Showing 261001 words to 264000 words out of 280244 words

Chapter 88 - AUREN HUCE HAUSHI complete

07 Feb 2026

1073

aji ya Zama soko marar katabus.
Tunda na tashi da misalin hudu da rabi na asuba yanda na Saba Sam najini a wani yanayi Sam banajin Dadin jikina ga faduwar gaba wadda da ita na tashi har nayi nafilolina na wuce masallaci gani Nan dai, sai da nayi karatun Qur'an sannan na samu relief na faduwar gaban, a ranar ko breakfast kasa fita nayi sai Sajjad autan momin Kano ya kawo min tunda Ammi Bata barin yaranta Mata shigowa part din mu ko Mai aiki Bata Bari su shigo gyaran part din ma maza ne keyi Kuma ko su zayyan basa shigowa gidan suna waje Bata hana suyi min aiki ba Amma Banda shigowa gida.
Haka na zauna Ina ta juye-juye a gado na rasa me yake min Dadi ga Sameer lokacin ana ta shirye-shiyen bikinsa a yanda mukayi ma a ranar Zan shiga Kano Dan na tura su naseer a sakawa gidan Dana Gina Masa furnitures tunda komai yazo, ban fito ba sai lokacin sallar Azzahar daga masallacin bangaren Ammi na wuce Ina Nan har la'asar tayi tambayar duniya akan meya sameni amsar Daya ce nake Bata ba komai, haka ta hakura ta kyaleni Amma itama sai Naga ta rage walwala.
Daga sallar la'asar ban dawo gidan ba Saina wuce mabera gidan Hajiya Inna a can na zauna nayi ta aikina har kusan Tara da rabi, nida zayyan ne kawai muka taho shiya tuk'o motar Sai goma muka shigo gidan saboda mun tsaya an sawo fruits saboda Dana shiga kitchen Naga sauran kadan Dan Apple da pear ma babu, ban shiga part din Ammi ba Amma na Kira su Batool nace suzo su shiga da kaya ciki.
Zayyan ya wuce Nima na shige ciki Dan har lokacin ji nake kamar Wanda aka yiwa duka, na gaji matuk'a.
Ina shigowa naji atmosphere din dakin ya canza daga daddad'an kamshin turarikan daki sai wani irin kauri marar dadin shaqa a dakin, ban zauna ba gudun A/C din parlour din na Kara na kunnu electric din da ake zuba masa turaren daki, tun a parlour na cire Kayan jikina wannan kuma normal d'abi'a tace ban fiye shiga bedroom da Kayan jikina ba idan na fita dasu Saida na cire na saka a washing machine ya Zama daga ni sai boxer short na wuce bedroom dina da niyyar nayi wanka na hada coffee na Sha tunda Ina da coffee maker a daki.
Ina shiga ba zato ba tsammani naji an rukungumeni gaba daya, sautin muryar Safna naji na fadin Dan Allah kayi hakuri,wallahi ka sakani a cikin mawuyacin Hali ka tausaya min idan ka fita a rayuwata mutuwa zanyi wallahi, Kai kadai nakeso nake muradi a rayuwata, kaji tausayi na, wallahi duk abinda kakeso Zan baka ko kaina Zan baka kaji dadi Dan nasan kana dasu da yawa Nima kazo wallahi kayi abinda kakeso Dani.
Rudewa nayi gaba Daya na rasa in da Zan saka kaina, wani abune da bantab'a zaton faruwarsa ba ya sameni bagatatan, kokarin raba jikina da nata nake kokarin Yi Amma kamar Wanda akayiwa dabaibayi a hannunsa sai Kara shigewa jikina take ga ta hade kirjinmu sai goga min jikinta take cikin kukan dana kasa tantance wane iri ne, da kyar na iya kokartawa ba juyar da ita ta tafi zata fada Kan gadona banyi aune ba naji ta fizgoni gaba daya na fada saman kanta kafin nayi wani yunguri Dan tunda na s???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?higo na shaki warin Nan na kara rasa kuzarina, naji an kwalla ihun kuka a saman kaina, abinda yayi saving din kenan daga rikon da Safna tayi min, da sauri na mirgina na tashi, sai lokacin na Farga da suturar dake jikinta, wata rigar barci ce marar Albarka duk breast dinta a waje. Ga hawaye bibiyu na bin fuskarta gashin kanta Mai Kama da hatsin bara ta barbaza shi.
