Showing 126001 words to 129000 words out of 153980 words
ya rikice har baiji kukan da Amar ya fara ba Alamun ya tashi zahra ko Naji ta fara kokarin ya saketa amma ta kasa chuchu daga palourn da take ta dinga jiyo kukan Amar shataf ta manta da MD.na d'akin da gudu ta Ruga d'akin abunda ta gani ne ya sanyata yin Sauri tayi baya ba shiri tana dafe k'irji tace"na shiga ukku ni maryam me.na ganoma.idona"Zaune tayi tana tagumin tunanin yanda zahra ta biyewa Yayan nata murmushi tayi Ita d'aya ta ce "Allah sarki babu yanda banso zahra da yaya na ba ashe Allah ya Riga da ya tsara itace matarsa hadda y'ay'a ita kanta ta tuna abun nan al'ajabi take sai ta tuna lokacin da take cewa su Asmy.kilama ita d'in rabon yaya ce Ashe dai rabonshi d'ince...saida Little itama ta tsala nata kukan kasancewar na yara biyu ya dawo da MD hankalinshi cikin Sauri ya tashi a kanta Ajiyar zuciya zahra ta sauke tare da sauke numfashi Cikin Sauri MD ya d'auki little ta dauki amar jijjigashi ta fara shima MD na jijjigashi ganin bata da shirin feeding dinsa ya sanya MD cewa " ki basa abincinsa bakijin irin kukan da yake"Kauda kai tayi tana turo baki gaba tayi ta ce "Dan Allah Malam ka fita Haba" murmushi yayi ya ce "Ko kunyata kike Bayan yanzu na gama liliy...batajira abunda zaice ba tayi Sauri ta bar dakin cike da jin kunya da haushin Rashin junyarsa palourn ta koma gefen Chuchu ta zauna tana turo baki Chuchu na kallon yanda ta fito a murtuke saida tasoyin Dariya ta Had'iye MD ko murmushi yayi tare da jijjigar y'arsa kafin ya d'auki akhbar dake bacci Duka ya sanyasu a kafada ya fito Chuchu ya mik'awa shi ya ce " ku daina barmun yara su kadai a d'aki ko nan da nan ne"Murmushi Chuchu tayi tace "Daman bama barinsu yaya " satar kallon Zahra yayi da ta wani had'e rai yayi murmushi ya wuce da little kasa...tundaga lokacin nan MD ya samu damar zuwa ya rage zafi da zahra Chuchu ko tuni ta ganesa Dan d'aya shigo d'akin yake cewa ta basu waje ganin haka ya sanya data gansa take ficewama ta basu waje Zahra ko Dan dole yake mata Dan ba irin yanda batayi dashi akan ya daina zuwa Wajenta ita bataso idan yaranshine Ya dinga kiran Chuchu tana Kai masa su A haka dai har zahra ta kusa yin arba'in Yau ma MD yazo Chuchu ta fice tana palour ita da Amar da Alkhbar da suke kan gadonsu na kwanciya tana yi musu wasa suna mata dariyar koda Ammy ta shigo d'akin rik'e da little dake Tsala kuka Chuchu na ganinta ta ce "Ammy kuka take" Eh kuka take ai tamayi hakuri rabonta da mamanta tun safe fa "bari na kai mata ita" ta fad'a tana nufar kofar chuhu na ganin haka tayi Sauri ta shige gaban Ammy Dukta rude ta ce "Am my bari na kai mata ita" Harararta Ammy tayi ta ce "Da Allah bani waje bansan shiririta D'akin naku bako na ne " ta fad'a tana tura kofar kusan daskarewa tayi ganin MD kan zahra sai kissing d'inta yake Saurin rumtse ido tayi kafin Ta daka masa wata irin Tsawa wadda ba shiri MD Ya tashi a kanta Sosai ya rud'e ganin Ammy baiyi tsammaniba zahra ko wace irin kunya ce ta lullubeta tasan Ammy bazata fahimceta Ba ason ranta yake mata haka ba Dan ba yanda zatayi"Cikin Tsawa Ammy ta ce "Wuce ka bar dakin nan munafiki" sim sim MD yabar dakin cike da jin kunya Zahra ko kunya ta isheta saita fashe da kuka "Cikin fad'a Ammy ta