Showing 84001 words to 87000 words out of 153980 words
zuba daga idanunta "Naji ba ciki jikinki Zarah akwai matsala fa Auren nan na gabatowa na fara tunanin kawai mu fito mu fad'a Gaskiya bazai tab'a yiwa muna sane a daura Aure kan Aure ba" a matuk'ar firgice Zarah ta ce "Me kike nufi?ina nufin mu fuskanci su mama da maganar nan" wani banzan kallo na baki da hankali Zarah tayiwa Asmy tace "bantaba sanin baki da hankali ba sai yau taya kike tunanin zamu fuskanci iyayenmu da wannan Maganar hauka muke ,Sannan ya kike tunanin Baba zaiji Lamarin nan Duk wata yarda da Amincewa Baba ya Riga ya bani ya yarda dani 100% da wani ido zamu Kalleshi mu fad'a masa wannan Maganar cewa zanyi na Aurar da kaina kome ai bani da idon dazan iya Kallon Baba na fada masa wannan maganar" kuka ne ya kubce mata Inda ta had'a kai ta gwuiwa ta shiga rerewa gwanin ban tausayi....
Shiru jaber yayi kamar bazai magana ba saikuma ya Ce " A Gaskiya da nace Babu ruwana a sabgarnan bloody Saboda Gaskiya ba k'aramun b'atamun rai kayi ba last time anma ya wuce yanzu me.kake so ayi wannan hukuncin daka yanke nayiwa iyayen ka k'aryar Amera Nada ciki mai bullewa ce kuwa?Nima bansani ba Jaber na zab'i nayi hakan ne kawai saboda ragewa kaina damuwa ina cikin damuwar da bakowa zai fahimci yanda nakeji ba a cikin raina jaber kome nema yake ya jagulemun taya zan nemo yarinyar Chan ina tsananin buk'atarta a halin yanzu"Kaika bata komai tun farko MD me yasa baka sake ta ba tun farko data bukaci hakan da ka saketa da komai yazo da sauki sai mu samu wata manufar amma kin sakin nata da kayi k'alubale ne babba ta bangarenta ka cuceta sannan ta bangarenka kuma bangane abunda kake nufi nakin sakinta ba Yanzu haka Inaji ina gani saboda kai sai blocking din Asma'u nayi Bayan son yarinyar nake Har cikin raina ni kaina ka jazanun matsala wlh"duk yanda MD yake cikin damuwa Kuma yake neman shawarar jaber bai hanashi Jan tsaki ba ya ce "Mu koma magana me mahimmanci meye mafita kasan dai dakai aka k'ulla abunnan to dakai ya kamata a samu mafitar warware matsala" Ajiyar zuciya mai nauyi jaber ya sauke ya ce "Babu mafitar da ya wuce ka saketa" Bazan iya sakin ta ba"Ya fad'a kai tsaye "mamaki d'auke da fuskar Jaber ya ce " saboda me "Saboda ina tausayinta" Murmushi jaber yayi ya ce "Bloody kodai son yarinyar nan ka fara bamu sani ba " Tsaki MD yaja ya ce "kana da matsala Jaber nafada maka ina tausayin yarinyar ne ,na zalince ta farkon Haduwarmu ,sannan na zalince ta a karshen rabuwarmu dole ne na gyara mu'amula ta da ita karta rikeni a zuciyarta babu abunda nake bakin ciki a rayuwa kamar na mutu Da hakkin wani dole ne na nemi yarinyar nan Duk Inda take " numfashi jaber yaja yana ayyana yanayin abokin nasa Har wata rama yayi cewa yayi"Kasan garinsu ne"a a a "Tirk'ashi aiki ja" jaber ya fad'a kafin yace "To me zai hana na kira Asma'u a waya nasan zata d'auka saimu basu hakuri ka saketa ta Cikin wayar Inajin hakan zaifi sauki " wani irin kallo MD yayiwa jaber ya ce "so kake ayi ta maimaita maka magana d'aya To bazan sake ta ba " Ikon Allah to idan baka zaketa ba Me zaka mata ka saketa tayi Aurenta wannan shine adalci"tsaki MD yaja yana maida Kallonshi ga kofa ya rasa abunda yake