Showing 90001 words to 93000 words out of 153980 words
had'u kasancewar lokacin sun fito daga lectures farinciki d'auke da fuskarsa ya ce "Kinga ko yanda kika k'ara kyau da fresh kuwa my Zarah ko har amfara dilkan Amarcin ne" Rufe fuska tayi ta ce "Kai ya Hafiz ana sch ina aka samu daman dilka kawai idonka ne ke gane maka haka fa" Serious fa nake maki magana wlh kin k'ara kyau da fresh da komai ma"Uhm"Kawai Zarah tace cike da jin kunya sai wajen Yamma ya tafi Tukwana ta koma hostel Dan yau bata da niyyar komawa gidan MD Dan yanzu Abunda yake mata ba dadinsa take jiba ita kanta har mamaki take da yanda takeson abun Amma yanzu kwata_kwata ko feeling ta dainaji"Tana shiga Chuchu kadai ta tarar kwantawa tayi kan gadon ba bacci take ba duniyar tunani ta Lula Wanda a kasheta bazatace ga tunanin da take ba a haka har Asmy ta shigo"saida ta daddabata tukwana ta dawo "harya tafi Hafiz din" Eh "ta bata amsa a takaice" okay kunyi maganar shirye shiryen bikin dashi"Girgiza kai Zarah tayi ta ce "a a a " to saboda me Abu na tahowa yanzu ai ya kamata a fara tsara abubuwan tunda Kinga damun koma wata gudane za a k'ara ba wani isashen time"ku shirya kawai ni bani da wani shiri da zanyi ta fad'a tana hade fuska"Ikon Allah Asmy ta fad'a kafin ta ce "hmm kede kika sani" Bata kula ta ba Zarah da dare tana jin Suna dahuwar indomie Bayan sun gama Chuchu ta ce "Ki sauko muci momcy wai ko baki da lafiya" Girgiza mata kai Zarah tayi ta ce "Na koshi ina Lafiya kawai ina danjin kasala ne shiyasa" Gaban Asmy ne ya bada daram Kallon Zarah tayi ta ce "Kasala kuma?gyada mata kai tayi tare da juya mata baya " Chuchu ta ce "Ki sauko muci Bafa kici komai ba" na k'oshi banajin yunwa "Zarah ta fad'a tare da kauda kai Dan k'amshin abincin baiyi mata ba yana neman tasar mata da zuciya Asmy saida taga Chuchu ta fita tana waya tukwana takamo hannun Zarah tare da cewa " Sis kina shan wannan maganin nan kuwa?wani magani ?Zarah ta tambayeta ?Wanda Dr Halima ta rubuta maki mana"Sai sannan Zarah ta tuno ma da maganar cewa tayi "ohhh eh ina shansa ya akayi" Ajiyar zuciya Asmy ta sauke ta ce "Daman ina son fita kokontone tsoro nake Kar Aje ciki gareki naga duk kin sauya kwanannan" tsaki Zarah taja ta ce "Ke baki da hankalina wlh mai ciki kama da wa yake mema zai had'ani da ciki Bayan watan nan ma.Saida nayi perioud gashi ina shan magani kuma ma shida ba haihuwa yake ba karma ki damu kanki ba wani ciki da garan kawai ina tunanin Maleria ce Ke damuna" Ajiyar zuciya Asmy ta sauke ta ce "To gobe muje asibiti mana a gwada ki ko na cire zargin kokwantan da nake a raina" Ba Inda zani ni lafiya ta qalau please karki sake mun maganar nan marar ma'ana Asmy "washegari Bayan fitowarsu daga lecture driver yazo ya d'auketa koda ta isa bata samesa a gidan Ba dak'yal ta samu tayi sallah ta kwanta Dan wata gajiya a tattare da ita A sallayar da tayi salla a palour ta kwanta bacci ya d'auketa sai wajen 5pm MD ya shigo gidan dawowarsa daga kd kenan karewa d'akin kallo yayi tare da kallonta yanda ta dukunkune a kan prayer mat tana bacci harya k'arasa shigowa palourn yana mamakin baccin nan da ta tarka da sauyawar da tayi cikin satittikan nan ga wani fresh da take dukda MD baisan alamomin masu ciki ba Amma kawai zuciyarsa saita tsarga masa ko ciki