ce " Watau ni ina Chan ina kwata miki hakkinki ke.kina nan kinbiye masa Ina tibka kina warwarewa kin mayarmun da aiki baya zahra me.yasa kika saki jiki dashi haka bakison yasan darajarki da martabarki yagane matsayi da muhimmancinki zahra "Cikin kuka zahra ta ce " Dan Allah Ammy kiyi hakuri nima banason yana zuwa kuma ki tambayi Chuchu kiji "tab'a hannu Ammy tayi ta ce " kenanma wannan bashine karo na farko ba kafin ta dallawa Chuchu harara ta ce "Ke kuma Munafuka watau duk hudubar da nayi maki akan karki sake ki barsa yana zuwa Wajenta bakiji ba to ai shikenan gaba d'aya yau zata koma part Dina sai Inga in d'akin nau zai dinga binta " Dariya Chuchu tayi ta ce "Ammy ni karkiga Laifina Miji da matarsa kuma saina hanasa shigowa" Dundu a baya Ammy takai mata ta ce "ja'ira" Dariya Chuchu tayi tana kaucewa ..tundaga ranar Ammy ta mayar da zahra part d'inta ta kasa ta tsare sosai akan MD ko Yaransa Saidai taba Chuchu takai masa sosai MD ya damu da hakan hankalinshi ya k'ara tashi Dan koba komai yana da buk'atar ganin matarshi sosai Ammy ta burkuta masa lissafi gabak'i d'aya ...yana kwance a makeken Royal bed dinsa kamar koyaushe indai ya kwanta shi d'aya to ba tunanin da yake idan ba nata ba yaji wayarsa tayi ringing kamar bazai daga ba saikuma ya d'auka ganin Baba na gombe ne Cikin girmamawa MD ya gaishesa ya amsa masa ya ce "jikana ashe haihuwa akayi maka baka fadamunba Abun farinciki ya samu ashe har anyi wata guda bani da labari sai dazu Jabir Daya kirani muka gaisa yake fad'amun gsky banji dadi da baka fadamunba kasan ai nazo naga y'ay'an nawa amma dukda haka insha Allah na shirya gobe gani nan zuwa kadunar zanzo nayi maka barka naga yaran kaga harmun gaisa da Hajiya sannan nayi mata Godiya"Cikin girmamawa MD ya ce " ba haka bane Baba lokacin wani uzurine ya mantar dani fad'a maka ai Baba dama ka barsa karka wahalar da jikinka idan sukayi kwari a kawoma maka su kaga jikin naka bai gama warwarewa ba"murmushi yayi ya ce "a a jikana jiki kuma ai ya warware gobe insha Allah Zanzo naga y'ay'an tunda tafadamun haihuwar Naji ina son ganin Yaran " cike da murmushi MD.ya ce "To shikenan Baba gobe da safe driver zaizo ya tafi dakai saika biyoshi zai kawoka har gida " haka ko akayi washegari tunda safe driver yaje ya taho da Baba na gombe da Yakejin gabanshi na fad'uwa tunda suka taho suna isowa garin Kaduna Baba ya dinga bin garin da Kallo yana murmushi Har suka isa tafkeken gidan su MD Daman tun jiyan MD.ya sanar da Ammy da zuwan Baba anshirya masa komai na tarba a Babban palourn bak'i aka saukesa Bayan an cika masa gabansa da abubuwan makuleshe sosai MD ya nuna jin dadinsa na zuwan Baba Bayan Ammy ta shigo tana rik'e da Amar Hannunta da fara'a tayi welcoming din Baba cikin girmamawa tamkar mahaifinta haka ta dinga girmamasa Bayan sun gaisa Baba ya k'ara yiwa Ammy Godiya akan irin taimakon da MD yayi masa murmushi Ammy tayi ta ce "Bakomai Baba Ai anzama daya kaid'in ai tamkar uba kake a gareni shiko jika ne a gareka" fara'a cike da fuskar Baba ya ce "na jima banga mutanen kirki mutane na kwarai ba irinku ba Allah dai yasa a gama da duniya lafiya ya kareku daga sharrin makiya ya raya zuri'a Ameen Ammy ta fad'a tana mik'awa Baba Amar ta ce " Ga d'iyan naka Baba Biyun yanzu