe hudu na asuba alarm din da mahmud ya saka ya fara Kara, a hankali ya Mika hannu ya dauko wayar ya kashe, bedside lamp ya kunna harkenta madaidaici ya haske su. Zahra na kwance a jikinsa tayi lif da ita tana sauke numfashi cikin salama, dabin su na jiya ya tuna da kyar ta yarda dashi akan babu abinda zeyi mata, Dan Saida ya riga ta barci ma sannna ta saki jiki tayi nata barcin.
Sai kusan biyu da rabi ya farka ya ganta ta shige jikinsa kamar yanda suke barcinsu normal,sleeping dress din ya Kama ya janye 'yar igiyar da ake daurewa ta sunce ya zare a Hankali suka Sami body contact ya saka blanket ya rufesu, Yana kunna wutar itama ta farka a mamakance take Masa wani kallo ganin ta ba yanda ta kwanta ba, da sauri ta rarumo blanket din tana kokarin rufe saman jikinta da yake bude muraran, wuf ya saka hannu ya rike Yana Mata kallon k'asa-k'asa. "wallahi kina tufewa labarin ze canza salo Bakisan "I will eager to show you...ba ki barni na samu relief mana."
Ya fada tana Kai hannunsa inda yasa ta wuntsila gefe ba shiri tana kankame jikinta, Dan ya shammace ta Bata taba zaton haka ba.
Dariya yayi ya mike Yana fadin "matsoraciya kawai duk saina cire wannan kunyar dai Naga alama bazata Bari a kularwa da Malam dansa yanda ya kamata ba, gara na rabaki da ita kowa ya huta,kema ki Fara aikin Lada". Binsa tayi da Ido tana mamakinsa Dan da gaske ta yarda maza kunyarsu ragaggiyace wallahi.
Toilet ya shige yabar Zahra tana rarraba idanu kamar na shege a rabon gado.
Harya fito Bata motsa daga inda take a kudundune ba.
Da alama wanka yayi, kusa da kanta yazo ya tsaya Yana mamakinta sosai. wani smile ya saki Yana ayyana shifa yana ganin gara ayita ta Kare kawai duk yanda yaso a samu sirrin yayi hating din abinda akeyi a duniyar Hausawa Wai dole a washe gari sai Baki sunzo gidan Amarya sunga kwakwaf, to amma shi hakurinsa da ya Kare duk yanda yaso ya Dan daga Mata kafa saboda jama'a abun nema yaje yaci tura. Dan jiyama Saida yasha magani, to gara yasan abunyi da wannan shagwababbar yarinyar, ya kamata tasan Allah Daya ne, duk da yasan itama tana bukatarsa a yanda yake gani a cikin idanunta, yasan kawai tana zulumin yanda abun ze kasance Wala Allah tana karanta irin novels din Nan tana Jin yanda take kayawa a irin wannan dareren shine dalilin da yake d'aga Mata hankali.
Jallabiya ya zura ya Zuba turarensa, sannan ya dawo ya Dan cire rufar daga fuskata. "Tashi kiyi sallah kada guri ya kure Zan wuce masallaci". Dan mirginawa tayi tana kokarin tashi Bata zata ba yayi Mata daukar jarirai ya nufi katafaren toilet din dakin da ita tana ta magiyar ya sauketa amma yayi Mata fumfurus Saida ya dangana da ita cikin bathtub wanda ya cika Mata da ruwa Mai maraifaicin zafi sannan ya dire ta, Ganin Yana kokarin cire jallabiyarsa yasa ta waro idanunta tana Masa duban rashin fashimta.
Gira Daya ya dage Mata Yana murmushin data kasa tantance Kona menene "Ba.. ba.. masallaci zaka tafi ba Naga kana kokarin shigowa".
Girgiza Mata Kai yayi "na fasa fita yanzu wankan Zan sake kinsan bana gajiya da Wasan ruwa".
Bata San lokacin da dariya ta kubce Mata ba Jin yana fadin Wasan ruwa kamar wani small kid.
Ita dai batayi aune ba taji mutum a jikinta, duk iya magiyarta bai rabu da ita ba saida ya gamsu yanda yake so sannan sukayi wankan tare karshe shine yayi musu limanci a gida.
Sun jima suna Addu'oinsu sannan suka koma suka Kwanta Dan Shima barcin yakeji ba kadan ba.Amma Saida ya yamutsata iya yanda yake so Dan kirjinta Banda zogi babu abinda yakeyi da ba inda bakinsa Bai Kai ziyara ba Saida ya tabbatar ya Fara goge Mata hadda sannna ya saurara Mata ya sakata a jikansa kamar wata 'yar baby.
Wurin goma da rabi karar Kiran wayarsa ya tashi zahra, Mika hannunta tayi ta dauko wayar sai taga MY FIRST LOVE na yawo akan screen din wayar, wata faduwar gaba ce ta ziyarceta har wayar ta yanke bata dawo hayyacinta ba, wani Kiran ne ya sake shigowa cikin barci yaji special ringtone din Yana kadawa da sauri ya tashi sai yaga wayar a hannunta tana masa wani kallon tuhuma wayar ya saka hannu ya karba tana daf da sake katsewa ba tare Daya tanka Mata ba.
Yana daga Kiran ya tashi ya nufi kofa ya fice daga dakin. Baki a sake zahra tabi bayansa da kallo tana ayyana "wata sabuwa inji 'yan caca,wacece haka wadda har baza'a daga kiranta a gabanta ba? Harta koma ta kwanta sai kums ta tashi kamar wadda aka tsikara ta nufi kofar ta fice itama daga ita sai rigar barcin Wadda ta fito Mata da ilahirin surar jikinta muraran irin silk din nan ce kijinta ya fito muraran a ciki yayi irin cikar nan, wani yawu ya hadiye babu shiri..

