Showing 138001 words to 141000 words out of 280244 words

Chapter 47 - AUREN HUCE HAUSHI complete

07 Feb 2026

1043

blanket din ya sauka har saman cikinta ga rigar ita da Babu duk Daya, a hankali yake shigowa cikin dakin kamar Mai tsoron kada ya tasheta, Yana Kare Mata kallo yanda tayi wani mahaukacin kyau a cikin dinligh din dakin, har ze tasheta saiya tuna condition din da take ciki ya juya ta fi????? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ?  ce daga dakin, yaso ya gyara Mata gashin Amma yasan matukar ya tabata sai ya sake alwalasa, a waya ya Kira Faruq ya fito su wuce masallaci.

A cikin barci taji kamar an bude kofa dakin, fargigit ta tashi tana addu'ar tashi daga barci, kamshin turarensa da taji ya hade dakin shiya tabbatar Mata daya shigo cikin dakin. A gurguje ta nufi toilet jin har an Fara sallah a masallatai, fatan ta Allah yasa har ta Idar Bai dawo daga masallacin ba Dan ita fa wallahi tsoronsa takeji Bata shuryawa abinda yake muradi ba...

AUREN HUCE HAUSHI.


MAMAN FATEEMAH.


Page 50.



_______Tun idar da sallar Zahra ta shiga kakkabe gadon Tana dubawa ko Allah zesa tayi arba da tarkacen ta na cikin jaka amma ko alamarsu Babu dole ta hakura ta linke sallayar da hijabin Adana saboda tsaro.
Bata koma barci ba gyara dakin tayi duk da ba wani datti Dan da gani sabon guri ne da alama ma kamar a jiyan aka Fara amfani dashi Dan ko toilet din shima haka ne, Bata dauki dogon lokaci ba ta gama komai ta bazawa dakin kamshi Dan ga Room freshners Nan kamar anyi gorinsu, wanka ta shige, ta Jima tana gasa jikinta da ruwan dumi sannan tayi wanka ta fito haka nan taji tana son tayi kwalliya Sosai.
Zama tayi ta tsara light makeup tabi jikinta ta Sanya turaren gabobi Dana bayan kunne duk ta saka tunda gasu nan kamar ba da kudi ake sayensu ba, ita dai ta zubawa sarautar Allah Ido taga inda wasan ze Kare, clothset din ta nufa ta bude dayan bangaren, English wears ta saka riga da siket blue black masu ratsin fari a jikin coat din,rolling tayi da farin veil ta fito Shar da ita gefe gadon ta zauna tana karanta addu'ar Azkar din safe.
Su Mahmud Basu shigo gidan ba sai wurin bakwai tun bayan idar da sallar sukayi zaman karatun alqur'ani da Azkar din Suma a masallacin. Faruq yaso ya wuce gida amma Mahmud ya Hana shi yace yayi zamansa a Nan ze fiye Masa shi yau ze koma Nasarawa Daman akwai abinda yazo yi Nan din zuwa anjima Idan ya gama zasu wuce Kuma ma Basu gaisa da madam ba, part din Daya kwana ya wuce shi kumq Mahmud ya nufi sabon part din har ya Fara hawan steps din ya dawo Yana Kiran Faruq.
Shima gangarowa yayi Yana nufo Mahmud din Saida ya Karaso yace masa.
"Ina key din waccen car din akwai Kaya a baya za'a fito dasu".
"Oh! Sorry, wallahi na manta Yana ciki trouser din Dana sake jiya, harna na fito dashi na manta ban baka ba, daman ni ka barwa ita Naga tayi maka kadan motar five millions ai sai mu Kuma ma motar Mata ce"
"Nima ba tawa bace ta madam ce idan kana so ka tafi da ita kawai".
Baki ya rike alamar mamaki Yana 'yar dariya.
"Haba dai yaushe za'ayi haka da Wasa nake gani nayi dai tayi kankanta a gurinka harma ita din gaskiya".
"To Yaya kake son ayi kenan?kaga dai bani na Bata ita ba Babanta ya saya Mata Kuma saina ce batayi ba, Ina laifi da ake bani aro da ita fa nazo airport lokacin da zanyi tafiya,Kuma anan na aje ta harna dawo sannan na dauko Mata abarta, Kuma kawai saina ce Mata tayi kadan to ina wadda tafitan da Zan bata?".
Ya fada Yana kallonsa, shima kallon nasa yake yi, shi wani zance yake masa me Kama da zaurance me yake nufi da hakan Yana nufin a baibai ya ninketa kenan kome?.
"Pls jeka dauko min we will discuss later". Da sauri ya nufi ciki ya dauko key din suka nufi gurin da motar take.
Kayan ciki suka dauko, da gudu malam ya taho ya karbe kayan hannun Mahmud Yana fadin "Haba yallabai meye amfanin na a gidan da har zaka dauki kaya". Ya karba yayi gaba da sauri Faruq ba biye dashi suka nufi parlourn kowa da dauke da ledojin a hannau.
Har gurin dining table ya Kai kayan ya Dora kayan Faruq ma a Nan ya dora na hannunsa, Malam musa ne ya koma ya dauko sauran da suka rage a cikin motar.
Maimakon Mahmud ya shigo saiya Koma dayan part din bai jima ba ya fito rike da laptop da wayoyi tablet guda biyu.
A parlourn ya iske Faruq Yana tsaye kusa da wani freme Mai hoton wani tsibiri a tsakiyar teku gurin yayi matukar kyau sosai.
Jin shigowar Mahmud yasa ya baro gurin Yana fadin "gaskiya tsarin gurin Nan yayi kyau sosai banyi zaton ze kai haka ba kafin a gama".
Wani kallo Mahmud din yayi masa Yana aje abubuwan dake hannuwansa.
"Amma Faruq ka fiye gulma, Ina cewa Kaine ka zana ginin Nan da hannunka zakazo kana wani zance daban a Kai Kuma, ni zonan ka shigar min da wasu sakonni cikin laptop din nan jiya naso yin aikin ka hanani".
Ya fada Yana kokarin kunna wayoyin dake hannuwansa.
Saida ya nuna masa komai sannan ya nufi upstairs.

