Showing 165001 words to 168000 words out of 280244 words

Chapter 56 - AUREN HUCE HAUSHI complete

07 Feb 2026

1096

tace ta rubuta Miki bayanin komai, idan an kwana biyu zakuje ki gaisheta kiyi Mata ta'aziyyar abokiyar zamanta Hajiya sabuwa ta rasu".
"Allah sarki! Mutuniyar kirki Allah ya jikanta,Kuma kudin fa yayo min text yace a cikin Account dina ya ciro tunda ATM Dina Yana gurinsa".
"To ki aje a gurinki ni dai babu abinda zanyi dasu".
Haka zahra ta debe ta mayar jaka badan ranta yaso ba.
Har ta Fara tafiya Ammah tace ta leka ta yiwa Mama sallama.
Tayi knocking ya Kai sau biyar Amma hiru ba alamar za'a bude, dole ta baro kofar ta nufo ammah dake tsaye tana kallonta.
"Kije kawai mutum na jiranki, ki duba min malam din saina shigo da safe in Sha Allah".
Ta fada Zahra ta juya ta fice, tana ficewa aka bude kofar parlourn na Mama, wata mace Ammah ta gani ta bude tana Dan dube dube, a haka Ammar ta koma ko kallonta Bata Qarayi ba.

A wata sharceciyar mota Zayyan yazo daukarta,ba wadda sukazo a ciki bace ita lamarin nasu ya daina Bata mamaki dukkansu fuska biyu ke garesu a nan daban a gefe ma daban.
Sun dauki Ido lokacin da suka fito da Alama tun shigowarsa ake dakon ganin waye a ciki, dadin abin ma da ba'asan waye a cikin ba tunda daga cikin gidan suke fitowa ko shiga, Kuma ansan Mai gidan Shima a jikensa yake danma shi ba mutum bane me fariya.
Har suka karaso Yana waje a tsaye, fitowa Zayyan yayi daga mazaunin driver ya nufi inda Mahmud din yake tsaye, magana taga Mahmud din yana yiwa Zayyan kafi ya juya ya nufi parking lot na Asibitin,shi Kuma ya tako ya nufo ta Yana amsa waya

Hannu ya saka ya bude side din da take zaune baice Mata komai ba hannunta kawai ya riko ya fito da ita.
Saida ya gama wayar wadda ta fuskanci akan dai lalurar Baba malam ne yake yinta.
"Precious guduna kikeyi ko?".
Ya fada Yana kokarin rungumota jikinsa.
"Dan Allah ka Bari da mutane fa kaga can".
Ta nuna Masa wasu Mata da suka doso gurin da suke tsayen.
"Shine me Dan sun gani haramun na aikata?".
Kai ta girgiza tana Fadin.
"A'a Amma ana barin halas ko dan kunya, wata Kila ma nasansu".
Bai Kara ce Mata komai ba saboda mutanen sun doso inda suke.
Ba zato zahra taji an ambaci sunanta, da sauri ta juya, Maman mujiba ce da wasu matan unguwa suka shigo diba malam din,da sauri zahra ta Dan ja baya tana fadin.
"Sammunku Mama, Ina yininku".
Da fara'a suka gaisa, sannan Mahmud ya gaishesu, har wata daga cikin matan ke fadin.
"Ko shine Almajirin na Malam".
Kafin zahra ta samu zarafin magana Mahmud ya rigata.
"Eh nine Mama"

"Kai Dan Nan! To ai babu kama, mu ba haka labarin yazo Mana ba wallahi gaka nan wanke hannu daka tab'a, kamar Dan gidan shugaban Qasa".

