Showing 141001 words to 144000 words out of 153980 words
"Kuyi Mata gyaran komai please Karki Bari tayi aikin komai na baki amanarta"Insha Allah Yaya"Chuchu ta amsa Tana dariya kasa kasa"Zahra ko Kallonshi kawai tayi Ganin ya kashe Mata ido daya ya sanyata kasa da kanta Tana murmushi Saida MD ya fita su chuchu suka samu damar zolayar Zahra Asmy ta ce"Kuntafi Kuna love kunbar Yara sai kuka suke "Dariya chuchu tayi ta Ce "Antafi sama musu kanne dai Dan matar Yaya twins da triple zata dinga Haifa Mana kafin 5 years gidan ya cika da Yara tako Ina "shegantaka sosai suka dinga Mata wani ta biyesu wani ta kyalesu yanda MD ya fada su chuchu sukayi aikin komai Banda Zahra da ta kula da Yaran Bayan sungama Mata sauran gyare gyare sun karaa gyara Mata kitchen dinta da jeren da bai musu ba suka sake Wajen ukku sukaji knoking chuchu ta je ta bude Ganin aunty zey Ce sosai tayi murna Bayan ta shigo parlourn Gaisheta Zahra tai ta amsa cikin girmamawa a Tare da cewa "ya bakunta "Alhmdllh"Ta fada kasa kasa "Masha Allah Ubangiji ya bada zaman lfy Mai dorewata fadad'a Tana daukar Zahra ta Ce "Nayi kewarki Ammynmu"Saida ta danyiwa little wasa kafin ta Ce "ki yafa gyale maza ne zasu shigo da Kaya"to "Zahra ta fada gyale Zahra taje ta dauko ta yafa Fita zey tayi ganinta sukayi da kawai Maza na shigowa da jibga jibgan akwatina na gani na fad'a Saida aka jere akwati hamsin reras a palourn Sosai su kansu su asmy sukayi mamakin kayan lefen zey na murmushi ta Ce "To Amaryarmu ga lefe dai munkawo na Bangaren Ango sai Kuma na Bangaren Ammy da chuchu munji dai su shiru"dariya chuchu tayi ta Ce"Naku wasa ne Aunty Zey kikaga namu saikun Raina Naku"Dariya zey tayi ta ce "Ah to muga nakun Mana"Sosai Zahra tayi mamaki Kamar tayi magana yanzu wanna uban kayan duka lefantane ikon Allah "Asmy Ce ta Ari bakinta ta Ce "Kai Masha Allah Aunty gaskiya Kaya sunyi Allah Ubangiji ya saka da alkhairi ya Kara bud'i"chuchu ma ta Ce "To mungode Dai Allah ya saka da alkhairi Bari mu bude muga ko kunyi Abun kirki"ta fada suna Fara bubbude kayan na gani na fad'a mikewa zey tayi ya Ce "Bari na wuce naji Ammy nayimun waya zantafi da little anjima ya taho da ita saina dawo"TO aunty angode Allah saka da alkhairi"ta fada tare da mikewa tarakata har bakin kofa kafin da dawo ciki sai sannan aka Fara bude kayan da ita dariya chuchu tayi ta Ce "Waida Aunty Zey kikejin kunya shiyasa duk Kika wani daddare Naga Baki sake da ita ba kodan hakane Tana da wuyar sabo miskilancin tsiya gareta Anna ke ai Naga Tana sake Miki Sosai ki saki jiki da ita Bata da matsala wlh sannan ko wasu shawarori kike da bukatar irin Naku na masu aure zata taimaka Miki ba ruwanta "chuchu ta fada Tana dariya "Girgiza Kai kawai Zahra tayi ta ce"Insha Allah Abun bamu Saba Sosai ba shysa Saida suka daddaga kayan kowace akwati shake take da Kaya Banda akwatin zinare ma guda na sarkoki da awarwaro da zobuna Masha Allah anyi Kaya na kece rainin sai magriba su chuchu sukayi mata bankwana suka wuce Ganin dawowar MD
