Showing 123001 words to 126000 words out of 280244 words

Chapter 42 - AUREN HUCE HAUSHI complete

07 Feb 2026

1074

wanka cikin ruwan data hada ya shigo ciki ba zato ba tsammani sai ganin mutum tayi ya shigo daga shi sai boxer a jikinsa, gurin da take tsaye ya nufo, da sauri ta matsa gefe kanta a kasa Bata yarda sun sake hada Ido ba tace Masa.
"An Gama hadawa".
Tana aje robar dake hannunta ta juya da zummar barin gurin. Taku biyu tayi taji anyi sama da ita cak sai cikin ruwan daga ita har kayan jikinta, wata ajiyar zuciya ta sauke tana fadin "Dan Allah ka Bari wallahi nayi wanka fa".
"I know, tayani zakiyi Dan rashin kirki ai ni bakonki ne ya kamata ki tarairayeni har wankan ma kiyi min tunda kin hanani sukuni Saida Kika gargadoni na dawo gurinki Kinga kuwa ai duk lokacinki yanzu nawa ne".
Har ta bude Baki zatayi magana ya Dora Dan yatsansa a Kan lips dinta "kin manta ba'a magana a cikinki toilet? Muyi wankan later munyi maganar".
Janyota yayi jikinsa ya Fara cire Mata jikakkun kayan jikinta, a tsorace da Kuma wata azababbiyar kunyarsa da takeji ta Kara ninkuwa, dan wani Abu ne da be taba faruwa da ita ba a tarihin rayuwarta irin wannan kebewar da namiji baligi da uwar tana irin wannan Bata taba yiba shi yasa Daya hade jikinsu ta shiga tsuma kamar wadda Zazzabi ya rufe, wankan sukayi tare duk da shi dai kadai yake sha'aninsa Dan ita dai kam sai hankali.
Saida ya Gama son ransa sannan ya karasa wankan ya fito ya barta a ciki,Saida ta kimtsa kanta sannan ta fito, lokacin har ya shirya cikin wasu kananan Kaya Yana daura agogo, tsaye tayi a kofar toilet din ita Bata koma ba ita Bata karaso inda yake ba, kallon kasa kasa take masa gani tayi gaba Daya ya canza Mata kamar anyi musanyarsa da wani ya Kara zaman wani handsome dashi jikinsa ya Kara Zama fresh dashi.
Inda take tsayen ya nufa "pls ki shirya Ina son fita ne wurin after zuhur".
Kofa ya nufa ita Kuma ta nufi gurin mirror tana goge jikinta, hand dryer data gani a gefen mirror ta dauka ta jona ta busar da kanta, cikin kankanin lokaci ta shirya gurin kayan ta nufa tsaye tayi tana kallonsu. To Wai ita Nan din Ina ne gidan waye taga ya shigo ya barrarraje Yana tsula sha'aninsa ga kayan Mata birjik Kuma ance mamallakinsa ko aure beyi ba to Ina ba"asin kayan nan na can part din Aunty Rukayya tace nata ne to wannan fa na waye su kuma? Qundunbala tayi ta dauko wasu English wears, ta saka masu kalar brown dark sai veil milk colour tayi rolling ta fesa turarenta dake cikin handbag dinta sai lokacin taga maganin da Hajiyar makwarari ta bata, Dan murmushi tayi a zuciyarta ta ayyana "zanzo na Baki hakuri Hajiya nasan ban kyauta Miki ba dole ce tasa na aikata hakan".
Dakin ta Fara gyarawa ta cire bedsheet din ta duba gurin da take tunanin zata iya ganinsu ta duba.
Very luckily ta gansu ta Ciro Daya ta baza zata Fara shimfidawa ke Nan ya shigo dakin Yana waya, da hannu ya nuna Mata ta taso, ba musu ta taso ya nufo inda yake hannunta ya kama ya nufi kofa wani Abu kawai ya taba daga can kasa kofar ta bude, da kallo ta bishi tana mamakinsa gaba Daya ya canza Mata Kuma yanda yake mu'amala da gidan Yana Bata mamaki, har suka fito parlour na biyu Yana ta wayarsa wadda ta fuskanci kamar suna maganar kasuwanci ne sabo da aka Riga aka fara, direct dining ya nufa da ita Saida ya zaunar da ita sannan ya zauna.
