Showing 147001 words to 150000 words out of 153980 words
sume ma Saida mudan ya gama tonon asirin kansa Yana kuka Yana yayi nadama Yana Durkusawa akan Kakan Zahra ya yafe Masa kasan Dan uwa da d"an uwa sai Allah Sosai tausayin Mudan ya tsargu a zuciyar baba har za a fita dashi Baba ya juya ya ce "Na yafe maka mudan hakkin kasheni din da kasoyi da hakkin kwantar Dani ko yanzu ka mutu kar a tambayeka hakkin Nan na yafe maka"cikin kuka mudan ya ce "Nagode Yaya Saiwataran sai mun hadu a darussalam Kai baka mutu ba Ashe Ni Zan rigaka mutuwa Yaya nayi tsantsar nadama"Daya Daga cikin sojojin da suka zo kamasa suka Tisa keyarsa akayi waje dashi MD ma ransa a matukar bace Yaja hannun matarsa sukayi waje baima waiwayi Amera da take a sume ba Ammy ma da su baba waje sukayi gabaki daya mD da ammy Jin mutuwar Suke ta dawo musu sabuwa har suka Isa gida ammy na tsine mass Tana ja Masa alkaba'i Zahra ko dukta firgice ga Bata Manta ba Jin MD da aka Kira mijinta dashi sunan da bazata Manta Dashi ba Gidan ammy suka sauka Koda chuchu taji labarin Nan itama Nan tashiga tsinenewa Baban Amira har amirar take hadawa Zahra dai batacewa komai hankalinta duk Yana kan mijinta da taga ya firgice fuskarsa ba fara'a ko Zama baiyi ba ya juya ya koma police station Dan hankalinshi bazai kwanta ba har saiya tsaye an yankewa mudan hukuncin kisa Kamar yanda ya kashe Masa mahaifi ranar da dare Zahra tayi Tagumi Akan bed kallon chuchu Dake waya tayi Ganin yanda take wayar ya tabbatar Mata da Adil ne saurayinta Kuma cousine dinta Saida chuchu ta Gama wayarta kafin Zahra ta kalleta ta ce "Dan Allah chuchu na tambayeki waye MD please",Tirkashi chuchu ta fada kafin ta gyara Zama ta ce "Mijinki shine MD momcy Yaya ne MD din ai"Fuskarsa Zahra dauke da mamaki ta ce "Wai kina nufin shine MD dinnan da yayi harbi a gabanmu Wanda na tsana"Kama hannunta chuchu tayi ta ce "Tun lokacin a school naso maki bayani kikak'i fahimta momcy wanna mutanen da kikaga Yaya ya harba Sune wadanda sukayi kisan abokin mahaifinmu da kikejin labari yanzu ranar sun dawo Daga kisan sun kubucewa Yan sanda yayana yakai wajen Wanda dpo ya kirasa ya fada Masa akan ya harbe su Dan Karsu gudu tofa kinji dalilin daya Sanya har Yaya yayi Harbin Nan Amma ba halin sa bane bai taba harbi ba "Allahsrk shiyasa ba ason saurin yanke hukunci akan abunda baka da masaniya Ashe ma Shi taimakone yayi harna rike hakan a Raina nake Masa mummunan zato ke Kuma kinaji Ina zagin yayanki kikayi shiru kikaki fadamun yayankine"Zahra ta fada Tana sauya fuska"Dan murmushi chuchu tayi ta ce "To Taya zance Ni kanwarsa ce a lokacin tsanar da akayi Masa ta shafeni kintuna momcy yanda muke drama Dake a school Akan ki auri yayana Ashe dai tuni ma Yayan yayi wuf Dake nice bansaniba idan natuna abunnan al'ajabi nakeji"Dan murmushi Zahra tayi ce "Ni kaina wani gamin ina jinjina Abun"Ikon Allah ne kawai momcy wlh al'amarin Nan yakara wa'azantar Dani duk abunda yake rabonka ne Kota wace hanya sai Allah ya kawo dalilin samunsa sannan matar mutum kabarinsa Hafiz mutumin nawa ko ana Ina har yanzu mamaki nake fa dalilin da yasa yace yafasa Auren duk irin son Da ya nuna Yana maki"Sai lokacin Zahra ta tuno Hafiz kwantawa tayi tare da lumshe Ido a ranta ta na tunawa da ai Indai hakane soyayya to ba so takeyiwa Hafiz ba kawai dai zata auresa ne