Da dare suna manne dajuna ya ce"My princess Kinga kayasunyu maki ko"Murmushi tayi ta Ce "Eh Ya musty Nagode Allah saka da alkhairi ya Kara bud'i "Ameeeenmmn matar aljanna "ya fada Yana juyar da ita washegari Nanny din su Yaran biyu sukazo Wanda Ammy ta daukesu suka Fara kula dasu inda iyayen sure zuba love dinsu ba Kama hannun yaro Dan MD fitama gagararsa takeyi yini yake a gida Sai da suka kwana biyar kafin su fito ya zagaya da ita gidan taga ko ina Wanda wani wajenma a mota yakaita saboda Nisan musamman katoton lambun Gidan Masha Allah gsky Gidan yayi matukar kyau cikin gidanko ko palour ne guda takwaas kowanne shake da kayan waje Banda biyu da suke dauke da irin namu na Nan nja saidai Suma Masha Allah Anan Zahra ta gane sune Wanda su baba sukayi Mata kenan Sosai ta Yaba da irin kokarin da baba yayi bedroom din dakinko 12 kowanne Shima shake da Kaya nasu tiple ma cike da kayansu Banda dakin wasansu Wanda aka Sanya kekuna da abubuwa a compound gidanma had a Bangaren wasan Yara an zuba uban Kaya shakatawa baby banbanci da park ranar Ammy ta turo da nata Lefen akwati Sha biyar mamaki duk ya Gama cika Zahra to su wanna wani irin kudine garesu Kamar basusan darajar kudi ba Cikar Zahra sati a Gidan Tana kallon palour MD ya shigo Tana Ganin yanda take fara'ar tasan akwai magana wajenta ya nufa tare da rungumota ta gefe ya Ce "rufe idonki"Murmushi tayi tare da rufewa "Ba ayi two second ba ya Ce "open your eyes"budewa tayi taga ya Sanya mata kwalin waya kirar iPhone14 a hannu wara idanu Zahra tayi ta Ce "Wow"murmushi yayi ya Ce "Surprised na farko kenan tukuicin budurcinki "Wow Zahra ta Kara fada cikin doki ta Ce "Thanks thank you so much my Love Allah ya saka da alkhairi ya Kara bud'i "ameeen princess"Kafin yamikar da ita yaja hannunta sukayi waje daidai Wajen dalleliyar jar motar da Zahra Saida ta tsorata da Ganin kyau irin na motar ya jata daidai mota ya tsaya Yana murmushi ya Zaro"Key"Din Motar Ya Mika Mata ya ce"Ga motarki my love Tukuicin bani farinciki da bawanda ya bani saike na Haifamun triple da kikayi"sannan Ya k'ara d'auko wani Key d'in ya mik'a Mata ya Ce "Wannan Kuma makullin gidanki ne Dake abuja na sanyani kuka da kikayi na rubuta da shaidu da komai ya Zama naki halak_Malak "Ai Zahra daskarewa a Wajen tayi ta rasa want irin farinciki zatayi kawai sai fad'awa jikinshi tayi batasan sanda ta fashe da wani kukan farinciki ba cikin kuka ta ce............ ✍️
*Domin magana da marubuciyar Kai tsaye neman Karin bayani tambaya ko Kuma sayan complete kardai ku Manta Auren wata Tara littafin kudine zaku samu complete dinshi ne Bayan Kun biya 500 kachal domin neman Karin bayani ku tuntubeni Akan number wayata Kamar haka 07026166536*
_*Miss Hajo Ce*_🤙
[10/3, 7:17 PM] Mother Mamy: 🅿️...........*91 & 92*
&
🅿️..........*93 & 94*
"Ki kwantar da hankalinki Hajiya insha Allah zai huce idanma bai huce ba ni da kaina zankoma na basa hakuri"Baba tsoho ya fada kafin yayiwa Ammy bankwana ya koma masaukinsa Da aka saukesa a gidan"Sosai Md ya burkuce ya shiga tsananin tashin hankali na rashin Zahra da yaransa gaba daya baya cikin nutsuwa cikin kwana biyu harya zabge ya rame saboda tashin hankali da rashin bacci Ga ko abinci baya iyaci saidai ruwan Lipton idan ya zauna ba Wanda yake tunanin irin Zahra Shi kanshi baisan Yana mata so har irin haka ba sai yanzu da tayi nesa dashi Gaba daya yashiga tashin hankali rasa Wanda zaiyi shawara dashi yayi sai jabir ya bude wayarsa ya Kira Dan tun Kiran da iyayen amira suke mashi ya dameshi ya sanyashi kashe wayarsa .....bangaren Zahra Itama Bata da wata