Tunda ya doso saman yaji wani kanshin Dadi Wanda ya kasa tantance Kona menene, direct dakin Daya kwana ya shige Yana son ya sake wanka yana son ya fita wasu sabgogin nasa wanda yaken son yayi da Kansa.
Ya shiga ciki ba dadewa Zahra ta fito ta nufi kasa tana ayyana bari ta duba Koda kayan amfanin kitchen Dana abinci tasan abinda ya kamata tayi kada ta Zama sakarya wadda ta rako Mata. Plat shoes ta saka fari tas dashi ta nufo down stairs din cikin takunta mai daukar hankali, Bata ankara da mutum a zaune ba Saida ta ahigo tsakiyar falon taja ta tsaya tana rarraba idanu tana son tantance ya fasalin ginin yake da inda ya Kamata ta dosa,.
Carab suka hada Ido dashi ya aje abinda yakeyi ya Zuba Mata idanu irin kallon Nan na wuce shari'a Yana tsarkake ubangijin da ya yi wannan halittar da take gabansa.
Dan zabura zahrar tayi ganin mutum ba zato ba tsammani.
Aje abinda yakeyi yayi ya taso har lokacin Yana kallonta Dan ja baya tayi ganin ya nufo ta.
"Ina Zaki Kuma nida na taso na gaishe da Aunty na".
Ya fada Yana murmushi, saida ya matso ta Dan gane shi, shine jiya ya rungume Mahmud a kofar store din da yayi sayayya.
Sai lokacin ta Dan nutsu amma da tana tunanin ta Ina zata fece ta Koma saman tasan ko banza tana da mafaka a can.
Dan murmushi tayi itama tana fadin "Yaya sunan bakon da babu sallama? Kawai na wayi gari da ganin mutun ai dole na rasana".
Dariya yayi Yana fadin "Good morning Aunty".
"Morning".
Ta amsa masa a dan darare din nan ba wani sakewa, tana kallonsa.
"I am Faruq Dange".
Ya fada Yana juyawa zuwa inda yake aikinsa.
A hankali ta bude bakinta tace Masa.
"Sunana Fatima Zahra Muhammad Sani, Ina maka.barka da zuwa".
Tana Gama fada ta wuce can inda ta hango Kaya akan dining table.
Sakato yayi Yana kallonta Bai taba tunanin tana Jin yaren ba, Kai kawai ya girgiza Yana dan murmushi Yana fadin "wato Ya Mahmud sai a barshi kawai sannin inda ya dosa sai Allah, shi yasa kenan duk yayi d'iban Karan mahaukaciya da matan daketa rashin hankali a Kansa yayi tafiyarsa ya kyale kowa da nata salon rashin hankalin".