Da sauri Maman mujiba ta kwabi Mai maganar.
"Haba laure menene haka kikeyi Dan Allah, Zahra Allah ya Kara sauki sai anjiman ku".
Tayi gaba da gani bataji dadin abinda Lauren tayi ba.
Saida suka bacewa ganinsu zahra tayi masa kallon mena fada maka?.
Rausayar da Kansa yayi Yana dage Mata girar idonsa irin I don't care din nan.
"Matar Dan malam ai da nasan da 'yan tsirku a cikinsu babu abinda ze Hana nayi abinda zata baza a unguwa da safe".
Zare sexy eyes dinta tayi tana kallonsa.
"Tab daka Kira min Ruwa. Daman ya lafiyar kura balle tana hauka".
"Kai! lallai yarinyar nan kinji Hausa".
Dariya ya bata, sunanan tsaye har zugar su Mamar mujiba suka fito,Basu dawo ta gurinsu zahrar ba ta can bangaren suka wuce.
Lokacin da suka shiga Habib ne kadai a dakin Yana kokarin bawa Baba malam fura.
Ganin shigowar su zahra malam din yace ya dakanta.
Da sauri zahra ta nufi malam tana fadin.
"Sannu Baba malam Allah ya baka lafiya yasa kaffara ne".
Da murmushi a fuskarsa ya amsa.
"Allahumma Amin Fadima Allah yayi Miki Albarka ya baki zuri'a Mai Albarka yanda kikayi Mana biyayya Allah ya Baki 'ya'yan da zasuyi Miki fiye da wadda kikayi Mana,kibi mijinki mutumin kirki ne Mahmud ko bayan Raina nasan baze wulakantaki ba in Sha Allah".
Nan da Nan idonta ya ciko da hawaye Wai Baba malam ne yake a haka.
"Kada kiyi kuka Fadima shi baya maganin koma Addu'a da hakuri sune abinda bawa zeyi, tunda mutum Bai Isa ya gujewa kaddararsa ba kinji. Daman haka rubutun kaddarar yake sai hakuri da abinda Allah ya hukuntawa bawa, kaita gida ku huta tun safe kake tsaye Allah yayi Albarka".
Har gurin mota Habib ya rako su suna tattaunawa a Kan maganar Sameer na fita wajen, ganin wannan motar da Sameer yazo da ita gurin yasa Habib fadar.
"A'a Ashe oga Sameer be tafi ba?"
" Kamar Yaya meka gani? ya wuce tun yamma".
Motar ya nuna da hannu.
"Wannan data dauki magana mana".
Ya fada Yana Dan murmushi.
"Saboda tsaro ya barta Wai tunda yayi yamma sosai gara yayi badda Kama ya wuce saboda yanayin kasar kada ko an saka Masa target a hanya".
Ita dai zahra tana jinsu tasan kawai bada kafa ne Amma ba Wani Nan.
Tunda suka fito yake faman waya da Sameer ganin ba hanyar Daya kamata subi yake biba yasa tayi Masa magana, hannu ya daga Mata kawai, sai ta zubawa sarautar Allah ido. Shiga Nan fita can sai ganinsu tayi a wata sabuwar unguwa da masu hannu da shuni sukafi yawa a cikinta, sau biyu ta taba zuwanta Daya gidan Aunty safiya dayan Kuma Hameeda ta rako gurin kawarta.
Dai dai wani gida Mai azabar kyau sosai. Dan yafi duk sauran gidajen layin kyau ko Ina tar da haske, gidan plat ne. Horn Daya yayi aka bude katafaren gate din, a hankali ya sulala ciki.
Kallon tambaya take Masa shi Kuma yayi fuska, motar da Sukazo a ciki ta gani a parking lot, sai Kuna ga Zayyan ya rufe gate din ya karaso yana yiwa Mahmud barka da zuwa, ita Sam Bata gane waye ya bude gate din ba Saida ya karaso sannan ta gane shi, da gaske ta daina mamakinsu ko kadan.
Kin fitowa tayi Saida ya zagayo ya bude mata kofar.
"Fito Mana madam ko saina daukeki ne?".
Narai narai tayi da idanunta.
"Nan Kuma gidan waye? Dan Allah kada kasa kaina ya buga abubuwan sun Fara fin karfin Karan karamin tunanina, tunda aka daura min aure da Kai Kullum da abinda Zan gani a tare da kai, gidan Zama wannan baka ajeni a standard gida ba muke nan tsalle-tsalle tamkar matar Dan kidnapping".
Waro Mata idanunsa yayi masu rikita Mata lissafi a can baya.
"Au ke sai yau kika sani? Oyah sakko kina Bata mana lokaci Ina da abinyi".
Jiki ba karfi ta sako farar k'afarta sol wadda shaken ya haskakata ta fito tana karewa gidan kallo.

Kafin suje har Zayyan ya bude kofar parlourn tana shiga taga tamakar an dauko parlourn gidan BAWO ROAD an aje a Nan. Bata kulashi ba ta wuce ciki.
Ba Wani bakunta harta Saba da irin wannan rayuwar itama, Bata da kayan kah babu na rataya duk inda suka Sauka gida ne.
Ba Wani bayanin wanka tunda yanzu ba dadewa tayi, canza Kaya kawai tayi ta saka nighty tayi kwanciyar tana cika tana batsewa shi be San haushinsa take ji ba ya hanata kwana a gurin Ammarta kamar wani abun azo a gani zatayi masa.
Har tayi barci be shigo ba Batasan inda ya makale ba.