gareta saurin barin tunanin nan yayi sanin irin magungunan da ta dinga d'irka tsawon watanni zaiyi wahala ta samu ciki a y'an shekarun nan ma Inma basu mata illa ba a nashi tunanin " a hankali ya shiga Kiran sunanta saida ya daddabata tukwana ta tashi tana murza ido harta gama wartsakewa kallonta MD yayi ya ce "Me yasa kike baccin yamma kinsan bakyau" Muryarta mai kama da ta mai bacci ta ce "Nima bansan ya d'auke ni ba ko har anyi la'ar ne" Tun dazu yanzu har 5 "Firgit Zarah ta mik'e ta ce " subhanalla tun fa 2 na kwanta har 5 banyi salla ba "Cikin Sauri ta wuce toilet din palourn Dan ta dauro alwala harta gama salla MD yana tunanin wani abu a ranshi Bayan ta salamce fuskantarta yayi ya ce " Na tambayeki mana?Inajinka"ta fad'a a hankali"Yaushe rabonki da perioud"Shiru tayi kamar mai nazari kafin ta ce "two weeks " Kin tabbatar kuwa?Gyada masa kai tayi ta ce "Eh" okay "kawai ya fad'a tare da maida kansa ya jingina da Bayan cushion yana lumshe ido a ransa ya ce " To me yake damunta'"ya rage sati guda yarjejeniyarsu Ta k'are cikinsu babu Wanda baiyi sanyi ba Musamman Zarah da takejin wani iri a ranta Hakan yasa yanzu suka rage Rashin jituwa ita da shi Amma kuma idan ta tuna Ta kusa rabuwa da Kalular Auren nan da aka lak'a mata saitaji sanyi a ranta bangaren Hafiz Sosai ya shiga shirye shiryen biki ba kama hannun yaro bangaren Zarah ko ba wani shirin da take Dan tayi wani irin sanyi sanyin ta na da ya dawo harma ya fi na da Asmy sai mita take akan halin ko in kula da take nunawa a bikin yauma suna zaune a jikin wani block cikin b'acin rai Ta ce "Wai me kike nufi Zarah duk sanda na d'auko miki maganar hidimar biki saiki banzatar dani " Kauda kai Zarah tayi tare da kwantar da kanta bisa cinya ta ce "Asmy Kuyi komai da kikaga ya dace please kidainayimun zancen bikin nan" kama hab'a Asmy tayi ta ce"Lallai Zarah yanda nake tunani kin wuce nan kamarya nadaina yi miki zancen bikinki me kike nufi wai ki fito fili ki fadamun"Zarah batasan dalili ba kawai saiji tayi hawaye sun fara zubo mata Wanda in za a kasheta bazatace ga dalilin kukan ta ba "Saurin kama hannunta Asmy Tai ta ce " subhanalla meye haka wai zarah"Fad'awa jikinta Zarah tayi tare da fashewa da kukan da taso rikewa "sosai Asmy ta rude ta fara cewa " meye haka Zarah karki tayarmun da hankali daga magana sai kuka me aka miki karkija hankalin mutane su dawo Kanmu please "Kasa mata magana Zarah tayi sai kuka da take Chuchu ce data hangosu ta Iso gurin ganin yanda Zarah ta lafe jikin Asmy tana shashekar Kuka ya sanyata cewa " subhanalla me akayi mata Asmy "cike da damuwa Asmy ta ce " wlh ba komai daga fara zancen biki kawai tahau mun kuka"Ikon Allah to ko batason bikin ne?kamarya su shekara hud'u suna soyayya da mutum biki yazo tace bataso ai bata isa ba abunda bazaiyu bane bama tana so kilan wani abun ne"Dak'yal suka samu Suka lallab'ata suka wuce hostel Wanda suna shiga ta fad'a Gado tare da Kara fashewa da sabon kuka Kallon juna Asmy da Chuchu sukayi sannan suka Kalleta zaune sukayi suna Kallon ikon Allah ba irin Lallashin da basuyi mata ba Amma batayi shiru Ba Saida ta gama kukanta mai isarta kafin ta Bari daka Kalleta kasan Tasha kuka Wayartaace dake hannun Asmy tayi ringing dubawa tayi taga Yusuf ne "D'auka tayi nan yake shaida mata