a saboda Halaccin da yayi Mata Amma so na so to MD takeyiwashi akanshi tasan meye so,a kanshi tasan zafi da radad'in so,a sanshiba tasan menene kishi ,taba ta din da chuchu tayi ne ya sanyyata bude Ido ta kalleta chuchu ce ta ce "muna Hira Kuma zakiyi bacci"Ba bacci nake ba fa ai nazata waya zakiyi da Habibyn naki"Murmushi chuchu tayi ta ce "Ai mungama na Manta ban fada maki ba kiyi Mana murna an maido Yaya Adil aiki Abuja kinji murnar da nakeji Dan banason Nesa daku wlh dafa ba ayi Masa transfer ba saidai a kaini maidurin Nan da ko da ziyara banason zuwanta wlh zafi da ranar garin tayi yawa ga Hajiya ta addabeka Amma yanzu Kinga gani gaku ga ammy musamman ma ke da Rabin rayuwar Yaya a Abuja yakeyinta Kinga naji dad'ina "Dariya Zahra tayi ta ce "gaskiya nayi murna wlh Nima da kikacemun an Fara maganar tsaida ranarku da naji maiduguri ce saida hankakina ya tashi Amma yanzu alhmdllh Tunda dai muna tare"Wlhko najima Ammy Tana maganar kafin wanna Case din ya bullo wait zamuje maiduguri Dake y'an uwan abbanmu su ganki Wanda Basu ganki ba sannan tace idan zata India Ganin gida ma tare zaku tafi itama Yan uwanta su ganki "wai kina nufin Ammy y'ar India ce kenan shiyasa Naga ita da abban su Zahra Basu Kama da hausawa najima Ina wannan tunanin Ina musu kallon Indiawa Ashe dai da gaske ne kune bakuyo Kama da y'an chan ba keda Aunty zey"Zahra ta fada "Gyada Mata Kai chuchu tayi ta ce "Eh Mu munyi Kamar Abba ne shiyasa"Allasarki "Bari na Miki wata gulma kinsan Yaya Jabir da Asmy sunjone soyayya suke kuwa to ko rannan da kikaga tazo Shi ya kawota ya maida ita Kinga yanda yake tarairaiyarta saboda dakyal ya samu ya shawo kan y'ar rigimar tasa Suna chan Suna zuba love yanzu Haka da Zaki Kira wayarta waya zakiji tanayi"Chuchu ta fada Tana Dariyar shakiyanci "wow Da gaske kike wai "Zahra ta fada "Wlh da gaske Baku zauna kunyi doguwar hira bane shiyasa Bata fada maki ba "Cike da farinciki Zahra ta ce "Alhmdllh Kai Allah na gode maka wlh karkiji irin dadin da naji Kinga Shikenan dukanmu mu ukkun bamuyi nesa da juna ba"Wlhko Nima karkiji yanda nakeji"a wayar chuchu suka Kira Haka ko akayi suka samu Tana ways Saida ta gama takira Sosai Zahra tayi Mata tsiya ta Rama irin yanda ita take Mata sunjima suna hira cike da kewar juna "Asmy ce to ce"Wai kinsan rad'e_Rad"in da nakeji a gari Wai Su Habiba da Salamatu sunyi cikin shege anje a fidda Abun yaki fita karkiga yanda mama rabi ta rame ta jeme Niko nace Allah ya Kara aniyarta ce ta kome Mata abunda taso ya faru Dake ne ya Kare a kan y'ay'anta har Biyun baba ma ya dawo shekaranjiya "dukda musgunawar da mama rabi tayi Mata Amma Zahra sai bataji dadin abunda ya faru ba kasa kasa ta Ce "Allah ya kyauta to ya kiyaye Dan Allah Asmy gobe kije ki amsomun number baba kituroman ta sabon layina da na kiraki ashi last week"Okay Insha Allah gobe na turo maki"Bayani sunyi bankwana sai sannan Zahra ta Ciro wayarta da ta mutu ta jona chaji gado tazo Harta kwanta saikuma ta kalli chuchu Dake chart ta Ce "Su Akhbar suna wajen ammy fa har 11 yanzu karsu hanata bacci"Naje daukarsu dazu ta Ce Wajenta zasu kwana akwai madararsu da abincinsu wajenta"Ajiyar zuciya Zahra ta sauke ta ce "Kice yau na kwanta sai safe"Gaskiyar Kam Ammy ta fansheki"Zahra Harta kwanta chuchu ta daddabata ta Ce "Momcy na Manta wlh gulmar Nan tun