Ledojin ta shiga dubawa taga Dame Dame Nene a ciki, Wanda su Fateeha da mommy ta Bata ta cire ta aje a gefe sai Kuma Wanda ya sawo jiya ta cire na kitchen, kofar data gani a tufe taje tadan tura ga mamakinta a bude ta ganta shiga tayi kitchen ne modern sosai babu abinda babu a cikinsa tsayawa tayi tana nazarinsa kafin ta juya ta koma dauko Kayan.
Saida ta aje komai a muhallinsa sannan ta bude freezer data gani ta kwance, nama ne dasu kifa da kayan miya a Nike cikin manyan bikitin roba, kaji biyu ta Ciro da Zuba a roba ta tarasu a famfo saboda kankarar ta saki.
Filawa ta diba ta kwaba da yeast da barking powder ta rufe ta koma ta gyara Naman ta Dora a wuta.
Wani ruwan ta Dora daban ta dauko Madara ta bude ta diba Mai yawa ta dama Zuba akan ruwa data Dora ta Dan zame murfin sannan ta ciro hollandia custard ta fasa ta dibi yanda take ganin zata ishesu ta dama ta aje a gefe. Plates da cups da duk abinda tasan za'a bukata ta dauko ta wanke ta aje a muhallin Daya dace.
Filawar data kwaba ta dauko taga ya tashi ta ringa murzawa round sai ta Gama ta shafa Mai a frying pan ta rage wuta ta shiga gasawa tanayi tana juyawa.
Biyu ta raba Naman ta dattaka rabi tayi source Rabin Kuma tayi pepper soup dashi ta dama custard din ta dafa coffee Kuma.
Tun daga sama Mahmud ke jiyo wani irin kanshi girki yayi tunanin ko da wani sabon restaurant a Nan kusa dasu, Saida ya fito yana saukowa yaji kamshin ya cika gidan.
Shigar kananun Kaya yayi yayi masifar kyau, yau shigar da yayi ta fito da ainihin ko waye shi Dan ba karya kana kallonsa kasan matashi ne Mai cike da Jin Dadi da wadatar arziki Dan agogon dake hannunsa kadai na millions of naira ne, shigar da ya Jima da daina yinta Nan gida Nigeria rabon da ya fito haka tun kafin ya shiga rubibi.
Hannu Faruq ya shiga tafawa Yana fadin "perfect match, wallahi kun Dace Ashe haka Auntyn tawa take? Haba shi yasa baka sauraren masu yi maka rawar Kai, ya Mahmud Ashe da abinda ka taka shiyasa kayi shuru ka kyale kowa, Mai irin wannan matar mezeci da tarkace irinsu Safna, wallahi na Dade Banga ma'auratan da suka tafi da imanina kamar kai da Aunty na ba, Dan Allah ka tsaya min na auri kanwarta pls=?O?".
Ikon Allah Mahmud ya tsaya yana kallo lokaci Daya faruq ya gigice masa wato yaga zahrar kenan tunda ya sauko yaji gidan ya hade da kamshin girki yasa itace a kitchen, ko ba komai yasan Allah yayi Mata baiwar iya abinci a Dan zaman da sukayi ya fashimci hakan.
Shi rasa abin cewa ma yayi a Kan kalaman Faruq, Dan uwansa ne na jini, amma ya gigice da ganin matarsa, tab lallai da matsala Babba.
Bai nuna Masa komai ba sai Dan murmushi da yayi Yana fadin. "Ai mata ta ita kadai ce Bata da Kani ko kanwa, nine wanta nine komai nata Sai dai ka duba ko a Ina ne Zan shige maka gaba in Sha Allah".
"Dan Allah nidai ka taimaka ko cikin family dinta ne ayi min wanna alfarmar ka shige min gaba".
Kyale shi yayi ya nufi kitchen din lokacin ta Gama hada komai ta juyawa kofar baya tana cire jan bayan kwakwa zatayi amfani da ita in anjima.