driver ne yake jiran Zarah tun d'azu" okay gata nan "Asmy ta bashi amsa " dafa Zarah tayi da tayi shiru zuwa lokacin Chuchu na gefenta tana Lallashinta dukda basusan meya sanyata kuka ba Ta ce "Ki tashi driver na jiranki" banza tayi mata"saida ta maimaita ta ce "magana fa nake maki Zarah" tukwana ta tashi tare da Goge hawayenta cikin muryarta data fara dishashewa ta ce "Bani wayar to" Mik'a mata wayar Asmy tayi harta amsa saikuma ta riko hannunta ta ce "Ki fad'amun me yake damunki please Zarah baki da sirrin da zaki iya b'oyemun bai kamata ki boyemun wani abu meya ke damunki wai kwanannan"ba komai " ta fad'a tana goge sabon hawayen da ya zubo mata"Hmmm to wannan kukan da kike na meye"ba komai Kawai na tuno da Mamana ne da bansantaba shiyasa"ta fada tana Goge sabon hawayen daya zubo mata tayi saurin Mikewa tare da d'aukar wayarta ta ce "saida safe" saida tayi control d'in hawayen dake zarya a idanunta kafin ta fita amma kallo d'aya zakayi mata kasan tayi kuka shiru Chuchu tayi Jin Abunda Zarah ta ce saida tabar d'akin kafin ta kalli asmy da itama jikinta yayi sanyi ta ce "Me take nufi Asmy mamanta bata raye daman" eh tun wajen Haihuwarta ta rasu bata Santa ba ko a hoto saidai kawai anbamu labarin kamar yanda zarah take itama haka mahaifiyarta take banbancin ba kowa ne zai iya ganesaba hannun Matar uba ta tashi"hawaye harsun zubo a idon Chuchu ta ce "wayyo Allahsrk momcy gsky dole tayi kuka Rashin uwa ba k'aramun Abu bane kamarni Tun ina ciki bansan mahaifina ba Sai a hoto amma gwarani gaskiya akanta tunda ina da mahaifiya mancewa ma nake da rashin mahaifin da nayi saboda kallo biyu nakeyiwa yayana na uba da kuma na yaya shiya mayemun gurbin abba na amma Kuma wai ya kuke da ita ne dafa na d'auka gidanku d'aya saidaga banbanci sunan uban yasa nake tunanin ko cousin ne?Dan murmushi Asmy tayi ta ce " mubar maganar nan chuchu"Jin haka ya sanya Chuchu Jan bakinta tayi shiru karsuce tana musu shishigi Zarah ko kallo d'aya MD yayi mata yasan tayi kuka Saboda yanda idanunta sukayi ja ga kuma Rashin walwalarta data shigo da ita a hankali ya kirata da sunan da yake kiranta watau Mamy "Cikin sanyi ta d'ago ta Kallesa saita maida idanunta kasa " Baki da lafiya ne?Girgiza masa kai tayi"wani Abu akayi miki?nan ma girgiza kai tayi ,"To me ya sameki "kukan da ta dinga Rikewa ne tun a hanya ya Kufce mata batasan sanda ta fashe da sabon kuka ba " subhanalla ya fad'a tare da komawa Inda take ya kama hannunta ya ce "Me akayi miki" Shiru nan ma saici gaba da kukan da tayi "Janyota jikinshi MD yayi saboda a rayuwa ba abunda ya tsana sama da sauraran kuka kukanma na mace wannan yana d'aya daga cikin abunda Yasa ake ganin kamar Amera ke juya sa nan ko haka rayuwarsa take bayason ganin wani cikin damuwa musamman Wanda yake tare da su bare kuma Amera matarsa da suka zauna tsawon shekaru goma " shafa bayanta ya fara cikin sigar lallashi kamar wata baby Yana cikin Lallashinta Har yaji saukar numfashinta alamar tayi bacci Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya dinga kallonta yana nazarin meke damunta ya lura dai kamar akwai abunda ke damunta d'an karta tashi ya barta a jikinshi dukda yana buk'atar tashin Saida tayi baccinta ta gaji dukda a takure yake koda ta bud'e idanuwanta Kallon gefenta ta