walwala Sosai dukda kannen babanta na kokari a kanta Sosai baba ma Yana nuna mata ya hakura Dan har yaran saiya daukesu su yini wajenshi Amma Kuma har yanzu batajin Tana da walwala Sosai takejin kewar su Ammy ga Kuma tunanin Md da tarasa dalilin da Indai ta zauna ba Wanda take tunawa da irin rayuwar da sukayi a baya irinshi yauma Tana kwance Tana tunani batasan lokacin da wasu hawaye masu dumi suka zubo mata ba Haka kawai data zauna saita dinga tunaninsa ta rasa fahimtar abundanda ke damunta game dashi lura da rashin walwalar na Zahra ya sanya Mama habi tafiya da ita gidanta katsina Dan taci gaba da Kula da ita Komawarta katsina Zahra ta danji sassauci saboda koba komai akwai yaran mama habi Sa'anninta da Wanda suka fita sun zauna su danyi hira ta rage kawaici triple ko Daman idan ba yunwa sukaji ba tofa ba a kawosu wajenta suna hannun mama habi da yaranta haka dai rayuwa taci gaba mama habi naci gaba da yiwa Zahra gyara Sosai dukda damuwar da tasa a ranta ta rame yaranta ko sunyi b'ul b'ul abunsu gwanin sha'awa kamanninsu da mahaifinsu na Kara fitowa....a halin yanzu md kullum cikin zazzabi da ciwon Kai yake ya rame Sosai gashi yaki yaje asibiti Ammy ko itama duk hankalinta ya tashi ganin yanda beloved son din nata ya koma ita kanta batasan md Yana yiwa Zahra har irin wannan son ba sai yanzu lallashi ba irin Wanda batayi Masa ba Amma yakiji Baba tsoho ko Yana daya daga cikin gidajen Baki na md inda Ammy ta saukesa kafin Shima su waiwayi jigawa wajen ahalinsa sun Bari dai a gama da matsalar Zahra Ranar da Zahra ta cika sati ukku da tafiya idan ka kallesa saikayi Masa kuka saboda yanda ya firgice kamar ba mr MD billonia ba matashi da kudi Ranar ji yayi bazai iya jure rashin Zahra ba saboda yanda yakejin zuciyarsa kamar zata tarwatse a daddafe ya Kira chuchu a waya Koda tazo saida tayi hawaye ganin yanda Yayan nata ya zabge Address din garin da suka Kai Zahra ta basa tare da fada mashi drivern da ya kaisu baiyi wata wata ba ya Kira drivern a tare da jabir suka tafi garinsu batsari Wanda tafiyar sirri sukayi Allah yasa Drivern ya gane Gidan Koda sukayi sallama da bappa ya fito ganin Baki ne ya sanyashi masu iso har cikin gida Md kanshi Kasa ya gaishesu Har baba da yake zaune baba ya Gane jabir cikin girmamawa suka gaisa Yana tambayar jabir ya mutanen gidan sannan yayi mashi godiya akan Abunda yayi mashi Lura da shine baban Zahra ya sanya mD Kasa had'a ido biyu dashi dakyal jabir ya iya bude Baki ya ce "Baba Daman magane ce tafe damu akan Zahra"Inajinku wace magana kenan"Baba ya fad'a"saida jabir yayi Jim kafin ya. Dago ya ce "Daman hakuri ne muka zo mu Kara Baku akan Abunda ya faru Dan Allah Baba kuyi Hakuri wannan abokina ne Kuma shine mijin Zahra baban yaran shine mukazo mu Kara Baku hakuri "Kallon md baba da bappa sukayi kafin Bappa ya ce "Allahsrk shine yaron kenan To Ai komai ya wuce Hakuri an Riga anyi d'an Adam ai baya wuce rubutun Allah duka abunda ya faru ya faru ne a bisa kaddara da Kuma rabon yaran Nan dan haka daga bangarenmu ya wuce yaro tunda dai ba Zina sukayi ba Aure sukayi har aka haifi yaran ta hanyar sunna kaga ai komai yazo da sauki "saida ya md ya sauke boyayyar ajiyar zuciya "Baba Shima cewa yayi "Ya wuce Allah yafe Mana Tare "Ameen baba mungode jabir ya fada shiru sukayi kafin