masa dadi shiru Jabir yayi kafin ya d'ago ya ce "Muyi serious magana Dan Allah saboda me bazaka sake yarinyar nan ba kowa ya huta?Saboda ina zargin cikina a jikinta"ya basa amsa kai tsaye " wara idanu sosai jaber yayi ya ce "what ciki Kuma?Of course ciki?ya akayi kasan tana da ciki?Jabir ya tambayesa" Naga alamominsa ne tattare da ita a takaice yabawa jaber labarin sauyin daya dinga gani a Wajenta har aman da tayi"shiru Jabir yayi sosai ya Lula duniyar tunani kafin ya d'ago ya ce "Ana wata ga wata" Tabbas indai hakane akwai k'amshin Gaskiya to amma tun kafin ta tafi meyasa kak'i kaita Asibiti aka gwadata"naso hakan takiya nikuma banason in takurata hakan yasa na rabu da ita"Tabbas indai hakane ya zama.dole mu nemu garinsu sannan ya zama tilas a dakile Bikinta da nake tunanin ana gab dayi"a matuk'ar zabure MD yace "kana tunanin bikin ya kusa ne " Bama tunani bane confirm Bikinta yana kusa saboda bazan manta lokacin da muke waya da Asmy takan Cemun Bayan gama makarantar su bazai wuce da wata d'aya bikin Zarah ba "Sosai MD ya shiga sabon tashin hankalin da yafi Wanda yake ciki a matuk'ar firgice ya ce " Impossible bazaiyu ba wlh"Mikewa yayi kamar zai tashi sama tare da shiga d'akinshi yabar jaber a palour girgiza kai kawai jaber yayi ya Mike tare da fita daga gidan yana tunanin Yanayin abokin nasa Tabbas indai ba idonsa ne yayi masa karya ba kishi ne yake gani k'arara a idonsa a zuciyarsa ya ce "Ina zargin MD ya fara son yarinyar nan " amma Indai haka ne sonta MD yake Nayi al'ajabi babba Mutumin da bai tab'a fad'awa tarkon son mace ba Har y'ar president ta sosa bai amince mata ba manyan mata masu ji da kudi gayu,mulki,sarauta,y'ay'an manya masu fad'a aji a k'asar ,suna sonsa yana Disgasu amma lokaci guda ya fad'a soyayyar k'aramar yarinya kamar Zarah da ko fari na azo a gani bata dashi"saikuma wata zuciyar ta ce "Amma kuma ba mamaki saboda yarinyar tana da komai daza aso ta tana da sihirtaccen kyau Tako ina tacika ta had'u dukda ba fara bace sosai amma ta ninka wasu fararen kyau nesa ba kusa ba Tana da kyau ,sosai jaber ya dinga sake_sake a ransa ya saka wancen ya since wancen.....MD yana kwance Sosai yake jin wani irin zafi a cikin zuciyarsa rumtse idonsa yayi sosai da sukayi ja tsabar bacin rai " Tabbas dole na nemo ki duk Inda kike Mamy"ya fad'a a fili Wayarsace tayi ringing ganin Ammy ce ya sanyasa d'auka daga bangaren "Ammy ta ce " Kana ina Baba na wai kwana biyu rabonka da gida Tundaga ranar da akace Matarka Nada ciki baka Kara zuwa gidan nan ba me hakan ke nufi meke damunka wai watanninan na kasa gane maka kaida ya kamata kayi murna da farinciki kyautar da Allah yayi maka lokacin da bamuyi tsammani ba Amma kwata-kwata ka watsar Kamarma baka farinciki da samun cikin Amera "ba haka bane Ammy akwai Uzurrrukan da sukamun yawa ne a harkar kasuwanci na shiyasama amma kiyi hakuri anjima ina zuwa" hmmm harda uzurin dazai hanaka nuna farincikin babbar kyautar nan da Allah yayi maka"Numfashi ya fesar ya ce "Ba haka bane Ammy ina cikin tsananin farinciki da hakan kune bazaku kula da hakan ba " Hmm to Allah ya kyauta saikazo"to"Ammy ya fad'a Bayan gama wayar sosai ya Lula duniyar tunanin Zarah "ina take?ya tambayi kansa".