Kamshinsa ya Fara fada Mata ya shigo gurin a hankali ta juyo, Yana tsaye ya harde hannuwansa a kirjinsa ya zubawa bayanta Ido,yanda ta juyo din nan shi Kansa da take halalinasa Saida yaji wani yarrr a jikinsa Dan gani yayi gaba Daya ta canza Masa ga wani irin cikowa da kirjinta yayi sosai.
Lumshe Ido yayi Yana tunanin lallai dole addinin musuluci da yayi Hani ga mutum baligi ya shiga gurin macen daba muharramarsa gaskiya. Yana can Yana tunani ya tsinkayi muryarta tana fadin "Ina kwana" batare data Kara kallon inda yake ba.
Bai amsa ba ya danyi gyaran murya.
"Meye Kuma Ina kwana? Na fada Miki ki iya tarairaya ta wallahi, kada garin kallon ruwa kwado yayi Miki Qafa, kina da kishiya fa kinsan idan ta fiki iya lafazi da tarairayata can Zan tare a gurinta".
Warrr tayi masa da sexy eyes dinta tana Masa wani kallo.
"Yes ko Baki yarda ba? yanzu na Kira Miki ita ku gaisa".
Kai ta girgiza Masa alamar A'a.
"Come on, zo Nan ki fada min bakya son kishiyar?"
Ya bude Mata hannuwansa alamar ta shigo, kafada ta make ta aje kwakwar ta nufi famfon cikin sink ta Fara wanke hannunta.
Cikin takunsa na nazantaka ya shigo ciki directly gurinta ya nufa Yana fadin "Ni gani na shigo sai nazo ki bani hot one tunda ni ba'a son nawa".
Bai jira tace komai ba ya saka hannunsa ya rungumeta ta baya Yana shafa cikinta.
Shiru tayi Masa kamar ruwa ya cinyeta, Jin hannun nasa ya nufi wata jihar yasa tayi saurin rike Masa hannu tasan idan ya karasa akwai damuwa sosai.
"Pls Dan Allah ka Bari kaga da bako a gidan kada ya jiyo mu fa".
Ta fada tana kokarin kwace kanta.
"Ok saboda shi Zaki hanani na sake kenan? To Bari na sender shi inda yafi wayo".
Dayan hannun ya saka ya ciro wayarsa yayi dialing din number Faruq, Sam batayi zaton kiransa zeyi ba, Saida taji Yana fadar "Faruq kaje wancen part din ka qarasa aikin gani Nan zuwa".
Bai jira yaji abinda yake kokarin fada ba ya kashe wayar ya Dora a gefen cabinet din kitchen yana fadin "to saiki sake ki bani hakkina tunda sirikinki yabar gurin".
Juyota yayi ya hade bakinsu ya cire rolling din, yana shafar gashin da yaji gyara ga qamshin hair spray sai tashi yakeyi ya jima Yana yamutsata kafin ya janye Dan Kansa yana Maida numfashi.
Tsugunnawa yayi ya dauko Mata veil din ya rufa Mata a Kanta Yana fadin "dauko wasu flask din ki zubawa Faruq nasa ki saka a basket na Kai Masa can idan ya gama ya tattara ya tafi gurin bikin da yazo".
"Me yasa? ba yace min shi qaninka bane".
"Ok. Dan Yana qanena saina zauna dashi gida Daya Yana kalle min Mata ko? Ai ya tafi shine mafita Dan akanki zamu iya batawa da kowa to maganin Kar ayi kada a fara, Dan Allah ki ringa saka hijab idan munyi Bak'i ba kowa ne ze iya kawar da Kai a kanki ba Kinga kuwa yanda Faruq ya gigice min na Nemo masa sister dinki, na fada masa babu Amma ya kasa fahimta sai rokona yake na samo Masa mace ko cikin family dinku ne"
Ya fada a Dan zafafe.
Shiru tayi ta nufi abinda ya sakatayi Saida ta Zuba Masa komai ta saka basket din ta aje a gefe ta dauko Wanda ta zubawa Mai gadi ta aje a kusa Dana Faruq din.
Malam Musa ya Kira yace yazo kofar parlourn su hadu, dauka yayi ya fice daga kitchen din yabar zahra da dogon tunanin akan abinda yace Faruq din yayi.