Aunty Sameera na gani ta Dora hannu a ka sai kuruwa take yi, da gudu Safna ta tashi tana wani gunjin kuka tana fadin , wayyo Allah Aunty ki taimaka mini wallahi ba laifina bane barazana yake mini Koda yaushe ya lalata min rayuwata batun yau ba Aunty na shiga uku waye ze aureni a haka.
Cikin kuka itama aunty ta Fara fadin wallahi Mahmud kaci Amanarmu Dan kana da dukiyar da bazamu iya ja da Kai ko mahaifinka ba shine zaka ringa ketawa yarinya haddi, haba Ashe shi yasa taketa rama a tsaye,wallahi banyi zatonka a haka ba, aiko kana bin Mata Ina ga ka d'agawa yarinyar Nan kafa marainiyar Allah, Kuma inda mutumci ai zaman kanwarka take Dan haka wallahi dole ka aureta tunda Kai ka Fara saninta 'ya mace bazan yarda ba da wannan cin mutuncin da tozarci.
Tunda na samu kaina jikina keta faman tsuma ga wani uban jibi Daya rufeni duk kuwa da sanyin A/Cn da yake ratsa dakin, ni dai banga shigowa ko motsin uncle saminu ba sai ganinsa nayi a gabana jikinsa na tsuma baiyi wata -wata ba ya shareni da mari Yana fadin munafuki maci Amana,to yanzu ina masu cewa karya ake maka? Sai suzo suga ta'asar da kake aikatawa da idanunsu tunda suna ganin qazafi akeyi maka, Daman nasan idan zabuwa na yawo kere na yawo wata Rana zasu hadu, nasan za'a rina munafiki wallahi kaji kunya, Zina a cikin gidan ubanka wannan masifa har Ina Allah ya Kara Basu ne da Aure -Aure ba,kadan ma suka Fara gani.
Hannun Safna Aunty Sameera ta Kama tana sharbar kuka suka fice daga dakin, saida suka wuce uncle saminu yayi wata dariya Yana fadin. Yaro baisan huta ba in Bai taka ba, ba dai kace bazaka auri Asma'u ba kadan ma kenan sokoto Nan sai tafi karfin zamanka mu zuba kasa Ido wallahi saika Zama mujiya cikin tsintsaye duk kuwa da arzikin da kake yiwa mutane d'agawa dashi dariyar ya qarayi ya Sara ya fice daga dakin. Aunty Sameera na fita part din Ammi ta nufa ta shiga Danna bell ba k'ak'k'autawa Batool ce ta bude tunda itace ke kasa tana zuba Kayan dana kowa a fridge.
Da sauri ta bude Jin kukan dake tashi daga wajen, dai dai da shigowar Ammi cikin parlourn tunda itama taji Karan door bell din da akeyi ba sassuci.
Da sauri Ammi ta karasa shigowa tana tambayar Aunty Sameera me yake fatuwa? Cikin kuka riris Aunty Sameera ta bude bakinta da kyar ta Fara fadin . Ammin Batool Mahmud ya lalatawa Safna rayuwa wallahi a gado na samesu shida ita tana ta rusa kuka da magiyar ya barta Amma abun yaci turn Ashe Daman haka yake Mata ta kasa fada sai Rama take a tsaye na shiga uku Yaya zanyi da wannan abun kunyar? Kasa ko motsi Ammi tayi haka batool ita abun Daya fi daure Mata Kai duka yaushe hakan ta faru kamar a cikin Shirin film to da yaushe ya shigo gidan da har wannan dogon labarin ze wakana har haka, Amma saboda tarbiyyar da akayi Mata yasa Bata tofa ba ta zubawa sarautar Allah Ido Amma ta yiwa abun question mark.
Innailaihi wa innailaihi raji'un, abinda Ammi ta dinga maimaitawa kenan ta kasa furta ko kalma Daya tamkar an saka padlock an rufa bakin da zatayi wani sharshi.