Kwance take ta d'ora kanta saman cinyar Asmy Kallo d'aya zakayi mata kasan hankalinta a matuk'ar tashe yake Kahirat ce ta shigo gidan ta ce " Aunty Zarah Mama Habi(kanwar babanta)sunzo tace a kira mata ke ?Okay jira mu tafi tare "Zarah ta fad'a tana yunkurawa ta mik'e saboda bataji dad'i dauriya ce kawai take Kallon Asmy tayi ta ce " Natafi ba lalle na dawo ba gobe idan na samu lokaci na shigo"Gyada mata kai Asmy tayi da ita tamafi Zarah rama saboda ita kadai tasan yanda takeji ji take inama kome ya dawo baya ,ta gyara kuskuren data aikata ganin irin yanda Asmy ta tayar da hankalinta ya sanya Zarah ta manta da komai na itace silar shigarta wannan halin ta dauki hakan a matsayin kaddara da kuma wauta da k'uruciya sosai ita kanta take Danasanin sake ma mugun mutumin nan jiki da tayi Wanda a yanzu ba Wanda ta tsana takejin Haushi sama dashi koda suka isa gidansu Sosai ta iske y'an uwan babanta Na Batsari da Wanda suke Aure a wasu garuruwan duk sunzo kasancewar Baban Zarah yana da yayyu da kanne maza da mata sosai Cikin ladabi da jin kunya Zarah ta gaishe su a sanyaye "Mama Habi ta kamota ta ce " me yake damunki Zarah jibi yanda kika zama kallo d'aya nayi maki nasan bakya cikin kwanciyar hankali me yake damunki?Murmushi Zarah ta kirkira ta ce "Bakomai Mama " Hmmm kodai har yanzu Muguwar Matar nan tana musguna miki "Girgiza kai Zarah tayi ta ce Bakomai Mama " Hmmm ai duk mai hankali yasan ba cikin kwanciyar hankali kike ba Zarah tun farko laifin malam ne tun Bayan mutuwar mahaifiyar Yarinyar nan babu yanda banyi da shi ba akan ya bani ita na tafi da ita katsina mijina ba k'i ba zaiyi amma yak'i ya nuna shi yakeson ya Riki y'arsa baya son zamanta wajen kowa hakan yasa muka hakura muna sane da duk gallazawar da akewa yarinyar nan kawai in banda kar kayi magana ne ace ka fiya fad'a Shikenan yanzu dai komai yazo karshe tunda har Allah ya kawo lokaci zakiyi Aurenki ki huta yanzu fad'amun abubuwan da kike so "k'asa tayi da kanta muryarta na y'ar kakkarwa ta ce " bakomai Mama"ke d'ago ki kalleni nidin kamar uwa nake wajenki karkiji kunya ki fad'amun abunda kike so da choice d'inki na kayan d'akin"kamar zatayi kuka ta ce "Bakomai Mama" Ikon Allah to tashi kije"kamar jira take ta mik'e ta shiga D'akin wasu daga cikin y'an uwa sukayi Dariya sukace "Zarah kenan itadai ba ruwanta har yanzu kunya ce fa takeji" Mama Rabi ko tana d'aki ta cika tayi Fam jin Abunda Mama habi take cewa Daman Chan tasan ba wani jituwa suke ba Habiba ce dake gefe ta ce "Ni Mama wlh mamaki kike ban Wai me kike nufi da barin ayi Auren nan da zakiyi nidai wlh harga Allah ina bak'inciki da Hafiz d'innan da Zarah zata Aure Dan Babban gida ne babansa yana d'aya daga cikin manyan masu kud'in garin nan haba Mama taya za ayi yarinyar da Mukasan yarintarta da komai muka bata shekaru nesa ba kusa ba ace wai tazo ta rigamu Aure muna nan zaune ko gaisuwa babu Wanda yataba zuwa sannan kuma ace tayi Aure Inda zata huta haba Haba Mama ina tuno wannan bakin cikin ji nake kamar na hadiyi Zuciya" da hannu Mama Rabi tayi mata nuni tayi kasa kasa cikin