___

Tunda garin Allah ya waye Ammah ke faman neman number zahra abin yaci tura, a yau dai hakurinta ya Gaza Dan tun Daren jiya da zilai ta Kira Ammah tana fada Mata yanda fasalin gidan da suke yake da kuma kudin da tace an Basu dubu ashirin da safe da yamma ma an kawo musu wasu kudin dubu dari-dari ita da iya Rahane ga turamen atamfofi guda hudu hudu da lace bibiyu, Kuma ta fada Mata tunda su zahrar suka fice Bata Kara ganin giccinsu ba ga wayar ta ma a rufe.
Akalar Kiran Ammah ta canza ta shiga lalubo Number Abdul Hakeem.
Ringing din farko ya dauka yana Fadi "barka da Asuba Ammah, an tashi lfy?.
"Alhamdulillahi, idan ka tashi ka shigo Ina son ganinka" ta fada cikin damuwa.
"To in Sha Allah, gani nan shigowa"..
Ta kashe wayar, ta ajiye a gefe tana fadin "kazo ka nemomin wannan yaron ya fada min waye shi Ina Kuma ya Kai min 'yata ko waya ya Hana muyi da ita inji meye dalilni Daya hana ta amfani da wayar, tunda Naga Abban ba wani Abu zeyi ba, ga wannan kinibabbiyar matar tasa da koma sai taji Masa kwakwaf".
Tsaki tayi tana Jin duk Zuciyar ta ba dadi ko kadan, tana Nan zaune Abdul Hakeem din ya shigo sanye da jallabiya coffee colour a jikinsa ya gaishe da Ammah ya nemi guri ya zauna Yana fadin "lafiya kuwa Ammah?".
"Da sauki, Nemo min mijin Zahra a wayarka naji dalilinsa na yanke ma'amalarta Dani tunda suka bar garin Nan ban Kara Jin duriyarta ba".
Shiru Abdul Hakeem din yayi kafin yace "ba haka za'ayi ba, Zan kirasa na saka handsfree sai kiji yanda zamuyi dashi idan munji da alamun rashin gaskiya sai a San abunda ya Kamata tunda ba'asan dalilinsa. Ba na hanata amfani da wayar, ke uwace kiyi hakuri babu abinda ze Samar Miki 'ya da izinin Allah, in Sha Allah sai kinyi alfahari da Auren Nan Muhmud mutumin kirki ne bashi da wata alama ta rashin gaskiya, kinsan ya fada min shi Dan Sokoto ne,.har unguwar su da iyayensa duk ya fada min lokacin da zeyi tafiyar nan, yace saboda halin Rai Koda be dawo ba na nemi Sameer ko sabon mai gadin Daya kawo a can gidansu na hayin banki, ko Binya na gidan Baba malam duk mutanensa ne. Bari na kirasa Dan hankalinki ya kwanta".
Ya Fara dialing din number sa.
Sun Gama break fast din kenan wayarsa ta dauki slow music daga kitchen inda ya barota tsam ya tashi ya nufi kitchen din kafin yaje Kiran ya yanke, sunan Abdul Hakeem ya gani, kafin ya Kira wani Kiran ya shigo.
Saida ya zauna daf da ita ya daga kiran.
"Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu babban yayan mu, barka da Asuba".
Ya fada Yana murmushi.
"Wa'alaika Salam warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu barkamu kadai, ya iyalin?" Dariya abin ya bashi "Gasu Nan muna ta basu hakuri kasan Mata sai a hankali".
Ya fada Yana Dan Jan tsunin hancinta, Batasan dawa yake wayar ba.
"Wai meya samu wayarta ne Bata shiga kwata-kwata duk hankakii Ammah fa ya tashi, Jin kwana biyu shiru ba suyi magana ba idan tana kusa ka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login