Showing 99001 words to 102000 words out of 153980 words
tayi alwala akan lallausan carpet din d'akin tayi salla jingina tayi da Gado tana rusa sabon kuka mai tab'a zuciya MD koda ya shiga ya ganta cikin wannan halin sosai ta daga masa hankali "Cikin tausassar murya Wanda kana jinta kasan Shima a tashin hankali yake ya ce " Dan girman Allah Mamy ina begging d'inki Dan Allah kiyi hakuri ki nutsu karki sanya kanki cikin wani hali ki sanya yaron dake cikinki "D'ago da idanunta da sukayi ja tayi tare da banka masa wata irin harara ta ce " kai har kana da bakin da zakayi mun magana akan Abunda ya shafi rayuwata wani hali kuma zanshiga Wanda yafi Wanda ka sanyani cikinsa Sannan cikin da kake magana kama daina sashi a lissafi Dan wlh kaji na rantse bazan haifesa ba bazan haihu da mutumin da ya ruguzamun farincikin rayuwataba bazan haihu da mutumin da yayi sanadiyar shigar mahaifina cikin wani hali ba ka cuce ni ka zalunceni......"kuka ne yaci karfinta ta kasa fad'ar abunda tayi niyyar fad'a rumtse idonsa MD yayi yanajin zuciyarsa na wani irin zafi da rad'ad'in maganganun nata a fahimtar sa kenan dalilin bayyanuwar cikin nan ya sanya mahaifinta shiga wani hali Tabbas dole ne yayi bincike sosai yakejin zafi idan tace zata zubar masa da ciki "Shiru yayi na d'an lokacin yana sauraran kukan nata da yake jinshi kamar ana d'iga masa darmar wuta kafarsa ya Kalla da tayi kumburi ga rad'ad'i da take na yankan glass din da ya shige masa danma kwalbar ta fita amma wannan bai dameshi ba hankalinshi yana kan yanda zai samu ta fahimcesa sosai MD ya shiga yi mata magiya da ban hakuri akan ta nutsu suyi magana amma takiya sai kuka da take tana ja masa Allah ya isa 'Ganin ta tsagaita kukan ne ya sanyashi cewa" Dan soyayyarki da fiyayyen halitta Annabi muhammad (s a w ) Wanda akayi duniya dominsa mukecin darajarsa kiyi hakuri ki nutsu muyi magana na had'aki da girman Allah da manzon sa Mamy badan ni ba girman da darajar Wanda na had'aki dasu zaki duba "Shi kanshi MD baisan ya iya magiya haka ba Dan baitabayi ba baitab'a rokon wani Abu ba a wajen wani tunda yake idan ba a gurin mahaliccinsa ba Amma yau shine yake magiya yana rokon yarinya k'arama tana batsewa gaba d'aya ta since masa notin kansa " Zahra batayi niyyar sauraransa ba Amma darajar Wanda ya had'ata dasu yasanyata tsagaita kukan ta d'ago kanta daga hade kai da gwuiwar da tayi tana Goge hawayen ta kauda kai Alamun tana sauraronsa "Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce " Me kikeso kike da Buk'ata da zakibar kukan nan Banason ganinki cikin halin nan ki fad'amun me.kikeso"cikin muryarta data fara dishshewa ta ce "Abunda nake so mai sauki ne na farko ka sakeni ka fita daga rayuwata har abada ko a hanya ka ganni.karka nuna ka tab'a sanin mai suna na ma ka rabu dani Na har abada na biyu Kuma ka kaini a zubar mun da Cikin nan...ta k'arasa fad'a cikin kuka" Tirk'ashi ai abunda ta lissafo MD baijin zai iya d'aya daga cikinsu musamman cikin d'aya kwallafa ransa a kanshi"fuskarsa ba walwala ya ce"ki daina maganar zubar da cikin nan Mamy ina son kaya na Ina kaunarsa Fiye da komai nawa da na mallaka ki taimakeni ki haifamun shi please Dan girman Allah "wani irin kallo na baka da hankali zahra ta bishi kafin ta ce " ohhhh wai a tunaninka ni zahra zan Haifa maka cikin nan to tun wuri Inma mafarki kake ka maza ka farka Dan wallahi tallahi