dazu take cina Wai da kukaje ana fadin abun Nan ya Amera tayi shegiyar Ashe duk Takama da gadara da take Akan kudi da duniya ita ta tashi cikin arziki kaza_kaza Ashe ma kudin dukiyar Kakanki ce kai gaskiya dai Baban amirar Nan yaji kunya wlh "Girgiza Kai kawai Zahra tayi ta Ce"Allah shiryeki chuchu Daman akan wannan ne har Kika tasheni bacci yaudai naji gulma kikeji nikuma bacci nakeji wlh"Dariya chuchu tayi ta Ce "Kamarko kin sani Allah yau y'an gulmar ne a Kai"washegari Zahra ta Kira baba a layinta bayan Asmy taturo Mata number Sosai suka Sha waya da mahaifin Nata sai Dadi takeji sunjima suna waya kafin suyi bankwana cike da kewar juna a cikin satin Nan aka yankewa Abban Amera hukuncin kiss ta hanyar rataya bisa ga rashin gardama da baiyi a Court ba yasanya shari'ar tasu tayi sauki Sai sannan hankalinta MD ya Fara dawowa jikinshi Koda yaje ya labartawa ammy Sosai taji Dadi Kuma tayi hamdala koba komai Shima zaije ya girbi abunda ya shuka a ranar suka koma gidansu shida Zahra tare da yaransa ranar dai Zahra taga yadan warware Wanda da taimakonta hakan ya faru da girki ta shimfida Masa Mai dadin gaske bayan ta dau gayu Kuma ta faranta Masa a shimfida washegari Zahra na kwance jikin MD kan kujera Tana zuba Masa shagwaba Yana biyeta Yaran ko suna tsakar polourn suna wasa da wutsil wutsiltu wayar MD tayi ringing yayi mamaki Ganin bakuwar number ta kirasa da special numbersa da makusantata ne kadai ke kiransa da ita kin dauka yayi Saida aka sake Kira Zahra ce ta Ce "Ka Dauka Mana Hubby ana kiranka fa"Dan kar Zahra ta zargi wani Abu ya sanyashi dagawa daga Bangaren Maman Amera ta na kuka ta Ce 'Ga Amira Nan mustapha zata mutu ba sunan da take ambata idan ba naka ba ka daure kazo ko bankwanar karshe ce kuyi Dan Allah"a zabure MD ya Mike ya ce "Subhanallah mama Kuna wani asibitin "BIBA HOSPITAL"ta fada Masa "Cikin sauri ya katse wayar ya ce "gani Nan"Mikewa yayi hankalinta tashe binshi Zahra tayi ta ce"Lafiya dai?Da sauki Amira ce ba lfy ki koma zanje na gano"ya fada Yana fita waje ba shiri komawa Zahra tayi ta zauna Tana tagumin kome ya samun amirar saikuma ta Tabe Baki ta koma wajen yaranta ta dinga yi musu wasa kafin ta Kara kimtsa Gidan da turarruka kamshi saikuma ta shiga kitchen Dan Dora sabon girki"Soaai MD hankalinshi ya tashi ganin halin da Amira ke ciki numfashima dakyal takeyi "hankalinsa tashe ya kalli Mamanta ya ce "mama tun yaushe ta Fara ciwon"Tun ranar da tashin hankalin Nan ya faru take kwance Daman dai duk zaman da tayi gida ba lafiya ta fiya ba yanzu dai yau batama gane wadanda ke zuwa da dawowa sunanka kawai take iya fada kafin Dr yayi Mata allurar bacci"innalillahi wa inna ilaihiraji'un"MD ya dinga maimaitawa kafin ya rike hannun Amira Yana kallonta yanda numdashinta ke fits dakyal Sosai yaji tausayinta Ganin irin ramar da tayi Yana rike da hannunta Yana ta kallonta Yanajin rashin kyautawarshi na kin. Waiwayarta Wanda a nashi salon Dan ya hora ta ne su zauna lafiya Shi yasan idan yace baya kaunar amera yayi karya kodan sabon zaman shekara goma ai ba wasa ba saidai kawai yaji a ranshi yafison Zahra fiye da soyayyar da yakeyi Mata a Cikin ranshi duk abunda mahaifinta yayi baijin Zai rabu da ita saboda Laifin mahaifinta daban ko a lahira Nata daban Laifin wani baya shafar wani ita kanta Mamanta tayi mamakin yanda MD