k'asa da murya ta ce "A tunaninki haka zan zuba ido ayi Auren nan ina nan ina ganinku wacce ta tsonemun ido ta rigaku Aure Aurenma kuma gidan Hutu ai abunda bazaiyu bane kusa ido Kuyi kallo wasa na gaba Dole zan saki jiki ayi komai dani saboda idan Abu ya lalace kar a zarge ni kina gani dangin Malam ba wani kaunata suke ba so suke ayi tashin hankali Wanda ni ban shiryawa haka ba ... Zarah ko tana shiga daki ta zunduma duniyar tunani gani take abun kamar mafarki Bikinta da Hafiz Wanda inbanda wannan K'addarar ta afka da ba Wanda zai kaita farinciki amma Kuma yanzu Shine take fargabar Auren to wai yanzu haka zata zuba ido A daura mata Aure kan Aure batasan sanda wasu hawaye masu d'umi suka shiga zubo mata ba Cikin muryar kuka ta ce " Ya Allah ka kawomun mafita a cikin al'amarin nan kafi kowa sanin halin da nake ciki Kaine mai iko akan komai babu abunda ya gagari ikonka ya Allah Kakawo mafita ta yanda ban tsammaceta ba Allah na tuba Ka yafemun Ka cireni cikin kangin rayuwar nan nasan wannan din duk yana cikin jarabawa ta ne ya Allah ka sassautamun jarabowowin nan da suke bibiyata tun yarinta ka kuma bani ikon cinye su kuka ne yaci karfinta Sosai tashiga rera kuka Daren ranar Zarah raba dare tayi tana addu'ar Allah ya kawo mata mafita a cikin rayuwarta..... a halin yanzu y'an uwa da dangi na nesa da na kusa duk sunzo domin ayi kome dasu Maman Asmy ma sosai take taka muhimmiyar rawa a bikin nan da za ayi dangin Baban Zarah sai Godiya suke mata na jajircewa da tayi tamkar bikin y'arta za ayi Dan wani irin tsumi takeyiwa Zarah dukda kwana biyun nan ba lafiya gareta ba yauma da Hafiz yazo da dare dak'yal ta samu ta fita cike da damuwa ya ce "Wai Dan Allah me yake damunki ne my Zarah bana gane maki kwannanfa" Kasa tayi da kanta tana maida hawayen da suka zubo mata Dan karya gani kasancewar duhu ne cikin rawar murya ta ce "Bakomai kawai banajin dadi ne" subhanalla ankaiki asibitine"eh Maleria ce" ta basa amsa Dan karya ce saitaje asibiti Ajiyar zuciya ya sauke ya ce "Allah ya baki lfy please kidinga shan magani sosai yanda zaki warke da wuri saida biki ya matso Maleria zatayi mana cikas " Shiru tayi batace komai ba "Kamo hannunta yayi abunda bai tab'ayi ba cikin firgici ta d'ago ta Kallesa Duka hannun nata biyu ya rik'e yana kallonsu tare da murzawa cikin Sauri tayi saurin kwace hannunta ta kauda kai tana hade rai" Sai sannan Hafiz ya dawo cikin hayyacinshi ganin yanda ta had'e rai dukda duhu ne ya ce "Sorry" a sanyaye ta ce "Dare nayi" Okay Good Night dinkunan nan dai sunyi kyau ko?Gyada masa kai tayi dukda ko kallon d'inkin batayi ba saboda yanzu bata wannan take ba "Ajiyar zuciya ya sauke ya ce " Duk abunda kuke da buk'ata keda kawayenku kuyimun waya "Insha Allah " ta fada a sanyaye Bayan sunyi bankwana ta koma gida Nanma saida ta kafa sana'ar tata ta kuka tana jin bata kyautawa Hafiz ba a halin yanzu Zarah bata da wata mafita data wuce Ta Allah Shi kawai take jira yayi ikonsa akan Abun tasan ko giyar wake Tasha bata isa ta tunkari wani da wannan Maganar bare yanzu da biki ya rage saura kwana shida....