kaji na rantse bazan haifi cikin nan ba ko ka kaini a zubar mun dashi ko kuma wlh na zubar dashi ta karfi da yaji"dafe kansa MD yayi dake matuk'ar sara masa yanajin wani irin daci idan yaji tace zata zubar masa da ciki "cikin dauriya da k'arfin hali Dan kansa wani irin ciwo yake masa ga tension ga kwanan zaune da yayi ya ce " Na shirya mallaka maki komai nawa dana mallaka kudi,kadara,componynnika na ,gidajena nako ina wallahi tallahi kinji na rantse na shirya sadaukarwa miki da komai nawa hatta gidajena bazan bar kaina da komai ba indai kin yarda zaki Haifa mun cikin nan wlh a shirye nake da baki Duka dukiya ta akan cikinnan yafiye mun komai Dana mallaka Abunda najima ina burin samune tsawon rayuwata shine yanzu na samu Mamy ki dubi girman Allah karki zubar mun da ciki a shirye nake da mallaka maki dukkan abubuwan nan Dana lissafa maki madamar zaki Haifa mun cikinnan saboda ina masa tsananin soyayyar da bantaba yiwa wani mahaluki irinta ba ,"wani banzan Kallon zahra take binsa dashi na tsana kafin ta ce"a tunaninka dukiya ita zata iya baka komai,a tunannika duk wannan abubuwan daka lissafo zanyi kwadayinsu ne yasa harnaji ina sha'awarsu na Haifa maka cikin nan to tun wuri ka sauya tunani k'aramar kwakwalwarka ta fad'a maka da daidai ba Ina son ka sani ba komai kudi ke iya saya ba ,baka da kud'in da zaka sayeni dasu ,Kai har kana da kud'in da zaka saye ni dasu to idan baka sani ba ka sani ni zahra bana sha'awar dukiyarka,bana kaunarta,kuma babu abunda zanyi da ita ,bakada kudin da zaka ribe ni da su wlh ,baka da wannan ikon koda kudinka Sunkai tundaga sama har k'asa "ta k'arasa fad'a tanajin wani irin dacin takaici a cikin zuciyarta " Sosai MD yayi mamakin yanda yarinyar ke fad'a masa magana son ranta kwata kwata gani yake ta sauya kamar ba zahrar da ya sani bace a baya mai saukin kai da saurin Sauka ,rasa ma abunda zaice mata yayi sai kallo d'aya dinga binta dashi Mikewa yayi batare da ya sake kallonta ba yayi palourn Yajima yana sake sake a ransa Ya zaiyi da rayuwarsa ne Wai "tunowa da bata ci komai ba ya sanyashi saurin zabura Tare da mik'ewa yafita compound din gidan ma'aikatan dake gadin gidan ya kira Tare da umartarsu su da suyo masa take away na abinci kala biyar " kafin ya juya Dan a cikin biyar d'in ta zab'a Wanda takeso yana palourn har aka kawo abincin A plate ya juye d'aya Bayan daya kafin ya d'auka ya fara d'aukar biyu yayi bedroom d'inta dashi yanda tabarya haka ya sameta ta hade kai da gwuiwa tana kuka shi yanzu baimasan da wasu kalamai zaiyi amfani wajen Lallashinta ba "zaunawa yayi tare da Aje Plate din Abincin Duka biyun a sanyaye ya ce " Ki taso kiyi break fast "Zahra kamar jira take tana gadowa ta kalli abincin da Kallesa D'aukar plate din Duka biyun tayi tare da watsa masa tundaga saman rigasa har kasa ga zafin abincim" MD baitab'a expecting haka daga Wajenta ba Kallon kanshi yayi da kalleta tare da Kallon abincin data bata masa kaya dasu Miyar soyayyan dankalin dukta bata masa farar shadda "Baice mata uffan ba sai barin dakin da yayi tare da komawa Bedroom dinsa shi kanshi yayi mamakin da bai iya cemata komai ba Yasan dai duk duniya Bayan Ammy babu wacce ta isa tayi masa haka a duk fadin duniyar nan ya rabu da ita shi kanshi har mamakin kanshi akan yarinyar yanda harta iya d'aga baki ta dinga gaya masa maganganu son ranta saida ya sake wanka ya sauya wasu