bai nuna komai ba duk wani abunda za a bukata Saida MD ya bada kudi koda amira ta farka da sunanshi a bakinta Yana kusa da ita ya ce"Bude idonki ki ganni honey nine mijinki a tare dake "A hankali amera take kallonsa kafin ta Fara hawaye ta garkame hannunsa ta Ce "Ka yafemun honey duk Laifin da nayi maka Dan Allah honey inajin a jikina mutuwa zanyi honey zuciyata ji nake kamar zata fashe ka yafemun Kace ammy da su Hajiya su yafemun da duk Wanda nayiwa laifi.."ta karasa fada Tana hawaye"Sosai hankalinmu MD ya tashi rukota yayi Sosai ya ce"Kidaina fadar irin maganar Nan My Merah bazaki mutu ba Zaki tashi mu cigaba da rayuwar mu muma zafin ciwo ne Dan Allah kidaina fadar Haka Kina tayar mun da hankalinna"Murmushi yake kawai Amera tayi "Mamanta ce ta karaso ta Ce "Ki daina fadar Haka Amira kinsan ke daya Kika ragemun a fadin duniyar Nan ke daya gareni ba uwa ba uba ba miji bazan rasaki ba amera zamu rayu"Hawaye kawai Amera take Tana kallon maman Tata ta Ce "ki yafemun Dan Allah mama"kuka Sosai Mamanta ta ke tace bakiyimun komai ba amera Baki da hakkina a tare Dake inma akwaishi na jima da yafe Miki banason kina kalama. Nan kina tayar mun da hankalin"MD ji yake kamar Shima yayi kukan mikewa yayi yaje wajen Dr din domin chuku_chukun a fidda ita waje cewa Dr yayi ba matsala sai a shirya fitar da ita din zuwa jibi "yinin ranar mD Shi yayi jinyar Amira Yana rungume da ita duk abunda take so Shi yake Bata Daren ranar shine baikoma gida ba Saida yaga ta samu bacci sai wajen karfe Sha biyu ya koma gida Koda yaje bai samu Zahra a parlour ba Yana shiga bedroom Amma ganta kwance ita da Yaran su duka suna bacci Banda ita daya same ta Tana kallon gefe Tana tunannika Wanda Saida yakira sunanta tukwana tasan da zuwanshi kallo daya tayi Masa da har bazata Masa magana ba saidai ta danne kishin da takeji Tunda yayi Daren Nan tasan Yana tare da matarsa ta Ce "Ya Mai jiki"Numfashi yaja kafin ya ce "Da sauki dai za ace Amma waje Zan fitar da ita gaskiya ban yarda da kwarewar asibitin ba Tana Shan jiki Sosai ciwon Nata ya dagamun hankalinta"ya fad'a fuska ba walwalar"Allah ya bada sauki"ta fada Tana juya baya tare da rumtse Ido tanajin kishin amera Sosai a ranta "Tana jinshi ya dauke Yaran ya mayar dasu gadonsu na iri Wanda ake turawa kowanne Mai net dinsu kafin ya kwanta ya janyota jikinsa Zahra Najin haka ta marairaice Cikin shagwaba ta Ce "nasan ka shawo gajiya kanason ka yi bacci please ka kwanta yanzu danka tashi da wuri Abbansu Amar"d'an murmushi MD yayi Yana jinjina hikima da wayewa irin ta Zahra Bata iya cemasa ita ta gajine bazata iya ba shiyasa ta sauya. Maganar cikin hikima baiyi Mata komai ba sai janyota jikinsa da ya karayi ya ce"Mu kwanta....washegari tun asuba MD ya wuce Asibitin ba yanda Zahra batayi dashi ba Akan Yama tsaya yayi breakfast Amma yakiya Bayan fitarsa Tagumi tayi tana Jin yanda zuciyarta ke nukurkusa akan kishi wata zuciyar tace Mata matarsa ce fa tun kafin ya sanki suke tare shekara goma Sha ,Bata da lafiya dole yayi fiye da Haka ma '"Saurin mikewa tayi ta Ce "Au'zubillah"Kafin ta cire duk wani kishi da tasa a ranta ta aje gefe saima.adduar samun lafiya da tayiwa Amira Bayan sun kimtsa Gidan tare da taimakon Yan aikinta Nanny din yaran Suma sun shiryasu kitchen ta shiga tayi girki Mai d'an yawa Bayan ta gama komai ta