Wani Dan guri ya danna jikin table din, ba'a Jima ba saiga wani saurayi ya shigo ta wata kofa.
Baiyi magana ba tun bayan sallamar da yayi Zahra ta amsa masa, wayar ya kashe ya juyo Yana duban Wanda ya shigo din.
" Safwan Kada naji labarin Ina garin nan a bakin kowa, kaje inda na turaka jiya?"
"Naje oga komai ya Zama normal, harma sun Fara aiki saidai Zayyan yace wannan Matar tana yawan zuwa kusa da gidan amma dai Bata karasowa take komawa".
"Ok ba damuwa kaje kawai idan ka dawo ka taho da fresh milk da fruits a saka a kitchen din nan".
"Ok sir, na gode ya juya ya nufi inda ya fito har ya danyi nisa yaji maganar Mahmud.
"Safwan banji ka gaishe da madam ba, bahaushiya ce ba wani yaren zatayi makaba, Naga alama saina miqaka makarantar koyon turanci tunda Naga shi kadai ne kake da matsalarsa".
Dan Sosa Kai yayi yana dawowa baya.
"Afuwan Auntyn mu wallahi na dauka bakijin yaren mu, Ina kwana?"
"Lafiya kalau ya aiki?".
"Alhamdulillahi Auntyn mu, Allah ya Kara sutura ya bar Mana ke a gidan oga Dan isar Annabin Rahama".
"Amin ya Hayyu Ya Qayyum".
Muhmud ya fada.
Hanya ya nuna Masa alamar ya wuce bai Kara tofa wata maganar ba ya juya yabar gurin.
Ita Zahra kallon ikon Allah takeyi wallahi wannan ba Wanda suka zauna a Azare bane da banbanci nesa ba kusa ba.
Iskar Bakinsa ya hura Mata a fuska saitin idanunta, "kallon na menene Kona canza Miki ne? Kika tsareni da wadannan eyes din naki masu hanani sakat idan Ina kallonsu Dan Allah ki barni naci abinci kome kike bukata saina Baki badai kin hanani zaman can ba, to aini gaba ta Kaini gobarar Titi a jos, haka ake fada ko?" Ya tambaya Yana bude abincin.
Dan kwabe fuska tayi tana Dan turza kafa a kasa.
"Ni wallahi bani nace ka dawo ba kawai Kaine kayi niyya da kanka ka dawo Ni ba ruwana to na kiraki nayi maka me?".
"Au haka Zaki ce shike Nan yanzu dai bani abinci daga baya sai kiyi min bayanin yanda aka haihu a ragaya".
Bata gane hausar tasa ba tayi Shiru dai kawai.
Abinci ne kusan kala biyar Banda pepper soup na turkey.
Kasa hakuri zahra yayi Wai daga Ina wannan abincin irin haka?"

"Daga jama'ar Annabi, kinsan mu 'ya'yan malamai ko Ina muka sauka gida ne".
Shiru tayi ta zuba Masa abincin zata Zuba nata ya dauke plate din.
"Kin manta ai ba raba Abinci a tsakaninmu muci kawai".
Tare sukaci abincin suka Gama, tana Dan kallonsa lokaci-lokaci, da gaske yazo Mata da abubuwan mamaki da yawa Amma azarbabi ba nata bane. Dole tabi kamai a hankali saida ya tabbatar ta koshi sannan ya saurara mata, Nan cikin parlourn suka dawo suka zauna ya dorata a cinyarsa yasa hannunsa ya zagayo cikinta yana ta faman
amsa wayayoyi, sai ya amsa way kamar uku, sannan ya aje ya fuskance ta. Wasu irin wayoyine guda uku Wanda ita dai sai a T.V take ganinsu amma sai gasu a hannunsa kuma ya wani ci magani Dan kada ta Tama Fara masa wasu tambayoyi.
'
"Bani labari ya akayi ciwo Bai tashi kamaki ba Saida nayi Nissan Zango, naji doctor tace Wai rashin samun biyan bukata ne yake kawo miki yawan ciwon marar saboda sha'awarki tana motsawa Baki samun biyan bukata".