"Ammy ba haka bane kiyi hakuri Dan Allah"ya fad'a cikin ladabi"Bani ya kamata kaba hakuri ba Matarka da kayiwa laifi ita ya kamata kaba hakuri"laifi kuma Ammy to me nayi mata "Ohh tambaya ta ma kake me kayi mata Bayan banzatar da ita da kayi Tunda akace tana da ciki baka Kuma waiwayarta ba " Ba haka bane Ammy kumin uzuri please yanzu ina amerar take "Ta tafi Gidansu kasan halinta ba sake mana take ba washegari ta shirya ta ce " zata wuce gidansu Ta kwana biyu ta warke a chan'?"Niko ban hana ta ba nace Allah ya kiyaye nasan duk haushin abunda kayi mata ne yasa ta tafi"Zankirata Ammy ina Hajiya wai tunda na shigo ban ganta ba "Dazu ta fita Ta lek'a gidan Zainab ne " Okay Chuchu fa "bai rufe baki ba yaga shigowarta palourn hannunta rike da waya kai tsaye wajenshi ta nufa fuskar ta cike da fara'a ta ce " Lah yaya yaushe kazo ina yini"Alhmdllh Auta ya gidan"Lafiya qalau ta fad'a tana zaunawa gefenshi tare da cewa "Yaya kazo a Daidai tun safe na rasa shawarar Wanda zan nema bikin momcy ne ya taso za ayi Saturday d'innan ina son ne na tafi wednesday tun gobe ma naso na tafi wlh ammy ta hana wai sai wednesday to shine zanyi mata gudummawar jaka nakirata akan taturo mun hotonta na biki tace batayi ba gashi nafison nayi mata mai hoto to shine nake gani ko hoton waya zaiyi akwai hoton Dana tab'a mata a hostel kuma yayi clear sosai bari ka gani kaga idan zaiyi ayi dashi ko kuma Wanda muka tabayi tare Shima tayi kyau saikaga idan zaiyi a datse ni " ta fad'a tana nuna masa hotonta data tab'a mata da Abaya ta ce Kalli yaya Dan Allah kana ganin zaiyi "Amsar wayar yayi daidai idonshi yakai masa hotonta sanye cikin doguwar Riga Abaya ta yafa beil din rigar Dimple d'inta Duka sun lotsa sakamakon murmushin da tayi a hoton sosai hoton yayi masifar kyau Kallon mamaki ya dinga bin hoton dashi kafin ya d'ago ya kalli Chuchu da itama shidin take kallo ganin yanda ya rik'e wayar gam yana yiwa hoton wani irin kallon mai kama Dana mamaki maida Kallonshi yayi ga hoton Kara murza idonsa yayi Dan son tabbatarwa itadince kuwa koko gizau ne Tabbas ita ce " ya fad'a a ransa "Kafin ya sake Dagowa ya kalli Chuchu a karo na biyu ya ce.........✍🏿
07026166536 domin magana da marubuciyar kai tsaye
*GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯♀️👎👇👇*
1, *MU GANI A ƘASA...*🔥
_Ummu Affan_
2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚
_Ummu Maher_
3, *GUNTUN GORO..*💥
_Mom Islam_
4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎
_Mrs Bukhari_
5, *AUREN WATA TARA*👩❤️👨
_Miss Hajo_
Guda biyar 1k
Guda huɗu N700
Guda uku N600
Guda biyu N500
Guda ɗaya N300
*DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇
0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank.
Domin tura shaidar biya👇
0810 433 5144
Masu tura katin MTN👇
0814 179 9224
Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇
0817 952 3215
Guda biyar 1000f
Guda huɗu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ɗaya 300f
*TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩❤️👨
_*Miss Hajo ce*_🤙🏿
[10/3, 7:17 PM] Mother Mamy: 🅿️.........*65 & 66*
"na shiga ukku na lalace Asmy shikenan na bani na lalace na shiga ukku na " ta k'arasa fad'a a matuk'ar rude tana d'ora hannu biyu aka "a d'imauce Asmy ta Dauki takardar ta ce " me akayi Zarah"Da hannu ta nuna mata da ta karanta "kafin ta k'ara rushewa da wani kukan Bud'e takardar Asmy tayi gabanta na fad'uwa Ta fara Duba good handwriting dinsa da bai wuce layi shida ba fara karantawa tayi kamar haka" Ko a addinin Christian ba a Aure kan Aure bare addininmu na musulunci da ya haramta hakan Har yanzu har gobe da Aure na akanki basaina yi doguwar magana Ba nasan kina da Ilimi kinsan abunda yake fari da baki Ki rik'e mutuncinki na Matar Aure ban Aureki Dan in sakeki yanxu ba har sai na samu cikar buri na nima kamar yanda kika samu naki zan waiwayeki nan bada jimawa ba ina Kara tuna maki karki sake ki yarda ki bari a daura miki Aure da