Uncle Saminu ne suka shigo shi da Abbie sai Momin Kano wadda ranar girkinta ne Dan a can part dinsa na bangarenta ya iske shi shine ta biyo su ganin hankalinsu a tashe.
Da ganin yanda Abbie ya shigo hankalinsa ba a karamin tashe yake ba Fadi yake Ina safnar take maza a Kira doctor innailaihi wa innailaihi ilaihi raji'un , wannan wace irin musibace ta shigo gidana?.Dan cikina ya aikata irin wannan rashin Albarka a cikin gidana, Ina Mahmud din take? Ita Ammi rasa abin cewa tayi ji tayi kamar an Dora Mata bulo inci Tara a kanta ga kirjinta yayi Mata nauyi, sahal ne ya nufi kofar fita da sauri saboda gaba daya suka fito Jin kuka a part dinsu Suma abin ya Basu mamaki Dan a gaban Sajjad na wuce Yana waya, Amma a cikin abinda Bai wuce mintina goma ba wannan kurar ta tashi, tun daga parlour har bedroom suna bude Amma bana ciki dole Sajjad ya koma ya fadawa Abbie bana nan, abunda ya Kara tada kura kenan uncle saminu ne yayi tsagal ya Fara fadin to Daman ta Ina ze tsaya yanda yayi wannan abun kunyar Zina har cikin gida duk wadda ake a waje Bata wadatar ba sai an yiwa yaran cikin gida fyade.
Nan da Nan Abbie ya Kara tunzira ya shiga fada sunce yayi fadan da Basu tab'a gani yayi ba Fadi yake wallahi babu shi babu ni ya cireni daga cikin y
'ya'yansa tunda na fita zakka naje ya sallamani gani ga duniyar Nan idan giyar kudi ke rudata Ina Dan k'aruna yake.
Jin furucin Abbie yasa uncle saminu tarar numfashinsa Yana fadin idan ya tafi ai yaci bulus a Nemo shi yazo ya aureta dole, idan aka barta a haka ai an zalunceta gaskiya saboda an fita gata, ai tun faruwar wancan abun nace maka ga Asma'u Nan na bashi Amma lokacin saika nuna ba haka ba in da anyi Masa Auren Aida hakan Bata faru ba, da ba'ayi maka halin Dan akuya a gida ba, idan kayi sake sai an Fara shigo da shegu ma cikin gidan Nan.
A cikin hasala momin Kano tacewa uncle saminu haba wace irin magana kake fada haka Bai Dace ba Dan zumunka meze Hana abi abun a hankali ita safnar yarinya ce karama da za'ayi ta babatu tayiwa mutane bayanin abinda ya faru Mana. Dan me za'ayi ta dorawa mutum Daya laifi ita meya kaita part dinsu a irin wannan lokacin ayeh?.
Cikin tashin hankali uncle saminun ya taso Mata kamar ze daketa Yana fadin.
To kice da hadin bakinki yake ketawa yaran mutane haddi kenan, Dan munafurci bazaki Bari ayi Masa hukunci ba tunda Yana kawo Miki abin duniya idan ya lalace Baki da asara Dan kishiya ne ko?.
Momi Bata barin ta kwana ta zaburo zata gaggaya Masa magana Abbie yayi Mata Karan tsaye, kofar fita ya nuna Mata alamar ta fice, zata bude baki tayi magana Ammi ta girgiza alamar tayi shiru kawai.
Ammin ma juyawa tayi zata bar gurin cikin kaushin murya wadda tunda suke Bai tabayi Mata magana da makamanciyarta ba.
Ki fad'awa danki duk inda ya shiga ya fito yazo Ina nemansa idan Kuma ba haka ba wallahi da kaina Zan Mika case din Nan human right kinji na rantse.
Yanda Bata tofa ba lokacin da suke babatun yanzun ma wucewa kawai tayi tana jiyo yanda Abbie din ke kwantarwa da Aunty Sameera murya Yana Bata hakuri ita Kuma tana daga murya, Batool ma barin gurin tayi.
Hummm previous Ashe kuka Rahama ne bansan haka ba sai a ranar, Dan naso ace Zan iya yinsa konaji sassuci Amma Ina Idanuna sun soye babu alamar hawaye sai zafin zuciya kawai nakeyi.