Waro Idanu tayi Baki bude tana Masa wani kallo.."Ni kuma? Wane irin magana ce wannan bayan fibroid din Kuma harda bita da kullin sharri? ta Nan Kuma ta bullo? To ai sai tazo ta ta cire min sha'awar tunda ita ta ganta, kawai ta Fadi gaskiya tanaso tayi amfani da aikinta ta cuceni,tunda da hadin bakinka Ashe ni aka mayar sakarya aka tasoni tunda daga kauyen mu aka kawoni gurin budurwaka ta dubani,ta ganeni ciki da bai kaga ko idan ta aureka bani da wata fuffuka da zanyi Mata, wata Kila da Allah baisa ta fito da maitarta fili ba da Allah kadai yasan illar da zatayi min.Da Jin saita cire min mahaifa gaba daya, ka fada Mata wallahi da gatana Ina da gatan da wallahi ta cutar da lafiyata Saida ta kare rayuwarta a life in prison, kuma indai Kaine nabar Mata taje ta hadiyeka kada wata ta Kara ganinka tace tana so, an fada Mata Ni Ina da damuwa ne da zata ringa wulakantani in dai saina Kara zuwa ta dubani ciwon yayi min abinda Zeyi min Kuma yau in Sha Allah gida Zan koma bazan iya Zama a Nan ba Ni duk kanon ma ta fice min daga Rai, ka mayar Dani inda nafi wayo".
Ta karasa fada tana juyar da fuskar ta gefe.
Kwanto da kansa yayi gefen wuyanta. "Cewa fa nayi ki bani labari ba cewa nayi meye damuwar ki ba, Ni meye laifina daga na turoki a duba min lafiyarki".
Ai fadar hakan saiya tunzurata nan da nan sai hawaye.
"Oh! My God!, Mena fada Kuma? pls tell me".
"Kwace Kanta ta shiga yi tana fadin.
Daman nasan ba Sona kakeyi ba tunda Ni matar shige ce Bata da daraja kuma wallahi duk Wanda ya Zama sanadin da wannan gararin rayuwar ya sameni ban yafe Masa ba, da qimata da mutuncina an mayar Dani wata shakatafi kowa saiya takani yanda yaso bani da wata qima".
Ta sunkuyar da kanta tana wani kuka Mai cin zuciya.
Iya dagula lissafi tayi Masa Dan kasa cewa komai yayi sai sakata da yayi a jikinsa ya kwantar da ita shi kadai yasan abinda yakeji, suna haka yaji wayar Daya Bari a kunne wadda yake amfanin yau da gobe ta dauki kida Mai Dadi.
A hankali ya Kai duba gurin wayar, Sameer ne.
Dauka yayi baice komai ba "Ina kofar part din Nan kana da bakuwa".
"Dude ka shigo sai muyi maganar".
Ya kashe ya aje wayar, Jin ya ambaci Sameer ya shigo yasa zahra yayi kokarin zare jikinta amma Dan bawan Allah nan kememe yaki sakinta saiya gyara Mata Zama kawai.
Dago Kai tayi da niyyar yi Masa magiyar ta saketa ta tashi dai dai lokacin Sameer ya karaso gurin, be taba tunanin tana jikinsa ba tunda shi kadai ake hangowa Saida ya kure musu yanda ba yanda za'ayi ya koma, tsaye yayi shi Bai Kona ba shi Kuma be karasa gurinsu ba ita kuma Zahra kunya kamar ta nutse wallahi Bata taba tunanin rashin ta idonsa ta Kai har haka ba.
"Have a seat, kazo ka tsaya Wai kuka take min na kawota an Mata wulakanci na Maida ta gida ita ko sunan Kano Bata sonji".
Sameer 'yar dariya yayi "Ni ba ruwana a ciki Dan aikene ni kasan Mata Dan Abu kadan saiya tada musu hankali, Daman bakuwar tata ce Hajiyar makwarari ce ta kirani bayan nabar Nan Ina gidan mommy na mayar da Rukayya saiga kiranta Wai lallai saina daukota tazo taga madam shine mommy tace na kawo ta indan ba haka ba zata iya rikita lissafin kasan halinta dai".
"Ok ba damuwa ku shigo tare ai Hajiyarmu ce ba inda bazata shiga ba".
"Ok sir".
Ya juya ya fice daga parlourn da sauri,mamakin Mahmud ne ya kamashi sosai ya rasa wane irin so yake yiwa yarinyar Nan ne haka? Yana tare da wannan mezeyci da wata Haseena ai saidai tayi hakuri da can Bata you tasiri ba gurinsa ba bare yanzu daya Sami abinda ya kwallafa rain a kansa.