fara ya tabbatar mata da Cikin namiji take sai sannan tunaninta ya dawo mata cikin Sauri ta Zame jikinta a hankali daga nasa kallo d'aya tayi masa tayi kasa da kanta Tare da saurin Mikewa ta shige bedroom sallah kawai tayi danko yunwa bataji tarasa cikin kwanakin nan biyu abunda ke damunta ga tunanin mahaifiyarta da ya sanyata gaba sosai ta fara shiga kogin Dana sanin abunda ta aikata dukda tasan Asmy itace makasudin faruwar komai kwance tayi kan bed tare da lumshe ido kamar mai bacci Tana jin shigowarshi ta k'ara lumshe ido Zaunawa yayi gefen bed din tare da juye take away din d'aya sanya akayo musu a plate ya ce "taso kici abinci" Shiru tayi kamar mai bacci"Nasan kina jina kikamun banza ko Mamy"Kamar bazata tashi ba saikuma ta bud'e ido a hankali tare da mik'ewa ta tashi zaune tana jin kanta na ciwo kauda kai tayi bata bari sun had'a ido ba Plate din ya Aje gabanta tare da cewa"Ki juyo kici karya huce nasan ba abunda kikaci"a sanyaye ta ce "Na koshi?Baki isa ba sai kinci maza karki sake mun musu kinsan abunda bana so kenan"Sosai ta kwabe fuska kamar taga kashi haka ta fara cin abincin da ba dadinsa takeji ba Dak'yal tayi chokali shida ta Aje ta ce " na koshi"Kallonta ya dingayi yana Nazarinta a hankali "Ganin irin kallon da yake mata ya sanyata tsarguwa da kanta taki bari su hada ido" Kince kinyi perioud wannan watan? cike da kosawa ta gyad'a masa kai"shiru yayi kafin ya ce "Kishirya na kaiki Asibiti idanma Maleria ke damunki a baki magani" Kamar zatayi kuka ta ce "Ni wlh banason zuwa Asibitin lafiya ta qalau kaina ne kawai yake ciwo" Dage kafada MD yayi ya ce "Jikinki" yana gama fad'ar haka ya fita da harara ta bishi kafin taja tsaki kasa kasa tana tunanin tambayar da yayi mata sau biyu na perioud a ranta ta ce "Ko ina ruwansa da perioud dina "ba adau lokaci ba taga shigowarsa d'auke da ruwa a cup zaunawa yayi gefenta tare da b'allo parasitimol guda biyu ya ce " Anshi tana yamutsa fuska ta amsa Bayan ta amshi ruwan da ya mik'o mata saida ta rumtse ido kafin ta Had'iye saboda warin maganin da ya ke neman tayar mata da zuciya kakarin kamar zatayi amai yaga ta fara cikin Sauri ya d'aga pridge din d'akin ya fiddo fresh milk saurin budewa yayi tare da kafa mata a baki tana farasha taji ta dawo normal saida ta kusa Rabi kafin ta mai nuni da ta k'oshi janyewa yayi tare da kallonta ya ce"Ko bakiji dadi ba karki sha wani maganin da ya wuce wannan"Saboda me?Saboda haka nace maki"Shiru tayi tare da kwanciya ta juya masa baya"Ki tashi daga baccin nan na fad'a miki"Tana turo baki dukda baya ganinta ta ce "ba bacci ba zanyi" Da Dare tanaji MD ya fara yamutsarta ta fashe da kuka "Sosai MD yayi mamakin abunda bata tab'a masa ba kenan " Hakan yasa ya rabu da ita yana tunanin ko jikin nata ne dayan d'akin ya koma Zarah najin fitarsa ta sauke ajiyar Zuciya raba dare tayi tana salla Wanda yawaici duk adduarta akan mahaifiyarta ne Sosai take roka mata Rahama A wajen ubangiji saida taji bacci ya fara daukarta tukwana ta lallaba ta koma ta kwanta MD ko tunda ya koma ya kasa bacci yana tunanin sauyin yanayin yarinyar abunda bata tab'a masa yau tayi masa A ranshi ya ce "Kodai itama ta fara gajiya ne?To amma me yasa da Chan bata tab'a nuna Rashin So ga abunba sai yanzu" Karfa ciki ne da ita?kai gsky ba