za a kawo maka ana shiryasu"Murmushi Baba yayi yana amsar yaron Ya ce "kai kai masha Allah Tubarakalla Allah ubangiji ya raya ya karesu daga sharrin makiya " shidai MD yana mamakin Baba tsoho da duk addu'ar da zaiyi ko waya suke saiya ambaci makiya da mahassada "Kallon yaron kawai Baba yake yanajin k'aunar yaron haka kawai yakeganin yaron tamkar ya rik'e jininsa Chuchu ce tare da zahra suka shigo tana sanye cikin zullubebiyar hijab har kasa ita na rik'e da Akhbar Chuchu kuma little gefen Ammy Zahra ta zauna Hakanan yau ta tashi a sanyaye kallon ta kawai MD yake tunda ta shigo sosai yaga ta k'ara yi masa kyau da kwarjini baisan lokacin d'aya saki kasaitaccen murmushi ba tare da sauke ajiyar zuciya Dagowar da Baba zaiyi daga Kallon Amar idonsa ya sauka akan zahra dake mik'awa Ammy akhbar Ammy ta ce " To Baba ga sauran an kawo maka kaga maman yaran"ta fad'a tana nuna masa Zahra"A matuk'ar firgice Baba ya Mike Hankali tashe yake kallon zahra yana rik'e da Amar ya fara nunata da yatsa kasa magana yayi sai nuna ta da yatsa da yadingayi muryarsa gaba d'aya ta sartsa ya kasa furta abunda yakeson fad'a duk Kallon mamaki suke binshi dashi har zahra da ita yauma ta fara ganinsa Rumtse idonsa yayi da karfi kafin ya bud'e yana nunata da yatsa a rarrabe ya ce "Ma my y'a ta Zahra'u da man kina raye ba ki mutu ba Zahra'u kece nake gani ko ko mafarki ne nake........✍🏽
*Domin magana da marubuciyar kai tsaye 07026166536*
*GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯♀️👎👇👇*
1, *MU GANI A ƘASA...*🔥
_Ummu Affan_
2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚
_Ummu Maher_
3, *GUNTUN GORO..*💥
_Mom Islam_
4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎
_Mrs Bukhari_
5, *AUREN WATA TARA*👩❤️👨
_Miss Hajo_
Guda biyar 1k
Guda huɗu N700
Guda uku N600
Guda biyu N500
Guda ɗaya N300
*DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇
0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank.
Domin tura shaidar biya👇
0810 433 5144
Masu tura katin MTN👇
0814 179 9224
Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇
0817 952 3215
Guda biyar 1000f
Guda huɗu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ɗaya 300f
*TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩❤️👨
_*Miss Hajo ce*_🤙🏿
[10/3, 7:17 PM] Mother Mamy: 🅿️...........*83 & 84*
Gaba d'aya MD yana rikice ya rasa wace irin Godiya zaiyiwa Allah s w a da yayi mashi wannan gagarumar kyautar yara Ukku lokaci guda yana Rungume da babyn yayi sujudu shukur sosai yake kwararo yabo da gdy ga Allah s w a Kafin ya bud'e fuskarsa d'auke da murmushi kamar gonar Auduga ya kalli Ammy ta ce "Ammy wai wannan din Duka yara na ne da gaske" murmushi kawai Ammy ke masa Dan farinciki harya mantar da ita wani b'acin rai Ta ce "yaranka ne babana " Daga hannu ya sakeyi ya ce "Allah Alhmdllh Alhmdllh bansan da wasu kalamai zanyi amfani ba wajen gode Maka " murmushi kawai suke Chuchu ma uwar kuka yanzu andawo murmushi cikin d'oki ta ce "Yaya wlh Duka kamarsu d'aya kuma dakai sukayo kama " daidai lokacin da na hannun Ammy ya fara kuka jijjigashi Ammy tayi ta ce "Yi Sauri Babana Kaje gida D'akin nan na kusa da na Chuchu zakaga kayan jarirai kodan ku tafi da chuchun Aje a d'auko duk abunda ya kamata sannan Ka taho da Dabino