Zahra Jin Sameer ya fice yasa ta dago da kanta daga kijinsa tana ajiyar zuciya, Dan just tayi kukan ta Kama nasa guri sai mamakin furucin oga Sameer daya cika Mata zuciya wai sir to me hakan ke nufi itafa kada su manna Mata Dan karamin hauka gaskiya.
Dan Allah ka barni na tashi kaji fa Hajiya ce yace fa
Zata shigo, Kuma Dan Allah bakaji kunya ba ka wani sakani a jikinta salon yace bani da tarbiyya".
Wani kallo ya watsa Mata "ai yau ko waye ze shigo gurin Nan a haka ze samemu gara asan Ina sonki tunda kina ganin ba sonki nake ba har kina kallona kina fadin Wai matar shige ce ke idan aka sameni rungume da kayana Ina lallashi kuwa koya saiya sheda ina son abuna, nine dai ba Sona ake ba anfi son wannan Mai jan kamar karas tunda saboda shi aka yarfeni da bakaken maganganu".
Har ta bude Baki zata bashi amasa taji rangada sallamar Hajiyar makwarari, ai ita kanta Bata San yanda akayi ba ta tsinci kanta a tsaye ballentana shi da ake zaune a jikinsa, shi dai Sameer Bai San lokacin da dariya ta kubce Masa ba ganin yanda Zahra tayi wani wuk'i-wuk'i da ita shima gogan dariyar yake Amma a ciki.

Da sauri ta nufi Hajiyar tana fadin. Oyoyo -oyoyo ga Hajiyata ga Hajiyata".
"Ke tafi can Ashe duk abinda na fada Miki ta bayan kunnenki ya wuce Saida Kika fice Kika barmu da tashin hankali, jiya kukan da nayi rabona da yin irinsa tun rasuwar mijina. Amma Kika sakani maimaitwa Dan Allah ke kuwa 'yar Nan Ina Kika tafi jiya".
"Haba Hajiya Dan Allah haka mukayi da ke a gida kafin mu taho wato kin karya Alkawarin kenan? To a kazarki ta juma'a wallahi"
Ita dai Zahra borin kunya ta Fara "Allah ya Baki hakuri nifa na fada Miki kawai dai yawan mutane ya Hana ki gane waye yake Miki magana, Amma yaushe zanyi Miki haka Allah naji maganar ki kinga yanzu ma Zan Sha maganin fa".
Mahmud ne ya taso Yana fadin "Hajiyar mu ki shigo ciki ki fada min abinda ba'a so na sani Zan Baki abinda yafi kazar ma".
"Yauwa nasan kafi da haka, kanaji jiya ne wata daukakkiya ta tadawa yarinyar Nan hankali Wai kome gareta a mahaifa bansan dai sunansa ba da yaren Nasara Amma dai da hausa muna ce Masa tsiron mahaifa Wai sai tayi Mata tiyata,haka kawai ta ragewa zukekiyar 'yar Nan kwaliti yo an yanka mutum tun baiyi haihuwar fari ba Ina labari, shine nace baza'a yanka ta ba ga magani Nan Tasha na wata Daya in Sha Allah ze narke, ai sai daga baya Rakiya ke fada min ita waccan din ta Dade tana sonka tun Kuna turai koba haka bane? Ja'ira taga yarinya danya Sharab zata zauce tayi Mata illah to Banda abunka yaushe zaka ce buduwarka ta duba matarka ai wauta ce babba, wallahi kada a Kara kwatantawa, shine fa yarinyar nan tayi Mana batan dabo tun azzahar muka nemi 'yar Nan muka rasa nayi kuka kamar Zan yada idona to me zamu fada maka daga kawo yarinya ace ta Bata a gidana wallahi in takaice maka labari sai goma Sha biyun dare aka ganota ta Janbulo gidansu kawarta, itama uwar da yake ta kirki ce sai tayi tunani ta Nemo uwarta a waya take tambayarta duk da tana gurinta ta haka akasan guduwa tayi daga gurina cikin dare suka daukota to kaji yanda magana dai take".
Wani kallo ya yiwa Zahra Mai ma'anoni da yawa, sannan ya juya Yana kallon Sameer Wanda tunda Hajiyar makwarari ta Fara zuba ya sadda kansa kasa yayi Dana sanin kawota tafi cikin cikin masaki.