Tunda Mahmud ya shigo dakin da yake kusa da Wanda Zahra ta shiga yake faman research akan Asibiticin guda biyu Daya karbi website dinsu ya shiga yayi bincike sosai,sunyi commucating sosai da Sameer akan maganar Asibitin Daya Dace, daga karshe Mahmud yace Sameer din ya biya chargers din komai na Max surgeon din idan da yuwuwar gani doctor daban Fortis din Suma sai aje. Bashi ya shigo bedroom din da zahra take ba sai kusan karfe biyu da kwata na dare, barcinta take sadidan da Alama ta tattarra shi ta Zuba a dust bin.
Wani murmushi ne ya sille Masa,kalamanta ya tuno na dazu Wai matar Dan kidnapping.
"Zakiga kidnapping iya ganinki Dan idan na sakayaki Zaki gane na iya kidnapping na kirki.
Saida ya gama duk abubuwan da zeyi sanan ya hayo Kan gadon kusa da ita yana zare blanket din, jikinta ya shige ya sakata a jikinsa sosai ya maida blanket din ya rufe su, lif tayi a jikinsa kamar Daman jira take.
Gyara Mata kanta yayi a gefen kafadarsa, a hankali ta sauke numfashi, Shima ajiyar zuciyar ya saki barci yakeji sosai dan yayi mamakin yanda har ya Kara Kai wannan time din baiyi barci ba.
Bayan sallar Asuba ma Kara komawa barci sukayi manne da juna, da gaske zahra ta dauki Shawarar Aunty zilai data ce Mata duk inda ya kaita ta karbeshi a gidanta ne kawai, kenan da hasashen da tayi a Dan zaman da tayi dasu.
Ring tone din wayar ta ya tashi Mahmud lokacin goma da Arba'in da biyu Hannu ya saka ya dauko wayar.
*AMMAHTA* ya gani baro-baro a Kan screen din Yana yawo, nauyin daukar Kiran yaji saiya shiga Yi Mata abunda dole ta tashi.
"Wash Allah menene haka Dan Allah?"
Dan bakin ya sakarwa kiss Yana Mika Mata wayar Yana fadin "Ammah na Kira yayi toilet. Dan ba karamin barci sukayi ba yaso ace karfe tara ya wuce Asibitin to shi barci ba'a ci Masa bashi.
Kiran Ammar zahrar tayi.
"Ina kwana Ammah".
"Lafiya kalau Alhamdulillahi, Abincin break fast ne magaji da Musaddiq suka kawo muku sunata knocking ba'a bude ba sunce babu alamun mutane ma a gidan".
Ajiyar zuciya zahra ta sauke cikin raunin murya tace.
"Ammah! yanda kike tunanin abun yafi nan fa, ina wannan sabuwar unguwar dana taba raka Hameeda wadda nake baki labarin ta? Wallahi nan ya kawo mu nayi masa magana yayi min banza,Dan Allah kizo kiga gidan sai kiyi Mana shari'a".
"Ikon Allah, Ina tambayarki kina min korafi kiyi hakuri Mana abi komai a sannu, yanzu dai ki Fadi Address din sai su kawo muku".
"To ai Nima bansan sunan unguwar Nan ba fa wallahi na manta ".
"Ikon Allah, Bari magaji ya Kira mijin naki saiya fada Masa".
"To Ammata saina zo anjima".
Tayi saurin kashe wayar Dan ma kada ta hanata Dan wallahi Qafarsa Qafarta.
Blanket din ta ture ta tashi daidai lokacin da Mahmud ya fito Yana kokarin zare pyjamas din jikinsa Kira ya shigo, magaji ya gani bayan sun gaisa ya shiga yi Masa kwatancen gidan.
Armless da three quarter ya saka farare sol na kamfanin Adidas ya dauki wayarsa ya fice daga dakin.
Har waje ya fito Yana son yanayin unguwar babu hayaniya sosai, tun daga nesa magajin ya hango Mahmud a ransa ya ayyana.
"Ba dai daga wannan gidan ya fito ba?".
Har suka Karaso be gaskata abinda idanunsa ke fada Masa ba, dan totally shi kansa Mahmud din bana gidan Baba malam bane wannan wani ne yaje gani daban a gabansa Mai wata irin haiba da Kamala, dan hutu domin ko ba'a fada ba fatar jikinsa kadai ta nuna kanta, suna kokarin tsayawa sukaga an bude katafaren gate din.
Bai shiga parking lot ba inda yaga motoci a kalla sun Kai hudu ko wacce ta millions of naira.
Fitowa magaji yayi suka gaisa da Mahmud Musaddiq ma ya gaishe shi sun gaisa da Zayyan ma, backseat ya bude ya Ciro babban basket da Wani k'arami kuma, Zayyan ne ya amsa da sauri yayi ciki dasu, ba yanda Mahmud beyi da magaji ba ya shiga ciki ba Amma yace a'a sai Wani lokacin, Ammah na jiransu ze kaita duba baba malam,Musaddiq ne ya kwabe fuska kamar zeyi kuka dole magaji ya jira shi a mota Yabi Mahmud ciki.
Gidan kawai magaji yake kallo Yana jinjina Kai a fili yace.
There's something behind".
Basu Dade da shiga ba suka fito harda zahrar ta saka wata abaya baka all stones sai walainiya take.
Magaji yaso yayi halin nasa na tsokana sai Kuma yaji baze iya ba sunyi Masa wani irin kwarjini ita da mijin duk yanda taso ta ta tabo shi saiya share ta.
Saida suka fice sannan ya rungumeta suka koma ciki Zayyan dai sai kauda Kai yayi, yana mamakin ogan nasa yana son yarinyar sosai Saida hakan Bai Hana ya gwada Mata halinsa ba.