Jabir ya ce "Sai magana ta gaba baba yace kuyi hakuri Dan Allah ku mayar Masa da Zahra saboda Yana sonta Kuma ba rabuwa sukayi ba "nannefa baba ya murje ido ya ce "baisan wannan Zancen ba "Magiya Jabir ya dingayi Shima md ji yake kamar zai fashewa baba da kuka cike da magiya ya ce"Dan Allah baba kuyi hakuri ku yafemun wlh tallahi in son matata Dan Allah baba kuyi hakuri ku maidomun ita karku rabamu "Saida MD ya bawa bappa tausayi Kallon baba bappa yayi ya ce "Meyasa zakayi haka Yusufu kaida bansanka Da tsauri ba Kayi hakuri a barwa Allah lamarin Nan Karka shiga lamarin aure tunda kaga Allah shine ya hadasu tun farko dukda Bata shara'a a ba akayi abun to me zai Hana abar Masa sauran yayi ikonsa Dan Allah kayi hakuri ka janye fushin Nan Karka shiga ka zak'e cikin lamarin tunda ba a asan Abunda Allah zaiyi gaba ba"Numfashi baba yaja kafin yayi shiru saikuma ya dago ya ce"Na janye fushi na ka nemu yarda a wajenta idan ta amince ba matsala saiku sasinta Allah ya zab'a Abunda yafi Zama alkhairi"wata irin ajiyar zuciya mD ya sauke kafin ya dago ya dinga jerawa baba addu'oi Sosai ya shiga yiwa baba godiya yanda kasan yayi Masa albishir da gidan Aljanna"Jabir ne ya ce"Tana ciki ne bappa"a a a kanwar mahaifinta ta tafi da ita katsina yanzu Tana katsina ita da yaran"Cikin sauri MD ya dago ya ce "Bappa Dan Allah bamu address din gidan da take Dan Allah"Murmushi bappa yayi ya ce "Kai jikannan nawa ka cika azarbabi to bari Nak'i fad'a maka tunda dai Daman kwacen amaryace zakamun "Dan Murmushi MD yayi Yana Kasa dakai Yana Sosa keya"Shidai baba shiru yayi Jabir ne yayi dariya ya ce "A a a bappa ai kayi mata tsufa"Saida suka danyi barkwanci kafin Baffa ya Basu address din gidan Ba yanda baiyi dasu ba Su tsaya ko fura a Dama musu Amma suka kiya saboda saurin da MD yake su wuce katsina kudade bandir biyu md ya bawa su bappa Amma sukaki amsa ba irin yanda baiyi dasu ba Amma suka ki amsa suka kafe ba yanda ya iya sai maida su yayi a yammar driver ya wuce dasu katsina sai Bayan magrib suka Isa garin katsina salla kawai sukayi suka wuce Unguwar su mama habi dake Bayan high court Basu wani Sha wahala ba Wajen gane gidan almajiri suka tura suka ce ana sallama'bayan fitowar Almajirin ya ce "ance wai wa ake nema"Mamy"MD ya fada jabir yayi sauri ya ce "Kace Zahra ake nema"Kallon md yayi ya ce "waya santa da Mamy in Banda Abunka "Dukna riikicene shysa wlh jabir bakasan irin son da nakeyiwa yarinyar Nan ba shiyasa"Dariyar mugunta jabir yayi ya ce "Au Haba yaushe ka Fara son matar Wata tara Kuma tsaki md yaja yace"Kaga matsalata dakai kenan to wannan dai matar ta Har Abada ce Babu rabuwa "Dariya Jabir yayi fitowa Almajirin yayi ya ce "Ancewai Bazata fito ba "OMG"MD ya fada"Jabir ne ya ce "zasuyi tunanin wasune ko samari kaga Tana da aure bazasu Bari ta fito ba fa"Eh Kuma hakane "MD ya fada kafin ya kalli yaron ya ce "ka ce "Baban su Y'an ukku ne yazo"To Almarin ya fada Yana komawa"Ajiyar zuciya mD ya sauke Dan yaji Dadi koba komai ana tsare Masa igiyar aurensa Fitowa Almajirin yayi ya ce "ance wai ku shiga"Ajiyar zuciya mD ya sauke jabir ya bawa Almajirin 2k kafin su shiga Cikin gidan da a palourn Mai gidan aka saukesu Kafin mama habi ta shigo da hijab dinta dafara'a ta tarbesu suka gaisheta Cikin girmamawa Bayan ta zauna ta ce "Kuyi hakuri an tsaidaku waje bamuganeku ba saidaga baya"Murmushi jabir yayi ya ce "Ba komai mama"Madalla Diyarta ce to shigo ta aje musu ruwa da lemo Bayan ta gaishesu ta juya mama habi ta ce "Ku Sha Mana"Jabir ne yasha MD baisha ba "Shiru sukayi kafin mama rabi ta ce "koba a fada ba nasan ga Baban yaran nan ganin Kama karara Masha Allah"ta fada Tana Kallon md "Murmushi Jabir yayi ya ce "e shine mama. Daman zuwa mukayi mu Kara Baku hakuri"A Haba yaron Nan hakuri Kuma na me ai komai ya wuce anzama d'aya tunda harda zuri'a Allah dai ya Raya Ameen MD ya fada Kasa Kasa kafin jabir ya ce "Mungode Daman daga Chan batsari muke munje mun karaba su Baba hakuri Kuma sun hakura harma sun amince da maganar Komawar Tata suma suka fada Mana Nan inda take.akan muzo Kuma mu nemu amincewarku. Da Tata shine mukazo Mama Dan Allah ayi hakuri ta koma dakinta wlh Yana sonta Kuma insha Allah zai riketa da Amana"shiru mama tayi kafin ta dago ta ce "Ai ba matsala tunda Sun amince muma mun amince Allah zaba Abunda yafi alkhairi saiku nemu yarda a wajenta Bari na shiga na turo muku ita "ta fada Tana mikewa ta shige ciki"MD jinshi yayi Cikin wani irin farinciki Jin abun ya Fara zuwa dasauki Koda mama taje ta fadawa Zahra wadanda ke tafe Saida tayi mamaki mama ce ta ce "tashi ki Mike kuje da yaran ku gaisa ko"Zahra kamar zatayi kuka ta ce "Dan Allah akai mashi yaran ni ba sainaje ba"Dukda Tana da bukatar ganin nasa"Tsaki mama habi taja ta ce "Da Allah tashi kibani waje bansan shiririta kije ku gaisa mutanen su taho tundaga kaduna saboda ke Dan iskanci Kiki zuwa ku gaisa maxa tashi kije kafin ranki ya b'aci"ganin ran mama ya b'aci ya sanyata mikewa da Akhbar a hannunta Ta fito MD suna zaune Yar mama habi ta kawo mishi yaran su biyu Amar da Little Sosai ya yaba yaran sun Kara kyau da wayo har Dariya sunayi sunyi bul_bul gwanin ban sha'awa Duka biyun ya dauka Yana musu Dariya ya ce "oyoyo my kids I really miss you so much please karku sake nesa da daddynku zai shiga wani Hali"Daidai shigowar Zahra Cikin hijab sab'e da Alkhbar tunda ta shigo palourn MD ya kafeta da kallo Bako kiftawa yanajin wata irin kauna da soyayyarta na Kara fusgarsa ji yake kamar yaje ya rungumeta Harta zauna Yana kallonta a sace Zahra ta kellesa idonsa suka sartse Cikin na juna sauri tayi ta kauda Kai gabanta na faduwa nauyayyar Ajiyar zuciya mD ya sauke yanajin wani irin sanyi na ratsa sa shiru Zahra tayi Bata tanka ba jabir ne ya ce "Hajiyarmu ina yini Kodai har yanzu fushin ake damu nidai ina bada hakuri Kuma ina wanke laifi na "Dan Murmushi Zahra tayi ta ce "Ina yini Yaya jabir anzo lfy"lafiya qalau ya triple dinmu "Alhmdulillahi"ta fada Kasa Kasa Tana wasa da zoben hannunta"MD bai daina kallonta ba kamar zai cinye ta Biyun ya aje kan sopa kafin ya koma kujerar da take kamar zai shige jikinta saurin matsawa tayi tare da satar kallonsa suna hada ido ta Galla Masa harara"Mika hannu yayi ya amshi little dake Zillo a hannunta Ajiyar zuciya ya sauke tare da kissing din little ya ce "i Really miss you my All above I love you so much my beloved daughter ina sonki Sosai takwarar Ammy na Kuma Favorite wife d'ina gaki Kuma daughter ta "ya fada Yana mata Dariya kamar tasan me yake cewa tahau Masa Dariya hada Zillo "Tabe Baki Zahra tayi Tana Shirin mikewa ya ruko