*_AUREN HUCE HAUSHI_*

*AISHAT ISAH MUSAH*
(Maman Fateemah)

09061432330
Or

08055362975

Page. 84

.......".Good Morning Ammina". Abinda kunnenta ya Fara cin karo dashi kenan Yana fad'a lokacin data fito da azama idonta ya rufe da kishi ganin sunan da yake yawo a Kan screen din nasa, sai Kuma tayi turus taji wani irin sanyin Rahama Yana saukar Mata a cikin zuciyarta, dan ita kanta Bata San tana da irin wannan kishin ba sai yanzu da taga wasu kalmomi dake nuna mace aka alaqanta dasu, da sauri ta juya zata koma tunda babu wata tazara Mai yawa a tsakanin su, ita dai ba zato taji ya saka hannunsa Kan cikinta ta baya harga Allah batayi zaton ya ganta ba kuma Bataji tafiyarsa ko dan Valentino silifas din dake kafarsa masu irin laushin Nan ne, mannata yayi a jikinsa ta baya Yana cigaba da wayarsa ji tayi yana fadin. "Gata nan lafiayrta kalau Bari na Bata ku gaisa da 'yar taki Naga alamar Nan gaba duk tawaye zakuyi min tunda Naga kin damu da ita da yawa kamar an ce Miki Zan gutsiri Naman jikinta".
Wayar ya saka Mata a kunne Yana Kara kanainaye ta Yana shafa ruwan cikinta a Hankali.
"Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu, Ammy barka da Asuba".
Zahra ta fad'a cikin nutsuwa duk da jikinta yana karbar sakon da ake aika masa.
"Wa'alaiki Salam warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu, barkamu kadai diyata ya bakunta Ina fatan babu damuwa dai ko?".
A kunyace zahra tace Mata "babu komai Ammy na gode".
"To Masha Allah haka ake so, Allah yayi Albarka".
A zuciyarta ta Amsa da "Ameen".
Wayar ya mayar kunnensa yaci gaba da magana da Ammin nasa inda taji tana fada masa ga masu kawo musu break nan.
Taso ta zare hannunsa daga kan ruwan cikin nata Amma yaki Bata wannan damar falon saman ya shigo dasu ya zauna kan two seater ya dorata a cinyarta yayi Mata irin rungumar Yara har ya Gama wayarsa da Ammi dinsa.

Kallonsa tayi tana dan marairaicewa "pls ka barni nayi wanka kaga Ammy tace Baki sun taho kar ace min kazama fa"
Bakinta ya saka yatsarsa ya Dan zageye lips din Yana fadin "waye zece Miki kazama ai ke ko Zaki shekara bakiyi wanka ba babu Wanda zega kazantarki kinsa kuwa baiwar da Allah yayi Miki?".
Dan far tayi Masa da fararen sexy eyes dinta tana Masa wani kallon da yake susuta shi tana kokari barin Jikin nasa, tashi yayi tsam da ita Bai koma bedroom din da suka kwana ba, wani taga ya nufa da ita, ita fa sai yanzu taga yanda tsarin sama ma yake tamkar wata fada.
Bedroom din da suka shiga tsaruwarsa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login