Tunda suka fice daga dakin Nima na zura jallabiya na dauki key nayi waje tunda na fita na rasa Ina Zan nufa nayi ta yawo a cikin gari har sha biyu da kusan minti arba'in da biyar, Dana gaji da yawo na shiga wata primary na yiwa Mai gadin gurin bayani Ina son na yada zango ni matafiyi ne, wallahi haka na kwana ko gyangyadi Bai kamani ba, ban taba tunanin haka akeji idan an yiwa mutum k'azafi ba sai da yazo kaina, ban taba tunanin Alkhairi Yana Zama mugunta ba sai a kaina da Safna ban taba hasasota a haka ba ko cikin mafarki, shi yasa hausawa ke fadin idan kaga mutum a Rana barshi a ranarsa da hikimar da tasa aka aje shi a ranar.
Bayan nayi sallar Asuba gida na nufo ban shiga gurin Ammi ba part din mu na nufa Ina zuwa dakin naji wani irin tashin hankali kamar lokacin abin yake faruwa, a parlour na zauna Ina sakawa da kwancewa na rasa tudun dafawa, wurin bakwai da rabi naji ana tab'a kofa ban motsa ba ban Kuma bada izinin shigowa ba, Faruq ne shida saif kanin Ya Abbas ne suka shigo Ina Zaune Ina dafe da goshina kaina na matukar Sara min, daga kallon farko da nayi musu ban sake daga idona na kallesu ba.
Cikin nuna damuwa Faruq ya tambayeni Wai meya faru ne jiya shi Yana barci baisan wainar da aka Toya ba, Saida Asuba sahal ke fada Masa abinda ya faru, ta tafasa ban iya tofawa ba Dan bakin cikin dake ci min zuciya haka ya hakura ya tashi amsa Daya na bashi nace masa babu mutumin da ze iya yi Mana shari'a da duk Mai hannu a cikin Lamarin sai Allah.
Wurin goma Kiran Abbie ya riskeni banyi kasa a gwiwa ba na nufi part dinsa, Ina zuwa na samu Abbie ne da 'yan uwansa sai Safna da Aunty Sameera.
Ina shigowa Safna ta fara share hawaye, Abbie na fara gaishewa Wanda Ni dai da kunnena banji ya amsa ba, sai su Uncle Mustapha nayi musu gaisuwar Jimla.
Kamar jira ake Ina Zama aka Fara surfa min fada babu ji babu gani, Auncle Mustapha ne kawai ke supporting dina Yana fadin kowa ya lafa a tambayi ba'asin meya faru ne Amma babu Wanda ya saurare shi, duk yanda yaso ayi adalci a cikin Lamarin abin ya gagara, Dan har gaban Abbie mukaje zanyi Masa bayani Amma ya tashi ya bar gurin abinda ke daure min Kai yanda uncle saminu ya Zama shike bada Umarnin abinda za'ayi Dan yace aure nida Safna babu fashi haka aka tashi baran baran da uncle Mustapha inda ringa fada Yana fadin an fada musu mutane jahilai ne a tsaya ayi abinda ya kamata Mana sai a dauki son Rai a Dora ga gaskiya Amma ana neman taketa da gangan Dan wata manufa ta daban, a gaba uncle Mustapha ya sakani mukaji wurin Ammi Abu mafi bani tsoro Kinsan kallona Ammi batayi ba duk yanda uncle yayi Mata bayanin irin nasa hasashena wallahi Sam ta nuna Bata bukatar jin komai daga bakina haka muka fito Ina rangaji ga Abu goma da ashirin ya tare min inda nake tunanina Zan samu tallafi da tausaywa sai Kuma na Sami aka sin haka, Bari nayi Miki taku ta Mata a lokacin fa kakana Alhaji sa'id ya rasu, nasan da Yana Nan abun baze Kai haka ba.
Kiran sallar da aka kwalla shi ya tsayar da Mahmud da dogon labarin da yake bawa zahra, kallon fuskarta yayi sai ganin hawaye yayi suna bin kuncinta Bai hanata ba ya dai gyara Mata kwanciya a cikin jikinsa duk da lokacin sallah yayi.