kayan kafin ya fito hankalinshi gaba d'aya yana kanta bataci komai ba wani Abu zai iya affecting cikin dake jikin ta " amma yasan ko yaje da wani abincin bazata sauraresa ba "Wayarsa ya janyo tare da dannawa jaber kira Jabir yanajin muryarsa yasan cikin damuwa ya ce " Yadai bloody meke faruwa?Numfashi yaja kafin ya ce "Jabir ina son kayi mani wani taimako? Inaji Jabir ya fad'a daga wayar" Akwai mahaifin yarinyar nan da nake tunanin bashi da lafiya ina son ka binciki Chuchu ta fad'a maka asibitin da yake duk wani taimako daya kamata da ni zanyi kayisa kome ake ciki ka kirani sannan a sauya masa Asibiti duk yanda likitocin sukace idanma waje ta kama a fitar dashi kome kenan na bar maka ragamar kula dashi a hannunka"daga bangaren jabir ya ce "Insha Allahu baka da matsala Aboki amma Bazan tambayi Chuchu ba saboda kartai zargin wani Abu tunani na general hospital d'innan da na gansu a nan ne asibitin da yake yanzu zanje garin na bincika tunda nasan gidansu kaga komai mai sauki ne karka samu damuwa" numfashi MD yaja yanajin yarage y'ar Kad'an daga cikin abunda ke damunsa ya ce "sainajika idan ansamu yanda akeso ka kirani" yinin ranar ba abunda zahra taci a cikinta dukda irin yunwar da takeji har juya ke daukarta amma batajin zata iya cin abunda ya fito daga hannun mutumin nan da takejin tsanarsa a ranta bangaren MD ma hankalinsa tashe yake bai iya sanya komai a cikinsa ba sai fresh milk yinin ranar daga ita harshi Cikin tashin hankali Suka yishi Dan sosai ta d'agawa MD hankali washegari ma haka zahra harta fara fita daga hayyacinta da komai bibbiyu take ganinsa kwana biyu kenan ba abinci cikinta sai ruwa da Takesha yanzu babu abunda take da muradin sama da tasamu hanyar da zata zubar da kadararren cikin nan Kallon cikin tayi Wanda da a haukanta kiba ce ta fara taga harya so ya fara fitowa batasan lokacin da ta fara bugun cikinta da hannu bibbiyu ba iya karfinta sosai take bugun cikin dukda azabar zafin da takeji tana cikin Bugawa taji wata irin azaba batasan lokacin data k'walla wani uban k'ara ba Wanda daga nan bata Kara sanin Inda kanta yake ba ta zube a wajen summammiya MD daga palour ya jiyo Karan da tayi ba shiri ya Ruga d'akin yanda ya sameta ne ya yi tsananin tayar masa da hankali kwance k'asar tiles ga jini da ya ga ya fara fitowa daga kasanta a matuk'ar tashin hankali ya nufi Inda take tare da Fara jijjigata yana kiran sunanta shiru Ba shiri ya sungumeta a guje yayi waje da ita makullin motarsa dake kan centre table ya d'auka cikin tashin hankali yayi waje yana bud'e motar ya sanyata a baya tare da Juyawa gidan Gaba a 360 ya figi motar tare da dannawa mai gadi wani Mahaukacin horn kafin ya isa da motar get dinma an wangale masa gudu yake sosai Cikin tashin hankali yana driving yana waigawa yana kallonta ikon Allah ne kawai ya kaisa Asibiti....✍🏾
*Domin magana da marubuciyar 07026166536*
*GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯♀️👎👇👇*
1, *MU GANI A ƘASA...*🔥
_Ummu Affan_
2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚
_Ummu Maher_
3, *GUNTUN GORO..*💥
_Mom Islam_
4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎
_Mrs Bukhari_
5, *AUREN WATA TARA*👩❤️👨
_Miss Hajo_
Guda biyar 1k
Guda huɗu N700
Guda uku N600
Guda biyu N500
Guda ɗaya N300
*DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇
0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank.