"To shike Nan in Sha Allah za'a kiyaye yanzu kiyi hakuri bata kyauta ba za'a duba korafin, nima ita ta tasoni na dawo ba Shiri wallahi hajiya yarinyar nan rikicinta yayi yawa".
"To ai tayi mini dai-dai ashe jikar tawa tasan kanta zo Nan Yar albarka".
Gurinta tazo ta zauna a kasa kusa da kafarata tana fadin "Hajiya Ina kwana?".
"Lafiya kalau ya jikin naki?"
"Nifa yanzu lafiya ta kalau ba damuwar komai".
Shima Muhmud Zama yayi kusa da ita da gani da shakuwa Mai yawa a tsakaninsu.
"Hajiyarmu kwana biyu Shiru ko nemana bakyayi ko?".
"Kaji kinibibi ta Ina Zan nemeka bayan kayi gudun hijira".
Dariya ya kamayi har ya bawa Zahra mamaki Daman Yana dariya haka.
Tashi tayi duk da Batasan Kan gurin ba Amma tana tunanin kitchen ne a cikin corridor din dake jikin dining area.
Babban tray ta dauko ta sako ruwa da lemo da Madara da plates ta dauko warmer din da aka zuba pepper soup din turkey din ta nufo parlourn ta dire cener table dake gaban Hajiyar tana fadin gashi Hajiyata ki Sha ruwa kafin nayi Miki girki yau fa a Nan Zaki wuni tunda oga ya dauke min Aunty Rukayya ko sallama bamuyi ba".
Inda Sameer din yake Hajiyar ta kalla "baka kyauta ba ai sai suyi sallama Mana kaga bataji Dadi ba".
"Ai zata dawo tunda zamuje Azare Nan da jibi".
Zahra na son taji ba'asin za'a tafi a barta Amma ba hali Dan tunda suka shigo ta kasa had'a Ido da Sameer da gaske ba karamar kunyarsa takeji ba.
Fita sukayi dare suka bar hajiya da zahrar.
Hira Hajiya ke Mata sosai tamkar sun shekara da sanin juna, taci Naman sosai Tasha madarar tana fadin "irinta muke Sha a makka laban kuke cewa ko tunda Sameer yace min mamarki balarabiyar Jordan ce ko?"
"Eh 'yar can ce".
"Ikon Allah ke Kuma Allah ya kaddaro naki mahaifin a wannan nashiya tamu, ai Sameer ya bani labarinki batun yanzu ba tun lokacin da mijinki ya kaini jidda akayi min aikin Ido da yaga wata yarinya diyar larabawa yake bani labarin ya ganki a jirgi keda wani mutum ko mahaifin ne ko Kuma dai mariki ne basu ba, Saida za'a daura Aurenki yazo yake dauko min tsohon zancen harna gane nace nasa a Ina suka laluboki yace min ikon Allah ne ya hada ku, daga Nan ban Kara ce masa komai ba, Fadima ki rik'e mijinki da kyau Yana sonki yanda Baki zato tun Baki San meye so ba yake Miki shi, kingan shi nan tun suna makarantar sakandire suke tare da Sameer Bai yadda shi ba, da Allah ya daukaka shi saiya Kara janyo shi jikin shi duk inda ya saka kafa Sameer yake aje tashi, duk abinda Sameer ya mallaka mijinki ne sila komu iyayensa da kakanni muna cikin cin arzikin".
Zahra abin jinsa take wani bai-bai me hakan yake nufi ne wai? Ana nufin Mahmud ne ubangidan Sameer ko me ake nufi? Lallai biri yayi kama da mutum duba da yanda suke rayuwa a Nan daga lokacin da sukazo garin zuwa yanzu kusan umarni ne oga Sameer yake karba kawai kasa hakuri tayi Saida ta tofa tata tambayar.


"Wai ni Hajiya waye Mai gidan nan ne? na Ya Sameer ne? ko kuma na wani abokin nasu ne? Nag?????
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
 a ya sakar musu ragamar ko Ina na gidan Baya tsoron abinda zeje yazo,nifa tsoro ma yake bani kamar baza'a mutu ba gaskiya ya mayar Dani gida inda nafi wayo, anan mutum saiya shagala da duniya wallahi".
Baki Hajiyar ta rike tana yiwa zahra wani kallo.
"Amma yarinyar nan lamarin ki da sauran gyara, gidanwa ze daukoki ya kawo idan ba gidansa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login