Sanya a warmers a lokacin 1:pm Cikin sauri tayi Wanka ta shirya Cikin kayanta masu kyau Bayan ta Sanya katuwar hijab dinta irin ta larabawan Nan har kasa wayarta ta dauka tare da Kiran number MD Bayan ya dauka ta Ce "ya sunan asibitin na shirya ne Ina son nazo na duba ta "Ki Dan jira minti biyar ga driver Nan zanturo ,zaizo ya kawoki Asibitin"ya fada a sanyaye"Okay"ba ayi 10 minute ba Saida driver yazo ya dauketa ita da yaranta sai nannynsu daya data rike Mata biyu koda suka isa har dakin da Amira take Sosai Zahra taji wata irin faduwar gaba Ganin yanda MD ya rungumo Amera jikinsa Yana bare Mata ayaba dakyal ta iya control din zuciyarta da take Jin kamar zata rabe gida biyu ta gaishe da maman Amera ta amsa Mata Cikin mutunci Dan ta gane ta tare da tambayar ya Yan Gidan ta ce "Alhmdllh"Dagowa MD yayi ya kalli Zahra dayaga ta Dan sauya zamewa yasoyi tun dazu Amma amera ta garkamesa Yana Jin nauyin mamantama Dake wajen Amma tun safe da yazo taki barinshi tashi a sanyaye Zahra ta kalli Amera Dake Numfashi dakyal ta ce "Ina yini ya jikin"Kallonta Amera take da idanunta da suka Fara sauyawa tsabar wahala ta gyada Mata Kai ta ce "Alhmdllh"Kallon MD amera tayi ta Ce"Ce ta mikomun yaran na gansu"Ta fada Tana hawaye kallon Zahra MD yayi ya ce "Mamy d'an Miko Mata su "Zahra ji tayi kamar ta ce "a a a Dan Bata mance lokacin da Amira taso halaka yaran ba dakyal tayi shahada ta Mike da little Dake haannunta ta nufi gadon Mika hannunta Amira tayi tana daga kwancen ta amshe ta "Zaki iya daukarta kuwa"Kirkirarren murmushi Amira tayi ta ce"Eh Zan iya yau jikin yafi koyaushe mun sauki"Alhmdllh Daman haka nake sonji Insha Allahu Zaki warke gobe ne tafiyar da za ayi Dake Egypt"Girgiza Kai kawai Amira tayi Zahra ji tayi kamar zuciyarta ta fashe juyawa tayi zata koma amera ta ruko Hannunta juyawar da Zahra tayi sai gani tayi tana hawaye ta ce "Dan Allah y'ar uwata ki yafemun duk rin abunda nayi maki ki yafemun banason na tafi da hakkin kowa ina Neman yafiya a gareki Dan girman Allah"zuciyar Zahra Sosai ta karye batasan lokacin data Fara hawaye ba. Ta ce "Ba abunda kikayimun Aunty Amira idanma kinyimun na yafe Miki Nima kiyafemun insha Zaki warke ki tashi kamar kowa"Suna Jin Amira ta sauke ajiyar zuciya har lokacin Bata saki hannun Zahra ba saikuma ta hada Dana MD ta ce "Honey ga Amanarta Yar uwata Nan ka riketa da Amana kamar yanda ka rikeni Amana nasan kaid'in Adalin mutum ne Kayimun halaccin da ba Wanda yayimun a rayuwa MD ka zauna Dani tsakani da Allah ka kyautatamun dukda irin rashin kyautawar da na dinga maka ka kula Dani ka Soni a lokacin da idan wanine xai gujeni Babu abunda zance a zama na dakai saidai godiya Allah ya hada fuskokinmu a aljanna fiddausi Kema Zahra ki rikesa da Amana Karki Bari MD ya kubuce maki samun irinsa a Cikin maza Abu ne Mai wahala Ina tayaki murnar samun miji na kwarai na gari nagartaccen sannan inayi muku murnar samun zuri'ar da kukayi Allah ya Raya su naso Ganin jini na a duniyar nan Ashe banida rabon Zan gani ,Dan Allah Ina Neman alfarmar da idan Kun haifi wata y'ar ku Sanya Mata suna na MD karka Manta Dani ko bayan Raina ka sani Ni amera na mutu ne da soyayyarka a Raina Kuma da ita zantashi Koda ranar gobe kiyayya Ina sonka mijina ina tsananin kaunarka Kuma Ina alfahari dakai Allah ya hadamu a darussalam"Kuka ne yaci