AUREN HUCE HAUSHI.

Maman Fateemah.

09061432339

Or

08055362975



Page 94.



_______ "Pls previous ki daina kukan Mana, abun Nan fa wani past event ne ya Riga ya wuce kawai dai Ina fada Miki irin Qalubalen Dana fuskanta ne a rayuwa da Kuma irin yanda na koyi iya mu'amala da jama'a Kinsan masu iya magana na cewa na daka baiyi kallon waje ba, to Nima hakan ce ta kasance dani da ba'a Sami wannan matsalar ba da wata kila harna koma ga Allah bazan San wasu abubuwan ba na yanda wasu suke rayuwa, previous na koyi darasin rayuwa yanda bakina baze iya misalta Miki ba, tashi muyi haramar sallah idan Allah ya kaimu wani Daren saina karasa Miki sauran labarin dan nasan daga safe har zuwa dare babu lokacin Zama kinsan Hausawa sai a slow su da gidan Amarya".
Ya fada Yana dariya itama duk da zuciyarta babu Dadi Saida taurmusa.
Tare sukayi wanka ya wuce sallah itama ta Fara nafila kafin a tayar.
Har gari yayi haske Bai shigo ba itama azkar tayi da karatun Qur'an, tana kokarin cire abayar da tayi sallah ya shigo, a hankali ya tako har inda take tsaye Yana zuwa ya Ida cire Mata Yana Fadin. "Meya hanaki barci? dubi idanunki barci ne fal a cikinsu da gani".
Dan narke fuska tayi tana Masa wani kallo, dan smile yayi Wanda yake karawa kyakykyawar fuskarsa kyau.
"Yaya ko da labari? Nasan jirana akeyi ko kuma gaisawa zamuyi ne?".
Kafada ta make irin yanda Yara masu kiwa sukeyi idan suna hannun iyayensu.
"Nifa Karatu nayi fa shi yasa ban kwanta ba gara na rabauta da Alkhairin dake cikin safiyar".
"Gaskiya ne sayyada". Ya fada Yana dariya, itama murmushi tayi, sunyi barci har kusan Sha biyu sannan suka tashi wanka suka shiga tare sun Jima sannan suka fito suka shirya ita cikin rigar material data Sha beads work shi Kuma cikin shada geezner boda style sai baza kanshinsu suke yi. Lokacin da suka sauko su Aunty zilai suna kitchen ita da binta suna girkin rana, fitowa sukayi suka gaisa sannan suka koma bakin aikinsu, bayan sun Gama break din ne suka dawo second parlour inda Mahmud ya dauki remote control ya canza Tasha daga Tauraruwa zuwa sport news inda ake highlight na kwallayen da akayi. Kasa hakuri Zahra tayi ta jefa Masa tambayar da take ci Mata tuwo a kwarya.
"Meu Amor Wai Dan Allah me kikeji idan kana kallon Ball din Nan?".

Dan kwantar da kansa yayi a gefen kafadarta Yana shaqar kamshinta Wanda yake sakar Masa da kasala.
"Yanda kukeji idan Kuma kallon series ko Kuna karanta novels Dan nasan daidaikun mata ne basa wannan sana'ar, Dan Batool har kwace wayarta na Sha yi lokacin tana secondary, to muma haka muke Jin Ball a cikin ran mu".
Jin jina Kai Zahra tayi tana farin "Na gane yanzu kam, ai karatun novel duniya ne Dan Idan book ya dauko Dadi wallahi bana kaunar abinda ze tasheni daga karatun".
Wata sinsina ya yiwa wuyanta tare da hura Mata iska ba kunne, hade jikinta tayi tana nuna Masa bangaren kitchen da Hannu.
Ido Daya ya kashe Mata. To Nima hakan nake Jin kwatankwacinsa akan Ball din".
Sun jima a gurin suna Hira har aka Gama labaran Ball din. Baki ne suka Fara zuwa danginsu na Dangen shuni Mama Bilkisu ce tazo Bata k'asar akayi bikin nasa, da gani sunyi saboda dashi sosai har yaranta, mace 'yar gayu ta ajin karshe ga sakin fuska Dan kamar ta goya Zahra sai fadin Masha Allah takeyi Nan da Nan aka cika gabansu da Kayan tarbar Baki Dan Aunty zilai expert ce a wanna fannin.
A cikin hirar da sukeyi ne Zahra ta gane suna k'asar Canada Latin America ita da yaranta inda mijinta yake ambassadorn Nigeria, Mahmud Bai samu fita ba sai lokacin sallar Azzuhar sannan ya samu ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login