Ai Auta kamar jira yake magaji ya tsaya ya Kama kofa ze bude ya jita a rufe, magajin ya kalla.
"Ya magaji ka bude min".
Ido ya zare Masa Yana fadin.
"Na rantse da Allah naji maganar zahra da gidan daka nace saika shiga a bakinka ka fadawa wani saina zaneka tas, kaji abinda na fada maka?".
Kaiya gyada.
"Oya fita.
Yaron ya fito jiki ba kwari yaso ya kwasa a guje tin kafin ya shiga daki ya Fara fesa labari, sai Kuma magaji yayi Masa karan tsaye.

Sai wurin Daya su zahra suka baro gidan Dan tasashi gaba tayi da shagwabar data saka Saida ya Dan mayar da yawunsa sannan sukayi wanka suka fito.
Yaso ya wuce Asibitin direct to Saidai baya son zuwa da ita da dare ma sun dauki idanu bare da rana, motar ta suka shigo gidan Baba malam suka Fara zuwa a kofar gida ta barshi suna gaisawa da dalibai manya da Yara anata jajantawa juna, masu gaje gani sunata Yi Masa Dan biki akan canjin da suka gani a tare dashi.
A tsakar gida zahra ta samu iya Abu tare da wasu matan unguwa sunzo jajanta mata, da farko Basu gane zahrar ba Saida ya matso kusa sun dai amsa sallamar ta, rike Baki Iya Abu tayi.
"Wace bakuwar jidda nake gani haka? Zahra'u haka Kika koma Masha Allah! Dana ya iya kiwo wannan kikayi shekara ai sai an duba fuska a jikinki".
Ta fada tana dariya.
"Kai Mamana".
Karaf a kunnen Mahmud da yayi sallam ya shigo.
Bai San lokacin da murmushi ya kubce Masa ba sai yaji ta Kara Qima da daraja a idanunsa,wato maganar Daya taba fada Mata, akan fadin Iya Abu da takeyi gatsal tayi tasiri kenan a zuciyarta.
Gaishesu tayi tare da jajanta Mata jikin Baba malam tana fadin.
"Na daina kaka dake Ni yanzu uwata ce ke Kuma kin.....
Bata karasa fadar abinda tayi niyya ba taji matan na gaisawa dashi Sam bataji shigowar sa ba tunda baya ta bawa kofar shigowar.
Har kusa da iya Abu ya zagaya ya gaisheta tare da Kara jajantawa juna tana fadin.
"Kaji sabon kinibibi gurin zahra'u ko? Wai nice mamarta saboda ta aure min da shine zata Fara ladabin gangan".
Dan kallonta yayi a fakaice, baice komai ba ya tashi ya fita waje.
Bata Jima sosai ba ta fito can ta hange shi suna magana da wasu matasan unguwar, wucewa tayi ta nufi gidansu Yana kallon yanda Idanu sukayi Mata caaaa kamar yaje ya boye abarsa.
Lokacin data shiga Abba na kokarin fita a mota shi da Bala driver.
Yana ganin zahra ya saka Balan tsayawa harta karaso inda suke cikin murna take fadin.
"Abbana ka manta dani ko?".
"Haba uwata kin taba ganin da ya manta da uwarsa kina raina Kullum ai muna waya da mijin naki Yana kirana ya gaisheni yaron kirki wallahi malam Bala sai yanzu nake ganin alfanun had a uwata da yaron Nan, tun ranar da muka ganshi nasan Mai nagarta ne"