Domin tura shaidar biya👇
0810 433 5144
Masu tura katin MTN👇
0814 179 9224
Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇
0817 952 3215
Guda biyar 1000f
Guda huɗu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ɗaya 300f
*TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩❤️👨
_*Miss hajo ce*_🤙🏿
[10/3, 7:17 PM] Mother Mamy: 🅿️...........*73 & 74*
Kin cucemu Zarah kin b'ata yardar da mukayi miki"ta k'arasa fad'a hawayen bak'inciki na sauka daga idonta Dan Duk cikin Yayan y'an uwanta ba Wanda tafiso kamar Zahra"Kuka Zahra take kamar ranta zai fita tama kasa magana Baba ne da hankalinshi yayi mugun tashi yana dafe da saitin zuciyarsa ya ce "me yake faruwa Habiba kiyimun bayani me zahrar tayi " Cike da takaici ta Kalleshi ta ce "Saidai kayi hakuri Malam abunda na kiyayar ne Ya faru Yaron nan yaudararta ya yi yayi mata ciki shiyasa yazo lokaci guda yace ya fasa" A matuk'ar tashin hankali Baba ya furta "Ci ki" a rarrabe "Mama Zainabu ce " Cikin b'acin rai Ta ce "Meye haka kike Habiba wai kasancewar itace gaba da ita ta ce " wannan Abun da kika fada kai tsaye ai sai kija kuma zuciyarsa ta tarwatse shida daman ba kosashshiyar lafiya ba tun mutuwar mahaifiyarta ba lafiyar kirki ta ishesa ba "To idan ban fad'a masa ba an nemu mafita shiru zanyi dole yayi hakuri muzo mu nemu mafita tunda Mai faruwa ta Riga ta faru Wlh Zarah kin kunyatamu bantaba tunanin haka daga gareki ba " Kasa magana Baba yayi sai Dafe saitin zuciyarsa da yayi cikin k'arfin hali ya ce "Habiba Nasan halin Zahra sarai na san irin tarbiyar da na yi mata ba zata aikata wannan Abun ba kodai likitan ya gwada ba daidai ba kafin ya kalli zahra data durkushe kasan kujera tana kuka ya ce " Zahra taso ki fad'a mana Ba Gaskiya bane bazakiyimun haka ba nafi kowa sanin halinki da irin tarbiyark...kasa k'arasa maganar yayi sakamakon wani irin daci da yake ji a a makogaransa na tashin hankali "Cikin muryar kuka zahra ta d'ago ta ce " Ba Ba "Saikuma kuka yaci karfinta " Cikin b'acin rai Mama Habi ta nufi Inda take ta ce "Fad'a mana ubanda yayi miki wannan abun" Kasa Dagowa tayi saici gaba da kukan da tayi tana tsinewa Musty a ranta ta ce "Ka cuce ni ,ka zalince ni,ka tozartani ,ka sanya mutanen da suka yarda dani yanzu bazasu tab'a aminta dani ba ,bani da bakin da zan k'are kaina Allah ya isa tsakani na dakai" cikin Zafin rai Mama Habi ta nufi Inda take tare da shakota ta ce "Zaki fad'a mana ubanda yayi miki ko saina illataki yau d'innan" dukda zahra taji shak'ar sosai kasa magana tayi sai kuka"Kasancewar D'akin tsakar gidan yake gashi da karfi suke magana ya sanya mutanen dake tsakar gidan suka Fahimci halin da ake ciki kowa Salati kawai yake Asmy ko tashin hankalin data shiga baya musaltuwa har Chuchu da taji abun tamkar almara saida tayi kuka ta ce "Asmy ban yarda ba Momcy zata aikata haka Dan Allah kije kiyi musu bayani kila Dr dinne ya rubuta ba daidai ba " tagumi Asmy tayi hawaye na sauka daga idanunsu Cikin tsananin b'acin rai Mama Habi ta ce "Magana ta ta tabbata amma yaron nan anyi Dan iska ba kama ,ya cucemu aiko wlh bai isa ba yanzunnan bazan zarce ko ina ba sai gidan uwarsa da ubansa suji abunda dansu yayi yasa ya ce ya fasa Auren ta fad'a tana yin hanyar waje