ciki bane saboda tace tayi perioud? Meke damunta ne?haka dai MD yayi ta sake sakensa "washegari Zarah duk yanda taso taje lectures MD ya hanata saboda yana tunanin bata da lafiya ita dai tasan lafiyarta qalau yanzu kam ba yanda ta iya ta hakura ta zauna saboda yanzu batasan yawan musu dashi tunda dai kowa ya kusa kama gabansa Ranar da ta cika wata Tara Cif da yarjejeniyarsu Aurensu Wanda MD mancewa ma da lokacin yayi Zarah ko tana sane sarai tunda safe Ta hada duk abunta da tasan nata ne a gidan ta sanya a akwati Kayan d'aya saya mata ta barsu a ciki Wanka kawai tayi hijab d'inta har k'asa bata shafa komai a fuskarta ba zallar ainahin Kyawun da Allah yayi mata ne bata samesa a palourn ba hakan ya tabbatar mata da yana ciki zaunawa tayi zaman jiransa ya fito ya furta mata Kalmar saki ko kuma ya bata takardar sakinta ko ta samu nutsuwa a cikin zuciyarta gashi Allah ya taimaketa kafin lokacin bikinta ta gama idda tayi minti sha biyar zaune kafin taji fitowarsa cikin shigarsa ta alfarma tunda ya shigo Palourn k'amshin turarenshi ya kauraye Duka ilahirin palourn lumshe ido Zarah tayi a ranta ta ce " Baya ragawa Turare"cikin Tafiyarsa ta izza ya Iso palourn "batare da ta Kallesa ba ta ce " Ina kwana"Morning muntashi lafiya"Steady"ta basa amsa a kad'aice "Kallon akwatin dake gefenta yayi ya ce " wannan fa "Cikin k'arfin hali ta ce " kaya na ne zankoma hostel "da izinin wa kuma saboda me?saboda Yarjejeniyar *Auren wata tara* yazo karshe yau wata Taran ya cika nasan kaima.kana lissafi ina jiran ka bani takardar saki na ne kafin na tafi"wani irin kallo MD yake binta dashi Wanda bazata iya fassara yanayin da yake ciki ba lokaci guda mood din fuskarsa ya sauya cikin dauriya ya ce"Kina nufin wata Tara ya cika da aurenmu?"Eh mana Ka lissafa mana ina tunanin ma harya so ya wuce" shiru MD yayi kafin ya d'ago ya ce"Bai cika ba ki koma Lokacin da ya cika zan sallameki da kaina?wani irin kallo Zarah ta dinga binshi dashi na ka rainamun wayau ta ce "Kamarya me kake nufi wlh ya cika kuma yau d'innan saika sakeni tunda ba a garin gab'a_gab'a muke ba " Dukda MD yayi mamakin jin furucin ta Wani murmushi ya saki da bazaka iya sanin na meye ba tare yin shiru ya lumshe ido cikin nutsuwa Hankali kwance"da karfi zuciyar Zarah ta dinga Bugawa bata San lokacin da ta fashe da kuka ba Ta ce "Wlh baka isa ba saika sakeni aiba haka mukayi daku ba,wannan ba adalci bane,kamar yanda a baya lokacin da naki Amincewa da Auren nan Abokinka yayi mana gori bada son raina ba harna amince yanzu kuma wata taran yayi kace bazaka sakeni ba wlh baku isa ba " ta k'arasa fad'a tana fashewa da kuka"Sosai take kuka kamar ranta zai fita MD jin kukan nata Yake har cikin ransa "Bar kukan indai kinason muyi magana ta fahimta" cikin Sauri Zarah ta bar kukan tare da Fara Goge hawayenta "Ajiyar zuciya ya sauke ya ce " Saki kike buk'ata ko?Gyada Masa kai tayi"Okay give me 2 minutes"ya fad'a tare da barin dakin ya shiga d'ayan ba ayi minti goma ba taga fitowarsa rik'e da takarda Yana linke ta dukda Zarah abunda take buk'ata a yanzu kenan saida gabanta ya fad'i k'arasa shigowa palourn yayi tare da makullin mota a hannunsa ya ce "Muje na saukeki" a sanyaye Zarah ta bisa parking space taga ya nufa ya fiddo mota nuni yayi mata da ta shiga Ciki ba