mai laushi tare da zamzam ka basu " to to Ammy Amma ya jikin nata ita mu bari a fito da ita"Jikinta Alhmdllh Dr ya ce "anwuce d'akin Hutu da ita bazamu samu ganinta yanzu ba allurar bata sake ta ba kuje ku kawo kayan yaran" Mik'a mata Namijin Chuchu tayi shiko MD Kallon yarinyar kawai yake dake tsala kuka yana murmushi wai yau shine rik'e da jininsa sosai yaji k'aunar yaran ta musamman Na ratsa sa wata nurse ta amshi yaran biyu Ammy ta rik'e d'aya Dan Aje a shirya su Kafin a kawo kayan "Cikin doki Ammy ta kira Zey tayi mata albishir Hajiya kaka takeson kira ta mata albishir to bata San taya zatayi musu bayanin zahra ba Hakanan dai Ammy ta lalubo number Hajiya Bayan suun gaisa ta ce " Hajiya Albishir na kira miki addu'ar ki dai ta amsu Matar MD ta sauka yanzu an haifi y'an Ukku"Ammy saida ta kauda wayar daga kunnanta saboda irin. Bud'ar da Hajiya ta rangada kira take "Alhmdllh Alhmdllh Ina kike rukayya maza taho ki kiramun iyayenki muyi musu Babban Albishir Matar Mustapha ta haihu"Ammy lura da Hajiya murna tama mantar da waya ya sanyata katse wayar tana murmushi ta window ta lek'a ta Hango zahra dake baccin wahala sanye da blue din rigar da aka gama mata aiki hannunta biyu Duka sanye da kalula d'aya Karin jinin da aka diba a na MD ne d'aya kuma Karin ruwa ne Goge hawayenta Ammy tayi ta ce "Allah ya baki lafiya zahra ya tashi kafadunki" ba ayi Minti goma ba saiga zey ganin yanda ta fito daga motar kasan ba karamun gudu ta sharara ba cikin farinciki ta ce "Ammy da gaske Ta haihu kuma y'an ukku yayanmu ahima ya zama uba" Murmushi ammy tayi mata ta ce "da gaske zainab kinga ikon Allah ko Yanzu haka Ana ciki ana shirya yaran ana jiran su maryam su kawo kayan da za a sanya musu kinsan a dimauce muka zo " Ajiyar zuciya zey ta sauke tare da goge hawayen farinciki ta ce "Alhmdllh ammy Adduar tsawon shekaru goma ta amsu Ta inda ba ayi tsammani ba ina mamyn take yanzu?tana ciki kinsan cs akayi " wayyo Allah ya bata lfy kaico "ba a dau lokaci ba su Chuchu sunkadawo tana rik'e da kayyayakin MD fara'a ta kasa barin fuskar sa sai nan nan yake Bayan an shirya yaran nanfa Chuchu ta shiga yi musu hoto Kamarsu d'aya har macen dukansu kuma da dimple d'insu irin na zahra dukda jariraine amma saida suka fito Fari da kammani da kyau duka MD suka biyo dimple din zahra kadai suka biyo nan fa aka shiga liliyar yaran d'aya Bayan daya MD ya d'aukesu ya tauna musu Dabino da zamzam rik'e Namijin dayan yayi yana ta kallonsa kamar zai cinyeta sai Murmushi yake yanajin wani irin farinciki na ratsa sa Ammy bata damu da irin rawar k'afar da MD yake ba ko Kara bayayi saboda tasan dole yayi abunda aka ta roka tsawon shekara goma yanzu Allah ya kawo ai dole yayi rawar kafa ganin yaran sun fara kuka ne ya sanya hankalin MD tashi duk ya rud'e Kallon Ammy yayi ya ce " please Ammy me za ayi musu suna kuka fa "Harararsa Ammy tayi ta ce " Waikai baka da ta ido"Sosai k'eya yayi ya ce "Ba haka bane Ammy kar wani abun ya samesu" girgiza kai kawai tayi koda Chuchu ta kira Asmy ta fad'a mata irin ihun murnar da tayi bana wasa bane farincikin data shiga bana wasa bane Koda ta fad'awa mamansu itama tayi farinciki matuka tana Jinjina ikon Allah tare suka shirya a motar babansu ya taho dasu Kaduna Dan suga jikin