kamar wacce aka tsunkula haka Zarah ta zabura tare da saurin Kamo K'afar Mama Habi " mama Ba shi ba ne "Ta fad'a a rarrabe duk juyowa sukayi suka Kalleta yanda ta rik'e kafarta tana wani irin kuka mai cin rai sai sannan Mama Rabi da shigo d'akin Bayan ta gama shewarta da hamdala a d'aki d'auke ta da Mari Mama Habi tayi ta ce " To Dan Ubanki idan ba shi ba uban wa yayi miki ko fyad'e aka miki"Nan ma shiru Zarah tayi saici gaba da kuka da take "Daidai lokacin da Baba ya fara tari dukansu cikin tashin hankali Suka nufi Inda yake sosai ya shiga tari ba kakkautawa yana dafe da saitin zuciyarsa" Salati duk mutane suka fara "Mama Rabi ta ce " Shikenan kin kashe sa kin kashemun miji bakincikin ki ya kashe ubanki Munafuka duk sanya hijab din da zarya Islamiya ba fashi Ashe na banza ne na kariyar iskanci ne ni daman Nasan An Rina jami'ar nan da ta tafi nasan da bura'ubar da take yo yarinya ce Daga shiga Jami,'a ta waye tana ganin kowa a daddage sai wani kyau da take Da kiba kamar ba karatu take ba Ai yanzu ga ranar tonuwan asirinki nan muna fuka algulguma "Kannen Baba sunajin abunda Mama Rabi take cewa Amma hankalinsu yana ga Dan uwansu dake tari hankali tashe sai sannan zahra ta lura da Baba da gudu taje Inda yake tare da Rungumesa da fashe da wani irin kuka ta ce " Dan Allah Baba karka tafi ka barni kai kad'ai ka ragemun a duniyar nan kai kad'ai ne mai sona kuma nasan kai kad'ai zaka fahimceni Dan Allah Baba karka mutu kodan ni ka tausaya mun "Mama Rabi Ce cikin zafin nama Ta fardo ta dagaa kan Baba ta ce " Dan Ubanki k'arasa kashe shine zakiyi y'ar iska karuwa cike da muganci ta hau Bugunta Karan da Zarah tayi ne ya sanya su Asmy da chuchu dake daki Sauri fitowa ba shiri suka shiga d'akin ganin irin dukan da Mama Rabi ke mata ya sanya suka isa wurin da Sauri tare da fardar Zarah Cikin b'acin rai asmy ta ce "Ke kuma ina ruwanki da ita Munafuka har zakiyi mata irin wannan Dukan Muguwa" Nuna kanta Mama Rabi tayi ta ce "Dan Ubanki ni kike fad'awa haka ohhh kungama yawon iskancinku tare shine Asirin d'aya ya tonu zaki Fara borin kunya to saura ke " Cikin Tsawa Chuchu ta ce "Shut up Malama Annabi MUHAMMAD (s a w) ya ce falyakul khairan auli yasmut " ka fad'i alkhairi ko kayi shiru amma daga ganinki bakinki baya fadar alkhairi wannan dukan da kika hauta dashi kasheta zakiyi Dan muganci "Salati Mama Rabi tayi ta ce " watau tsabagen yanda zahra keyi dani har kawayenta ta sanya zasu Zage ni lallai Ta haihu duk ruk'on da nayi mata tun yarinta"Mama Habi ce Dake kokarin tada Baba a kaishi Asibiti ta juyo ta ce "Da Allah Malama fita kiba mutane waje waya sakoki ma d'akin nan muna ta lafiyar Dan uwanmu kin zauna kina wasu banzayen maganganu marar tushe da ma ana ke in kina da kunya har kince kin Riki zahra wlh idan baki bar d'akin nan ba zanyi miki rashin mutuncin da bakiyi zato ba " Tsaki Mama Rabi taja kasa kasa ta ce '"yo ina zani mijina na wani hali yanda yake Dan uwanku nima haka yake mijina kuma uban y'ay'a na Dan haka ba Inda zani kuma ta kashe mun miji kotu Ce zata rabamu da ita "Ohhh haka kike ce kenan to bari nazo mu fidda Raini " Mama Habi ta fad'a tana tunkarar Inda take cikin Sauri Mama Rabi tabar d'akin tana tsine mata kasa kasa "tsaki taja