"To shike nan tunda ya kwace min kai Abbana".
'yar dariya yayi kawai wato halinta yana nan.
Tsugunawa tayi tana gaishe da Abban sannan ta jajanta masa jikin Baba malam, ta gaishe da malam Balan ma, Abban ne yace
can ma zeje Asibitin jiya Daya shiga gurin likitan dake kula dashi ya fada Masa Wai Sameer ya Barbi komai qungiyoyin dake bada tallafin makarantu da dalibai zasu fita dashi zuwa India, shine Zan koma na bibiyi lamarin kada abin ya Zama wasa tunda ciwon bana Wasa bane".
"To Abba saika dawo Allah ya bashi lafiya".
"Amin" suka amsa.
Suka fice ita Kuma ta shige.
Suna fita Mahmud na kawo Kai a motar zahra, parking suka gyara su Abban, Mahmud ya fito ya nufosu da Dan hanzarinsa suka gaisa da Abban ya jajanta Masa Matsalar Baba malam din sun Dade suna mag???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?anar fita wajen inda Mahmud ke bashi assurance Kan fitar, inda yake fada Masa yana Jin Nan da kwana uku zasu iya samun Visa tunda emergency issue ne na Asibiti.
Sukayi sallama su Abban suka wuce shi Kuma ya karasa gidan, very luckily Yana shiga Abdul Hakeem na fitowa cikin Shirin fita Yana ganin Mahmud ya karaso da sauri Yana fadar.
"Yanzu nake tunanin kiranka a waya za muyi wata magana da Kai Ina fatan ban takura maka ba? idan babu damuwa ka hakura da shiga cikin muje Asibitin daga baya sai mu dawo nan din tunda gaiswa ce kawai zakuyi dasu".
"Ok ba damuwa muje kawai next time na shiga".
Front seat ya bude ya shiga Yana fadin.
Ai dama nina karb'i tukin.
Suna tafe suna Hira wadda ta dangance su irin ta abokai aminai.
Kiran Sameer ne ya shigo wayar Mahmud suka Fara wayar yayin da Abdul Hakeem ya shiga duniyar tunanin yanda sukayi da Ammah dazu da da safe bayan su magaji sun dawo labarin da Musaddiq ya Bata yayi matukar daga hankalinta sosai da kyar Abdul Hakeem ya tausheta akan tayi hakuri yayi Mata alkawarin bincikar Mata waye Mahmud tun daga Nan har sokoton da yake Fadar can ne mahaifarsa,to gudun kada a samu subutar bakin Ammar ta kasa hakuri tayi Masa maganar yasa Abdul Hakeem dafe shi ya Hana shi shigar.
Suna shiga bangaren da aka kwantar da Baba malam din sukaci karo da Habib sun taho da Dr Omole da sauri wasu likitocin biyu suna biye dasu da gani dai akwai abinda ya faru.
Suma su Mahmud da sauri sukabi bayan su.

* AUREN HUCE HAUSHI*

MAMAN FATEEMAH.

Da sunan Allah Mai Rahama Mai jinkai salati da daukaka da Aminci su tabbata ga shugaban mu Annabin Rahama Muhammad s.a.w.w.

Page 60.


_____Suna biye da doctors din har suka shiga dakin abinda suka gani ya daga musu hankali, jikin Baba malam ne yake wata irin jijjiga Kamar Wanda yake ciwon tsintsinko irin na Mata masu haihuwa Abba dasu Abubakar suna ta faman tofa Masa addu'a, ganin lotoci sun shigo yasa su Abba suka matsa suka Basu guri, tamabaya likitan ya jefo musu.
"Ko akwai abinda ya faru Wanda ya haddasa Masa hakan ko Kuma an fada Masa abinda ya tada Masa hankali ne?".
"A'a Babu komai doctor daga barci ya tashi da wannan abun".
Abubakar ya fada, yayin da Abba ya Kara da "kwarai kuwa muna zaune ya farka da wannan shivering din".
Jinjina Kai doctor Omolen Yaya Yana faman gwaje-gwajensa, rubuta yayi a takarda ya Miko Yana fadin.
"Ayi maza a kawo wannan alluran yanzu za'ayi Masa".
Habib ne ya karba ya nufi kofa,mahmud ne ya ya biyo shi da sauri suka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login