na zahra tunda ance musu cs ne "Kafin one hour sun Iso sosai Ammy ta karramasu da girmamasu dukda a Asibiti ne akayiwa juna barka Asmy ko tunda ta rik'e macen taki ba kowa saida tayi hawayen farinciki wai wannan din Duka yaran zahra ne nanfa hankali ya koma jiran farkawar Zahra Dan har yanzu saida su lek'a ta window MD ko tsaye yayi a jikin window din sosai yaji tausayinta ya k'ara kamashi ganin halin da take ciki saida yaga y'an gidan su Asmy tukwana yabar jikin Window din sai wajen 4pm zahra ta farka koda ta bud'e idonta Kallon d'akin ta dingayi kafin ta kalli jikinta da hannunta duk drip yunkurawa tasoyi Dan ta tashi amma ta kasa komawa tayi tana lumshe ido wasu hawaye na zubo mata tunowa da wahalar da tasha dazu bata manta da lokacin da za ayi mata cs ba kasancewar bata ido biyu akayi mata ba yasanyata bata tuna ba har yanzu allurar bata saketa ba saboda bibbiyu take ganin komai daidai lokacin da Nurse biyu suka shigo suka duba ta kafin a sauya mata daki aka maida ita wani koda su Ammy suka shiga Sannu kawai suke mata bata iya magana ba sai daga musu kai Goge hawaye Asmy tayi taje gefenta ta ce "Sannu sis" Itama gyada mata kai kawai tayi tana lumshe ido Dan kanta duk Juyawa yake "MD ko daga jikin kofa yake kallonta Ammy ce ta ce Ku Aje mata yaran ta gansu gefenta aka aje mata su Kafin Ammy ta ce " Bud'e ido kiga kyautar da Allah yayi maki daughter "a hankali zahra ta bud'e idanunta har lokacin ba komai take gani ba " Kallon Yaran ta dingayi dukda ba Sosai taga fuskarsu ba Amma har a ranta sosai taji k'auna da soyayyar yaran na ratsa ta kenan y'an Ukku Ta Haifa kallonsu kawai take Ammy na ganin haka saitayi murmushi ta jima tana kallonsu kafin ta daga hannunta d'ayan dake rik'e da drip Da niyyar ta tab'a na kusan nata Daga tsayen da MD yake ya matso ya ce "Ki bari Mamy drip ne hannunki bayason motsawa" Harararsa kasa kasa Ammy tayi ya sanyashi yin shiru amma har lokacin hankalinshi na Wajenta kallonta Ammy tayi ta ce "Zaki iya" gyada mata kai zahra tayi D'aukar shi tayi Ammy ta Aje mata shi a gefenta a hankali zahra tasa hannu ta zagayosa ta matsesa gefenta tana Kallonshi tana kallon sauran Maman Asmy ce ta ce "karfa ki matse sa zahra" Bazan masa komai ba "ta fad'a kasa kasa " Girgiza kai Ammy tayi ta ce 'Allahsrk d'a da uwa kenan sai ALLAH "Dr ne ya shigo Bayan ya duba ta ya tambayeta Saidai ta gyad'a masa kai Dan maganar nauyinta takeji " Ammy ce ta ce "Dr kamarfa har yanzu bata dawo daidai ba " Eh daman bazata dawo daidai yanzu ba ita hakanma da sauki wasu allurar tana dad'ewa tana daukarsu sosai zakiga har suna wasu maganganu kamar marassa kai da ta ido biyu ce akayi mata zata tashi normal amma itama zuwa gobe zata dawo normal please a barta ita da mutum d'aya Ta samu Hutu sosai "Ammy tace zata zauna da zahra sauran duk su koma gida dukda maman Asmy taso zama Wajenta MD ma yaso ace shiya zauna Wajenta Dan hankalinshi yanzu yana ga samun Lafiyarta Ga damuwarshi na abunda za Aba yaran Dan sun fara kuka Sosai Ammy ta kula da Zahra da Yaran tamkar kwai Bayan ta had'a mata Malta da isashshiyar madara Abu mai ruwa ruwa dai ta dinga bata sannan aka bata maganin da tasha dan asamu abincin yaran yazo sai wajen 8pm aka samu ruwan yazo Ammy ta d'ora mata su ta dinga